Gidan Sayyada Fatima (S)

Gidan Sayyada Fatima (S) (Larabci:دار السيدة فاطمة عليها السلام) gida ne da yake jikin masallacin Annabi wanda Sayyida Zahra da Imam Ali (A.S) suke rayuwa a cikinsa, da yawa daga malaman shi'a suna ganin ƙabarin Sayyida Fatima yana cikin gidanta, falalar da wannan gida yake da shi ya samo asali ne daga inda Allah ya bada umarnin rufe ko wace ƙofar gida da take haɗe da masallacin Annabi, banda ta gidan Sayyida Fatima (S).
Yazo a hadisi daga Imam Sadiƙ (A.S) cewa yin Sallah a a wannan gida ya fi yin sallah a filin masallacin Annabi lada da daraja, an ruguje wannan gida a zamanin Banu Umayya wajan faɗaɗa masallacin Annabi, an zagaye ɗakin da aka binne Annabi a ciki da gini mai kyau.
Wasu suna ganin gidan Sayyida Fatima (S) da aka kai wa hari, a harin da aka raunata ta shi ne dai gidan Imam Ali (A.S) da ke unguwar Bani Hashim. Waɗannan masu binciken sun faɗi dalilai da hujjojin samuwar wannan gida a unguwar Banu Hashim da kuma yadda harin ya kasance.
Matsayin Gidan Sayyad Fatima
Gidan Sayyida Fatima (S) yana nufin gidan da take rayuwa acikinsa a garin Madina, wanda ya zo a cikin ruwayoyi na Shi'a da Ahlus-sunna da kuma na tarihi game da falalarta[1] da abin da ya faru na harin da aka kai mata[2] Har ila yau, wasu malaman Shi'a suna ganin shi ne in da aka binneta.[3]
Ya zo a cikin hadisin Shi'a da Ahlus-sunna cewa Annabi (S.A.W) ya gabatar da gidan Fatima da Ali (A.S) a matsayin ɗaya daga cikin mafi kyawun misalan gidaje wanda ya zo a aya ta 36 a cikin suratul Nur:
A cikin gidajen da Allah ya yi musu izini a girmama kuma ɗaukaka ambaton sunansa. A cikin waɗannan gidaje anayi masa tas'bihi kowace safiya da maraice.[4]
Gidan sayyada Fatima shi ne mahaifar ƴaƴanta[5] kuma a bisa abin da yazo a ruwaya shi ne gunda aka haifi Imam Sajjad (A.S).[6] A ruwayar da ta zo a cikin littafin Alkafi, Imam Sadik (A.S) ya ce salla a gidan Fatima (S) tafi daraja fiye da yin sallah a filin masallacin manzon Allah,[7] an ruwaito cewa Imam Jawad (A.S) ya kasance yana sallah a gidan Sayyida Fatima (S).[8] A wasu garuruwan Iran a lokacin Ayyamu Fatimiyya ana gine gine da kwafi na unguwar Bani Hashim da gidan Sayyida Fatima, kuma jama'a suna turuwa don ziyartar gurin domin su yi kallo.[9]
Yunkuri Sauyawa Sayyada Fatima (S) Gida Bayan Aure
