Jump to content

Ismar Sayyada Fatima (S)

Daga wikishia

Ismar Sayyida Fatima (S) tsarkaka da katanguwar ƴar Annabi (S.A.W) daga dukkanin zunubi da kuskure, a cewar Shaik Mufid ismar Sayyida Fatima (S) wani abu ne da musulmai suka yi ijma'i a kansa, a cewar Allama Majlisi ƴanshi'a sun yi ittifaƙi kan wannan batu, abin da ismarta take lazimtawa shi ne cewa tana tare da ba'arin wasu sha'anunnukan Annabawa da Imamai (A.S) misalin hujjar zantukansu da ayyukansu da abubuwan da suka goyi baya, haka da marja'iyyar addini da cancantar ba da tafsiri da bayani, haka nan tsarin yadda ta rayu a ma'auni ne na tantance gaskiya daga ƙarya, haka kuma ita abar koyi ce a fagage daban-daban na rayuwa. Daga jumlar dalilan da aka kawo game da ismar Sayyida Fatima (S), akwai misalin ayar taɗhir, hadis bad'atu da sauran hadisai da suke shiryarwa kan ismar Ahlul-baiti (A.S) misalin hadis saƙlaini, hadis safina. Malam Fakhrur Razi daga malaman tafsiri na Ahlus-Sunna wanda aka fi sani da imamul mushakkikin shi ma ya yi imani da ismar Sayyida Fatima (S)

Matsayi da Muhimmanci

A mahangar shi'a haƙiƙa Fatima ƴar manzon Allah (S.A.W) tana da muƙamin isma,[1] da katanguwa daga dukkanin zunubi da kuskure.[2] Shaik Mufid,[3] ya tafi kan cewa musulmi sun yi ijma'i kan ismarta, amma shi kuma Allama Majlisi,[4] yana ganin ijma'i ne na ƴanshi'a. Malamai masu zurfafa bincike sun yi bayanin dalilai game da ismarta; daga jumlarsu akwai:

  • Kasancewarta tare da ba'arin sha'anunnuka da muƙaman Annabawa da Imamai: Bayan tabbatuwar ismarta, tana kasancewa tare da ba'arin sha'annunka da suka keɓantu da Annabawa da Imamai, misalin hujjar zantukanta, ayyukanta da abubuwan da ta goyi baya, haka marja'iyyar addini, da haƙƙin yin tafsiri da bayanin addini.[5]
  • Ma'aunin tantance gaskiya daga ƙarya: Kan asasin ismar Fatima (S), za ta iya kasancewa abar koyi abar riƙa maudi'i cikin mas'alolin addini daban-daban misalin nuna rashin amincewar da ta yi kan kwacen halifanci da aka yi wa Imam Ali (A.S) da kwace mata gonar fadak, za a ƙirga ta matsayin ma'uni da sikelin tantance gaskiya da ƙarya.[6]
  • Kasancewa abar koyi: Idan aka yarda da ismarta za ta iya kasance kammlalliyar abar koyi cikin bakiɗayan fagage rayuwa, kamar yadda hakan ya zo ƙarara a ba'arin ayoyi[7] game da Annabawa.[8]

An bijiro da batun Ismar Sayyida Fatima (S) a cikin litattafan tafsiri a ƙarshe-ƙarshen bayanin wasu ayoyin kur'ani, kasancewar wannan bahasi cikin bahasussukan madogaran kalam da usulul fiƙhi.[9] an ce tarihin magana kan ismar Sayyida Fatima (S) wani abu daɗaɗɗe da yake komawa zuwa ga zamanin Manzon Allah (S.A.W) da kuma wasu ba'arin zantukansa da ba'arin ayoyi kamar misalin ayar mubahala da ayar taɗhir.[10] Rahotannin tarihi na farko game da ismar Sayyida Fatima (S) su ma su na komawa zuwa ga zamani bayan wafatin Annabi (S.A.W) zuwa ga abin da ya faru na labarin kwace gonar fadak inda Imam Ali (A.S).[11] ya kafa hujja da ayar taɗhir game da ismarta.[12]

Kafa Hujja da Ayar Taɗhir Domin Tabbatar Da Ismar SayyIda Fatima (S)