Ibn Sa'ad masanin tarihi a ƙarni na 3 hijriyya, ya ruwaito daga Imam Baƙir (A.S) cewa Imam Ali (A.S) ya gina wani gida da ke da nisa kaɗan da gidan Manzon Allah bayan ya auri Fatima (S) Annabi ya ce musu yana son `yarsa ta zauna kusa da gidansa. sai dai bai san yaya zai yi ba tin da babu wani gida da ya yi saura a kusa da nasa wanda ba mutane a ciki, sai Sayyida Fatima (S) ta nemi Annabi da ya yi magana da Harisatu Bin Nu'uman domin su zauna a gidansa da yake jikin gidan Annabi[10] saboda a baya ya bada wasu gidajensa dan Manzo Allah ya zauna da matansa a ciki[11] Sai Annabi ya ce ba zai iya tambayar sa ba saboda a ba ya ya ba shi , sai labarin abin da yake faruwa ya kai ga kunnen Harisatu, saboda haka, sai ya bai wa Annabi gidan nasa, ya ce Annabi ya karɓar dukiyarsa ya fi masa alhairi daga yaƙi karɓa.[12]
A cewar wasu majiyoyin Shi'a, Manzon Allah ya buƙaci Imam Ali (A.S) ya shirya musu gida da za su zauna shida matarsa bayan aure. sai Imam Ali (A.S) ya ce babu wani gida kusa da gidan Annabi sai gidan Harisatu Bin Nu'uman. Annabi ya ce Harisatu ya ba shi wasu daga cikin gidajensa, sai ya ji kunyar faɗa masa ya kuma ba shi wani. Da Harisatu ya samu labarin hakan sai ya taso da kansa ya zo wurin Annabi ya ba shi gidansa, da haka Ali (A.S) da Fatima (S) suka koma gidan Harisatu.[13]
Gida Ɗaya Tilo Mai Ƙofa Cikin Masallaci
- Ku duba: Saddul Abwabi
Gidan Sayyida Fatima yana gabas da masallacin Annabi (S.A.W) kuma a tsakiyar gidajen Manzon Allah (S.A.W.).[14]Wannan gidan yana da ƙofofi guda biyu: ƙofa ɗaya tana buɗewa daga cikin masallaci, ɗaya ƙofar ta wajen masallacin,[15] da umurnin Allah ya zo sai aka rufe dukkan ƙofofin masallacin Annabi (S.A.W) sai wannan aka bari.[16] Saddul Abwabi wata falala ce ta Imam Ali (A.S) shi kadai[17]
Gidan Sayyida Fatima (S) yana bayan gidan Manzon Allah (s.a.w).[18] A tsakanin waɗannan gidaje biyu akwai wata ƴar ƙaramar taga.[19] daga nan ne Manzon Allah ya ke tambayar `yarsa halin da take.[20] Akwai wani dare da aka sami jayayya tsakanin Sayyida Fatima da Aisha matar Manzon Allah (S.A.W) sai hakan ya ɓata ran Fatima (A.S) sai Manzon Allah (S.A.W) ya rufe ƙofar bisa buƙar Sayyida Fatima (S).[21]
Harin Da Aka Kai Gidan Sayyada Fatima (S)
Kamar yadda majiyoyin Shi'a da Ahlus-sunna suka ruwaito, bayan wafatin Manzon Allah (S.A.W) da waƙi'ar Saƙifa, wasu daga cikin Sahabbai sun garzaya gidan don tilastawa Imam Ali (A.S) yin bai'a ga Abubakar, da tilastawa wanda suka taru a gidan Imam yin ba[22] A cewar majiyoyin Shi'a, a lokacin wannan harin ne aka ƙona ƙofar gidan,[23] kuma a sakamakon raunukan da Sayyida Fatima ta samu ne ya janyo zubewar cikin (Muhsin)[24] sannan sanadin ciwon ya zamanto ajalinta, ta yi shahada bayan wani lokaci[25].
Wanne Gida aka Kai Hari?