Tushen ƙasida: Ayar Taɗhir

Malaman shi'a sun dogara da ayar taɗhir cikin tabbatar da ismar Sayyida Fatima (S),[13] kan asasin riwayoyi da shi'a.[14] da Ahlus-Sunna suka naƙalto.[15] wannan aya ta taɗhir ta sauka game da sha'anin as'habul kisa'i (ma'abota bargo), da haka ne ya zama abin nufi daga Ahlul-baiti sune mutane biyar: manzon Allah (S.A.W), Imam Ali (A.S) Sayyida Zahara (S) Hassan da Husaini (A.S).[16] Kan asasin ba'arin riwayoyi, ya zo cewa Annabi (S.A.W) cikin lokacin kowacce sallar asubahi, a wata riwayar kuma a lokacin kowacce sallah ya zuwa gidan Sayyida Fatima (S) ya yi sallama ya ce: ya Ahlul-baiti sallƙ,sallƙ,sannan ya karanta ayar taɗhir.[17] Fakhrur Razi yana ganin riwayoyin da suka zo game da saukar ayar taɗhir cikin sha'anin Ahlul-baiti riwayoyi ne aka yi ittifaƙi a kansu.[18] Cikin wannan riwayoyi an ba da labarin iradar Allah kan tafiyar da dukkanin datti da kazanta daga Ahlul-baiti (A.S), wanda hakan yake ba da ma'anar isma.[19] Cikin wata riwaya da aka naƙalto daga Annabi (S.A.W) waɗanda ayar taɗhir ta sauka cikin sha'aninsu haƙiƙa ma'asumai ne kuma sune: ni Ali da Fatima, Hassan da Husaini (A.S).[20] Sayyidina Ali (A.S) cikin labarin abin da ya faru kan kwace fadak tare da jingina da ayar taɗhir da ya yi ya tabbatar da tsarkakar Fatima (S) daga dukkanin zunubi.[21] Ayar mubahala ita ma tana nuni zuwa ga ismar Sayyida Fatima (S).[22]

Tabbatar Da Ismar Sayyida Fatima Tare da Jingina Da Hadis Bad'atu

Tushen: ƙasida: Hadis Bad'atu

Hadis bad'atu ɗaya ne daga dalilai kan ismar Sayyida Fatima (S).[23] Cikin wannan hadisi da Allama Majlisi ya lissafa shi matsayin hadisi mutawatiri.[24] Cutar da Fatima da sanya fushi, daidai yake da cutawa Annabi (S.A.W) da fusata shi, haka nan yardarta yardarsa, kan wannan asasi, idan Fatima (S) ya zamana tana aikata zunubi saki babu ƙaidi cikin kowanne irin hali ne, cutar da ita da fusata ta ba zai taɓa zama cutar da Manzon Allah (S.A.W) da fusata shi ba, saboda alal misali idan wani mutum cikin hanata aikata zunubi ya zamana ya fusata ta, wannan fushin ya kasance ba a mahallinsa ba, da haka ne ba za a ƙirga shi cikin fusata Annabi (S.A.W) da baƙanta masa.[25] kasantuwar ubangiji ba ya yarda face ayyuka nagargaru kuma baya amincewa da saɓawa umarninsa da kuma aikata zunubi, idan Fatima (S) ta aikata zunubi zai zamana ta yarda da wani abu da Allah yake fushi kansa.[26] kuma sun fassara shi kan ismar saki babu ƙaidi daga aikata saɓo da kuskure, kamar misalin Ayatullahi wahid khurasani.[27] Hadisin bad'ati an naƙalto shi a madogaran Ahlus-Sunna misalin Sahihul Bukhari,[28] da Sahihu Muslim[29] duka sun kawo shi[30] a cikin ba'arin riwayoyi ya zo cewa yardar Fatima da fushinta dai-dai yake da yarda da kuma fushin ubangiji.[31]

Tabbatar Ismar Fatima Tare da Jingina Da Hadisin Saƙlaini Da Hadisin Safina

Hadisai da suke tabbatar da ismar Ahlul-baiti (A.S) misalin hadis saƙlaini da hadis safina su ma su na cikin jumlar hadisai da ake lissafa su dalilai kan ismar Fatima (S).[32] saboda babu kokwanto kan kasancewar Fatima ɗaya daga cikin Ahlul-baiti (A.S).[33] A cewar Allama Majlisi hadisan da suke shiryarwa kan wajabcin riƙo Ahlul-baiti (A.S) misalin hadisin saƙlaini da hadisin safina, hadisai ne da suke shiryarwa kan ismar Fatima (S) saboda wajabcin kaɗai yana tabbata ne kan ma'asumai, mutumin da yake aikata zunubi bawai kaɗai ba wajibi bane riƙo da shi, bari dai daga babi hani da mummuna inkari kansa ma wajibi kan mutane.[34] Ya zo cikin wata riwaya da Annabi (S.A.W) a daren mi'iraji ya ga hasken Fatima da Imaman shi'a ya tambayi Allah su wane ne waɗannan, sai wani sauti ya fito yana faɗin sune Ali, Fatima, Hassan da Husaini da ƴaƴan Husaini, su ɗin tsarkakakku ne ma'asumai.[35]

Mahangar Ahlus-Sunna Dangane da Ismar Sayyida Fatima (S)

Ba'arin malaman Ahlus-Sunna misalin Shahabud-dini Alusi (Wafati: 1270.h.ƙ) malamin tafsirin kur'ani, kan asasin ayar:

«وَإِذْ قَالَتِ الْمَلَائِكَةُ يَا مَرْيَمُ إِنَّ اللهَ اصْطَفَاكِ وَطَهَّرَكِ وَاصْطَفَاكِ عَلَىٰ نِسَاءِ الْعَالَمِينَ؛

Yayin da mala'iku suka ce ya maryam lallai Allah ya zaɓeki ya tsarkakeki kan matan duniya.[36] ya ce haƙiƙa Allah ya tsarkake Sayyida maryam daga zunubi bayan ita kuma bayan nan yana ganin Fatima ta fifici maryam (s)[37] A cewar Hassan Zade Amoli (Wafati:1400.h.shamsi) malamin shi'a, lallai Fakhrur Razi malamin tafsiri na Ahlus-Sunna a ƙarni na shida bayan hijira tare da cewa ya yi shakka kan komai hatta ta kai ga ya shahara da sunan limamin masu shakku, amma tare da hakka bai yi shakka da kokwanto ba cikin ismar Sayyida Zahara (S) ba.[38]