Wasu masu bincike na ganin cewa harin da aka kai gidan Fatima ba a wannan gidan da ke kusa da masallacin Annabi ba ne, gidan da aka kai wa hari yana da nisa da masallaci[26] Kamar yadda Muhammad Sadiƙ Najmi (Rasuwa: 1390 kalandar Farsi) A cikin littafin "Tarikhe Harame A'imme Baƙi'a" wasu rahotannin tarihi sun tabbatar da wannan hasashen. Daga cikin su akwai rahoton cewa lokacin da suka kai Ali (A.S) masallaci don yin mubaya'a ga Abubakar, mutane sun taru suna kallon abubuwan da suke faruwa a titunan Madina[27] Wannan rahoton yana cikin littafin Saƙifa Wa Fadak na Ahmad bin Abdul-Aziz Jauhari Basari (Rasuwa: 323 bayan hijira).[28] Kuma an ce wannan gida yana gabas da masallacin Annabi, a bayan maƙabartar Baƙi'a, kusa da gidan Abu Ayyub Ansari, gida ne mai ɗauke da rumbun ajiya, ɗakuna da dama da babbar kofar katako.[29]
Samhudi (Rasuwa: 911 bayan hijira), malamin Ahlus-Ahlus-sunna mai bincike kan tarihin garin Madina, shi ma ya yi magana a kan gidan da ke kusa da maƙabartar Baki'a ,wanda yake na Imam Ali (A.S) ne,[30] cikin littafin Tabakatul Kubra daga madogaran tarihi da aka rubuta a ƙarni na uku an ambaci sunan gidan Fatima da cewa yana kusa da Baki'a[31] Wasu suna ganin wannan gida shi ne dai wanda Harisatu Bin Nu'uman ya bawa Fatima kyauta dan ta zauna a cikinsa.[32]
Sayyid Jafar Murtada Amili (Rasuwa: 1441H), masanin tarihin Shi'a, yana ganin cewa an kai harin ne a gidan da aka ruwaito labarin Saddul Al-Abwab (Batun rufe ƙofofin da suke ta masallacin Annabi da barin iya ta gidan Sayyada Fatima)[33]
An Binne Sayyada Fatima A Gidanta Ne?
A cewar Sayyid Jafar Murtada Amili, masanin tarihin Musulunci da na Shi'a, (ya rasu: 1441), ba zai yiwu a iya tantance inda ƙabarin Sayyida Fatima yake ba.[34] Kamar yanda Isma'il Ansari Zanjani ya ruwaito a cikin littafin Al-Mausuatul-Kubra an Fatimatul-Zahra, mafi yawan malaman Shi'a sun yi imani da cewa an binne Fatima a gidanta.[35] an ruwaito a cikin faɗin Imam Ali (A.S) a lokacin jana'izar Fatima (S) yana cewa:
Mai sauka kusa da kai
wannan yana daɗa tabbatar da an binne Fatima (S) a gidanta.[36]
An Sanya Gabaɗayan Gidanta Cikin Ginin Kabarin Annabi (S.A.W)
An ruguje gidan Fatima a zamanin Abdul-Malik bin Marwan (Mulki: 65-86 bayan hijira).[37] ko Walid bin Abdul-Malik (Mulki: 86-96 bayan hijira)[38] domin raya masallacin Annabi. An haɗe ɗakin ta dana Annabi a guri ɗaya.[39]
Bayanin kula
- ↑ Misali, dubi Kulaini, al-Kafi, 1407, juzu'i na 4, shafi na 556.
- ↑ Masoudi, Isbatul wasiyya, 1384, juzu'i na 1, shafi na 146
- ↑ Misali, duba: Sheikh Sadouq, Man La Yahdara al-Faqih, 1413 AH, juzu'i na 2, shafi na 572.
- ↑ Siyuti, Durrul al-Manthor, Dar al-Fikr, juzu'i na 6, shafi na 203; Erbali, Kashf al-Ghumma, 1421 AH, juzu'i na 1, shafi na 313.
- ↑ طبسی، «گزارشی از خانه زهرا علیها السلام»،Shafin Hauza.
- ↑ Tabari Amoli, Dalai al-Imamah, 1413 AH, shafi na 191.
- ↑ Kulaini, al-Kafi, 1407 AH, juzu'i na 4, shafi na 556.
- ↑ Kulaini, Al-Kafi, 1407 AH, juzu'i na 1, shafi 493.
- ↑ «روایتی از «کوچههای مادری»، Kamfanin Dillancin labarai na Jamhuriyar Muslunci.
- ↑ Ibn Saad, Tabaqat Al-Kubra, 1410, juzu'i na 8, shafi na 132.
- ↑ Ameli, Sahih Mn Sirah Imam Ali (A.S), 2009, juzu'i na 3, shafi na 132-133.
- ↑ Ibn Saad, Tabaqat al-Kubra, 1410, juzu'i na 8, shafi na 132.
- ↑ Tabarsi, Ilamul Al-Wora bi Alam Al-Huda, 1390 AH, shafi na 71; Majlesi, Bihar al-Anwar, 1403 AH, juzu'i na 19, shafi na 113.
- ↑ Tabasi، «گزارشی از خانه زهرا علیها السلام»، Shafin Hauza.
- ↑ Qaidan, Darsenameh Amakin mazhabi Makkeh mukarrama wa Madina, 1390, shafi na 177.
- ↑ Ibn Kathir, al-Bidaiya wa al-Nihaya, 1407H, juzu'i na 7, shafi na 342.
- ↑ Hakim Neishaburi, al-Mustadrak Ali al-Sahihin, Beirut, juzu'i na 3, shafi na 125.
- ↑ Qaidan, Darsenameh Amakin mazhabi Makkeh mukarrama wa Madina, 1390, shafi na 177.
- ↑ Al-Sagheer, Tarihin Imam Ali (A.S) Siratuhu wa kiyadatuhu fil al-Manhaj al-Tahlili, 2002. Juzu'i na 1, shafi na 31.
- ↑ Samhoudi, Wafa al-Wafa bi Akhbar Dar Al-Mustafa, 2006, juzu'i na 2, shafi na 57.
- ↑ Sabri Basha, EMasu'atu Mir'ati Al-Haramaini al-Sharifaini wa Jazeera al-Arab, 2004, juzu'i na 3, shafi na 262.
- ↑ Tabari, Tarihin A'umam wa Al-Muluk, 1387 A.H., juzu’i na 3, shafi na 202.
- ↑ Salim bin Qays, Kitabu Salim bin Qays, 1420H, juzu’i na 1, shafi 150.
- ↑ Masoudi, Isbatul Wasiyya, 2004, shafi na 146.
- ↑ Tabari, Dalai al-Imamah, 1413H, shafi na 134.
- ↑ Mousavi, "Pasukh Shubuhate Tarikhi ateshe zadane Khuneh dar Ayineh Tarikhi wa riwayat farikaini ", shafi na 140-141.
- ↑ Najmi, Tarikhi Harame A'immeh wa asare digare dar madinaeh munawarra, 1386, shafi na 166-163.
- ↑ Johari Basri, Al-Saqifa wa Fadak, Tehran, shafi na 72.
- ↑ Allahu Akbar«خانه حضرت فاطمه(س) کجا بوده است؟»،Shi'a News
- ↑ Samhoudi, Wafa Al-Wafa, 2006, juzu'i na 2, shafi na 59.
- ↑ Ibn Saad, Tabaqat Al-Kubra, 1410H, juzu'i na 4, shafi na 40.
- ↑ Duba Qazvini, Fatima al-Zahra (a.s.) Man al-Mahd al-Lahad, 2006, juzu'i na 1, shafi na 157
- ↑ Ameli, Musibar Al-Zahra (AS), 1418 Hijira, Juzu'i na 1, shafi na 177.
- ↑ Ameli, Ma'asatu Al-Zahra (AS), 1418 Hijira, Juzu'i na 1, shafi na 252 da 253.
- ↑ Ansari Zanjani, Al-Masu'a al-Kubra Fatima al-Zahra, 1428 AH, juzu'i na 16, shafi na 113.
- ↑ Makarem Shirazi, Payam Imam Amirul Momineen, 2006, juzu'i na 8, shafi na 32.
- ↑ Ibn Shahr Ashub, Manaqib Al Abi Talib, 1379 Hijira, Juzu'i na 2, shafi na 211.
- ↑ Samhoudi, Wafa al-Wafa bi Akhbar Dar Al-Mustafa, 2006, juzu'i na 2, shafi na 89.
- ↑ Jafarian, Asare Islami Makkeh wa Madina, 2007, shafi na 295.
Nassoshi
- Ibn Jozi, Abd al-Rahman bin Ali, al-Muntazem, bincike na Muhammad Abd al-Qader Atta, Mostafa Abd al-Qader Atta, Beirut, Dar al-Kutb al-Alamiya, bugu na farko, 1412H.