Bayanin kula

  1. Misali, duba Mufid, Al-Fusul al-Mukhtarƙ,1413 ƙ,shafi:88; Sayyid Morteza, Al-Shafi fi al-Umamƙ,1410 ƙ, juzu'i na 4, shafi na 95; Ibn Shahr Ashub, Manaƙib al-Abi Talib, 1379 ƙ,juzu'i na 3, shafi na 332; Majlesi, Bihar al-Anwar, 1403 ƙ,juzu'i na 29, shafi na 335.
  2. Kafi wa Shafiyan, “Ismat Fatimah (AS)”, shafi na 69.
  3. Mufid, Al-Fusul Al-Mukhtara, 1413 ƙ, shafi na 88.
  4. Majlesi, Bihar al-Anwar, 1403 ƙ,juzu'i na 29, shafi na 335.
  5. Kafi wa Shafiyan, “Ismat Fatimah (AS)”, shafi na 72.
  6. Kafi wa Shafiyan, “Ismat Fatimah (AS)”, shafi na 72.
  7. Duba Suratul Ahzab, aya ta 21; Suratul Momtahnƙ,aya ta 4
  8. afi wa Shafiyan, “Ismat Fatimah (AS)”, shafi na 72.
  9. afi wa Shafiyan, “Ismat Fatimah (AS)”, shafi na 72.
  10. afi wa Shafiyan, “Ismat Fatimah (AS)”, shafi na 71.
  11. Duba Sadouƙ, Ilalul Shara'i, 1385, juzu'i na 1, shafi na 191 da 192.
  12. Kafi wa Shafiyan, “Ismat Fatimah (AS)”, shafi na 71.
  13. Misali, duba Seyyid Morteza, al-Shafi fi al-imamƙ,1410 ƙ,juzu'i na 4, shafi na 95; Majlesi, Bihar al-Anwar, 1403 ƙ,juzu'i na 29, shafi na 335.
  14. Alal misali, ka duba Kulayni, al-Kafi, 1407 A.H., wol. 1, shafi na 287;
  15. Alal misali, ka duba Musulmi Neyshaburi, Sahih Muslim, Dar Ihya al-Turath al-Arabi, wol. 4, shafi na 1883, hadisi 61, Tirmidhi, Sunan al-Tazmidhi, wol. 5, shafi na 351, hadisi 3205 da p. 352, hadisi 3206 da p. 663, hadisi 3787, da Ibn Hanbal, Musnad al-Imam Ahmad ibn Hanbal, wol. 28, shafi na 195, wol. 44, pp. 118-121.
  16. Bahrani, Ghaya al-Maram, 1422 ƙ,juzu'i na 3, shafi na 193; Tabatabaei, Al-Mizan, 1390 ƙ,juzu'i na 16, shafi na 311; Sobhani, Manshur Jawed, 2003, juzu'i na 4, shafi na 387-392.
  17. Ka duba Kufi, Tafsir Furat al-Kufi, 1410 A.H., shafi na 338 da 339, Tabataba'i, Al-Mizan, 1390 ƙ, wol. 16, shafi na 318 da 319, Tabarani, Al-Mu'jam al-Kabir, 1415 A.H., wol. 22, shafi na 402.
  18. Fakhr Razi, al-Tafsir al-Kabir, 1420 ƙ, juzu'i na 8, shafi na 247.
  19. Faryab, Imat Imam dar tarikh Tafakkuri Imamiyyƙ,1390, shafi na 335 da 336.
  20. Kufi, Tafsirul Furat al-Kufi, 1410ƙ, shafi na 339 da 340.
  21. Duba Sadouƙ, Ilalul Shara'i, 1385, juzu'i na 1, shafi na 191 da 192.
  22. Shafi na 132 «آیات مباهله،‌ تطهیر و روایات، عصمت حضرت فاطمه(س) را ثابت می‌کند»،Kamfanin dilancin labarai na Shabistan.
  23. Misali, duba Seyyid Morteza, al-Shafi fi al-imamƙ,1410 ƙ,juzu'i na 4, shafi na 95; Ibnshahr Ashub, Manaƙib Al Abi Talib, 1379, Juzu'i na 3, shafi na 333; Majlesi, Bihar al-Anwar, 1403 ƙ,juzu'i na 29, shafi na 335.
  24. Majlesi, Bihar al-Anwar, 1403 ƙ,juzu'i na 29, shafi na 335.
  25. Sayyid Morteza, Al-Shafi fi al-Umamƙ,1410 ƙ,juzu'i na 4, shafi na 95; Ibnshahr Ashub, Manaƙib Al Abi Talib, 1379, Juzu'i na 3, shafi na 333; Majlesi, Bihar al-Anwar, 1403 ƙ,juzu'i na 29, shafi na 337 da 338.
  26. Sobhani,Pajuheshi dar shenanakti ismat Imam, 2009, shafi na 27.
  27. Duba Ruhi Barandagh, ƙalamru ismat Fatemeh Zahra (A.S) dar Hadis Fatemeh bad'atun minni', shafi na 83-85.
  28. Bukhari, Sahihul Bukhari, 1422 ƙ,juzu'i na 5, shafi na 21 da 29.
  29. Muslim Neishabouri, Sahih Muslim, Dar Ihya al-Trath al-Arabi, juzu'i na 4, 1902 da 1903.
  30. Duba Majlisi, Bihar al-Anwar, 1403 ƙ,juzu'i na 29, shafi na 336 da 337; Tabarani, Al-Mu'jam al-Kabir, 1415 Hijira, juzu'i na 22, shafi na 404 da 405.
  31. Duba: Sadouƙ, Ayoun Akhbar al-Reza (AS), 1378 ƙ,Juzu'i na 2, shafi na 46 da 47; Mufid, Al-Amali, 1413 ƙ,shafi na 95; Ibn Maghazali, Manaƙib al-Imam Ali bin Abi Talib, Darul Adwa, 284 da 285.
  32. Sobhani, Pajuheshi dar shenakti wa ismat, 2009, shafi na 27; Mohaghegh, Ismat aza didgahe Shi'a wa ahle tasannun. 1391, shafi na 256..
  33. Mohaghegh, Ismat aza didgahe Shi'a wa ahle tasannun. 1391, shafi na 256.
  34. Majlisi, Bihar al-Anwar, 1403 ƙ,juzu'i na 29, shafi na 340.
  35. Khazaz al-Razi, Kifayat al-Athar, 1401 A.H., shafi na 185 da 186.
  36. Alu Imran, aya ta 42
  37. Duba Alousi, Ruh al-Ma'ani, 1415 ƙ,juzu'i na 2, shafi na 149-150; Mazhari, Tafsir al-Ahnathoni, 1412 ƙ,juzu'i na 2, sashe na 1, shafi na 47 da 48.
  38. Hassanzadeh Amoli,Hezar wa Yek Nukte, 1365, shafi na 603, aya ta 748.

Nassoshi

  • Alousi, Mahmoud bin Abdullƙ,Ruh al-Ma'ani fi Tafsir al-ƙur'an al-Azeem da Al-Saba al-Mathani, bincike na Ali Abd al-Bari Attiyƙ,Beirut, Gidan bugawa na al-Alamiya, Littafin Muhammad Ali Bizoun, 1415ƙ.
  • «آیات مباهله،‌ تطهیر و روایات، عصمت حضرت فاطمه(س) را ثابت می‌کند»، خبرگزاری شبستان، (Ayoyin Mubahala, da Tathir, da kuma riwayoyi, suna tabbatar da rashin kuskure (is'ma) na Sayyida Fadima (A.S)) Kamfanin Dillancin Labarai na Shabestan. Ranar da aka rubuta labarin: 10 ga Maris, 2018., Ranar da aka duba shi: 2 ga Satumba, 2021M.
  • Ibn Hanbal, Ahmad bn Muhammad bn Hanbal, Musnad al-Imam Ahmad bn Hanbal, shuaib al-Arnaut, Adel Murshid da Dijran, Beirut, wanda ya assasa sakon, babin farko, 1421ƙ,
  • Ibn Shahr Ashub, Muhammad ibn Ali, Manaƙib na iyalan Abu Talib (a.s), Ƙum, Alama, babi na farko, 1379ƙ.
  • Ibn Mughazli, Munaƙib na Imam Ali bin Abi Talib, Gidan bugawa na Adwa, babu kwanan wata.
  • Ansari. Zanjani, Ismail, Mausu'atul Al-Kubra An Fatima Al-Zahra (S.A), Ƙum, bugun jagoranmu, ‌Ta.
  • Bahrani, Sayyid Hashem, Ghayat al-Maram Wa Hujjatul Khisam Fi Ta'ayinil Imam, bincike Sayyid Ali Ashour, Beirut, Gidauniyar tarihin Musulunci, bugu na farko, 1422ƙ.
  • Bukhari, Muhammad bin Ismail, Sahih al-Bukhari, bugun Muhammad Zuhair bin Nasser Al-Nasser, Beirut, Gidan bugawa na Tauƙi. babi na farko, 1422ƙ.
  • Tirmidhi, Muhammad Ibn Isa, Sunan Tazmizi, bincike da ƙarin bayani Ahmad Muhammad Shakir, Muhammad Fu'ad Abdul Baƙi da Ibrahim Atwa, Masar, Mustafa Al-Babi Al-Halabi Makaranta da Kamfanin Buga Littattafai, bugu na biyu, 1975M-1395ƙ, Tehran, Raja, bugu na 5,
  • Hassanzadeh Amoli, Hassan,Hezar wa Yek Nukte, Tehran, Mabugar Raja, bugu na biyar, 1365SH.
  • Khazaz Razi, Ali bin Muhammad,Kifayatul Asri Fin Nassi Alal A'immati Isna Ashar, bincike da gyara Abdul Latif Hosni Kohkamari, Ƙum, Mawallafar Bidar, 1401ƙ.
  • Kawous Rouhi Barandagh، «قلمرو عصمت فاطمه زهرا(س) در حدیث فاطمه بضعة منی», (Matsayin rashin kuskure (Is'ma) na Sayyida Fatimah al-Zahra (A.S) a cikin hadisin "Fatimah yanki ne na jikina.) Mujallar Nazarin Akida da Ilimin Tauhidi, fitowa ta 22, bazaran shekarar 2016M.
  • Subhani, Jafar, Pajuheshi shenakti wa Ismat mama, Tehran, Cibiyar Al-Sadiƙ (A.S). bugu na biyu, 1410ƙ.
  • Sayyed Morteza, Ali bin Hossein, Al-Shafi fi Al-imamƙ,Tehran, Cibiyar Al-Sadiƙ (A.S), bugu na biyu, 1410ƙ.