- Ibn Hajr Asqlani, Ahmad bin Ali, Al-Isaba fi Tamy'iz al-Sahaba, bincike na Adel Ahmad Abd al-Mojood, Ali Muhammad Moawad, Beirut, Dar al-Kitab al-Alamiya, bugu na farko, 1415H.
- Ibn Saad, Muhammad Ibn Saad, Tabaqat Al-Kubra, bincike na Muhammad Abd al-Qadir Atta, Beirut, Dar al-Kitab Al-Alamiya, bugu na farko, 1410 A.H.
- Ibnshahr Ashub, Manaqib Al Abi Talib, Amincin Allah ya tabbata a gare shi, Qum, Allamah Publications, bugu na farko, 1379H.
- Ibn Kathir, Ismail bin Umar, al-Bidaiyah wa al-Nihayah, Beirut, Darul Fikr, 1407H.
- Erbali, Ali Ibn Isa, Kashf al-Ghumma fi Marafah al-Imam, Kum, Razi, 1421H.
- Al-Sagheer, Muhammad Hossein, Imam Ali (A.S) Siratuhu wa Kiyadatuhu fi Zau'i al-Manhaj al-Tahlili, Bija, Al-Arif Foundation, 2002.
- Ansari Zanjani Khoini, Ismail, Al-Mausu'a al-Kubra Fatima al-Zahra, amincin Allah ya tabbata a gare ta, Qum, Dilil Ma, 1428 AH/1386.
- Jafarian, Rasul, Asare Islami Makka wa Madina, Tehran, Mashaar, 2007.
- Johari Basri, Ahmad bin Abdul Aziz, Al-Saqifa waa Fadak, bincike da gyara daga Mohammad Hadi Amini, Tehran, Ninoy al-Haditha School, B.T.A.
- Hakim Neishaburi, Muhammad bin Abdullah, Al-Mustadrak Ali Al-Sahihin, Dar al-Marafa, Beirut, Bita.
- Salim bin Qays, littafin Salim bin Qays, Kum, Al-Hadi, 1420H.
- Samhoudi, Ali bin Abdullah, Wafaa al-Wafa bi Akhbar Daril al-Mustafa, Beirut, Dar al-Katb al-Alamiya, 2006.
- Siyuti, Jalaluddin, Aldurrul al-Manthor, Beirut, Dar al-Fekr, Bita.
- Sabri Basha, Ayoub, Mausuatu Mirt'a Al-Haramain al-Sharifain wa Jazeera al-Arab, Majdeh Maarouf, Alkahira, Dar al-Afaq al-Arabiya, ya fassara, 2004.
- Tabarsi, Fazl bin Hasan, Ilamul Al-Wori Bi Alamul Al-Huda, Tehran, Darul Kitab al-Islamiya, bugu na uku, 1390H.
- Tabari Imami, Muhammad bin Jarir bin Rostam, Dalai al-Imamah, Qum, Ba'ath, 1413H.
- Tabari, Muhammad bin Jarir, Tarikh al-Umama wa al-Muluk, Musa al-Alami, Beirut, 4th, 1403H.
- Najmi, Mohammad Sadeq, Tarikhe Harame A'imme Baqi wa digar dar Madina, Tehran, Mashaar Publishing House, 2007.
- Allahu Akbar، «خانه حضرت فاطمه(س) کجا بوده است؟»، Labaran Shi'a, ranar shigowa: Janairu 13, 1401, kwanan wata ziyara: Agusta 21, 1402.
- Makarem Shirazi, Nasser, Payame Imam Amir al-Mu'minin, Tehran, Darul Kutub al-Islamiyya, 2007.* موسوی، سید محمدتقی، «پاسخ به شبهات تاریخی آتش زدن خانه وحی در آیینهی تاریخ و روایات فریقین»،Tarikhe Islami Ayineh Andisheha, Shekara ta 12, Fitowa ta 18, Fada da lokacin sanyi 2020