  • Sadouƙ, Muhammad Bin Ali, Ilalul Shara'i, Ƙum, Kantin sayar da littattafai na Dawari, bugun farko, 1385SH.
  • Sadouƙ, Muhammad Bin Ali, Ilalul Shara'i, Ƙum, Shagon Littattafai na Dauri, bugu na daya, 1385SH.
  • Tabatabaei, Seyyed Mohammad Hossein, Al-Mizan fi Tafsir al-ƙur'an, Beirut, Cibiyar Al-Alami, bugu na biyu, 1390ƙ.
  • Tabrani, Sulaiman ibn Ahmad, Al-Mu'ajm al-Kabir, wanda Hamdi bn Abdil-Majid al-Salfi ya yi bincike a Alƙahira, Laburaren Ibn Taimiyya,Babi na biyu, 1415ƙ.
  • Faryab, Muhammad Hossein, Isamat Imam dar tarikh tafkkuri Imamiyya ta payane ƙarne panjom hijiri, Ƙum, Cibiyar Ilimi da Bincike ta Imam Khumaini, bugun farko, 1390SH.
  • Fakhr Razi, Muhammad bin Omar, Al-Tafsir al-Kabir (Mufatih al-Ghayb), Beirut,Gidan Raya Gadon Al'adun Larabawa, bugu na uku, 1420ƙ.
  • Kafi, Abdul Hossein da Jawad Shafiian, 'Ismat Fatemeh (A.S)', dar daneshnameh Fatemi(wol.2), Tehran, Cibiyar Nazarin Al'adun Musulunci da Tunani, bugun farko, 1393SH.
  • Kulaini, Muhammad ibn Yaƙub, al-Kafi, binciken Ali Akbar Ghaffari da Muhammad Akhundi, Tehran, Gidan Littattafan Musulunci, na hudu, 1407ƙ.
  • Kufi, Forat bin Ibrahim, Tafsir Forat al-Kufi, bincike da gyara na Muhammad Kazem, Tehran, Ma'aikatar Al'adu da Shiryar Musulunci, bugu na farko, 1410ƙ.
  • Majlisi, Muhammad Baƙir, Bihar al-Anwar al-Jami'ah Lidar al-Akhbar al-Akhbar al-Imam al-Athar (A.S), Beirut,Gidan Raya Gadon Al'adun Larabawa, 1403ƙ.
  • Mohaghegh, Fatemeh, Ismat az didgahe Shi'a waahlutasannun, bincike da bincike Khalil Bakshizadeh, Ƙum, Mawallafar Ashiane Mehr, bugu na farko, 1391SH.
  • Muslim Neishabouri, Muslim bin Hajjaj, Sahih Muslim, bincike na Muhammad Fouad Abdul Baƙi, Beirut,Gidan Raya Gadon Al'adun Larabawa, babu kwanan wata.
  • Mazhari, Muhammad Thanaullƙ,Tafseer al-Mazhari, Pakistan-Kuwait, Laburaren Rushdieh, bugu na farko, 1412ƙ.
  • Mufid, Muhammad bin Muhammad bin Nu'man, al-Mali, bincike na Hossein Ostadoli da Ali Akbar Ghafari, Ƙum, Babban taron tunawa da Sheikh Mufid, bugu na farko, 1413ƙ.
  • Mufid, Muhammad bin Muhammad bin Numan, Al-Fusul Al-Mukhtara, Ƙum, Babban taron tunawa da Sheikh Mufid, bugu na farko, 1413ƙ.

Sadarwa Ta Waje

(Matsayin (iyakar) kariya daga zunubi (Ismah) na Fadima Zahra (AS) a cikin hadisin Faɗima tsoka ce daga gare ni)