Ƙungiyar Jihadul-Islam
| Suna | Harkatul Jihadil Islami A Falasɗinu |
|---|---|
| Jagora a yanzu | Ziyad Nakhala |
| Wanda Ya Kafa | Fathi Shaƙaƙi |
| Fitattun Mutane | Abdul-Aziz Auda. Akram Al-ajuri. Nafiz Azam |
| Manufofi | Gwagwarmaya ɗauke da makami domin fatattakar Isra'ila da `yantar da dukkanin garuruwan Falasɗinu da ta mamaye tare da kafa daular Falasɗinu |
| Mazhaba | Ahlus-Sunna |
| Shafin Yanar Gizo | https://jehad.ps |
| Ƙasa | Falasɗinu |
Ƙungiyar Jihadul-Islam (Larabci:حركة الجهاد الإسلامي في فلسطين) ta Falasɗinu ɗaya ce daga cikin ƙungiyoyin gwagwarmayar Falasɗinawa, wanda aka gina ta bisa tasirin hanyar da Imam Khomaini, wadda ya yi imani cewa hanya ɗaya tilo wadda za a iya `yantar da yankunan Falasɗinu ita ce tsayawa tsayin daka da gwagwarmaya kan mamayar Isra'ila. tushen wannan yunƙuri shi ne imani da koyarwar Musulunci da kuma haramta imani da Isra'ila a matsayin ƙasa mai zaman kanta.
Fathi Shaƙaƙi ne ya kafa ƙungiyar Jihadul-Islam a shekarar 1981 a Gaza. Har ila yau, reshen sojojinta ya kai hare-hare da dama kan Isra'ila, haka ita ma Isra'ila ta kashe wasu kwamandojinsu, Babban sakataren wannan ƙungiya shi ne Ziyad Nakhala. Kafin shi Ramadan Abdullah, kafin Ramadan, Fathi Shaƙaƙi ne ke ɗaukar wannan nauyi. Wasu ƙasashe kamar Amurka da Ingila da kuma Tarayyar Turai sun sanya wannan ƙungiya cikin jerin ƙungiyoyin ta'addanci.
Gabatarwa da Kafa Wannan Ƙungiya
Harkar Jihadul islam ɗaya ce daga cikin muhimman ƙungiyoyin gwagwarmayar Falasɗinawa, waɗanda suke ganin gwagwarmaya da daƙiya shi ne hanya ɗaya tilo ta `yanta Ƙudus.[1] Kuma bata goyan bayan yarjejeniya da Isra'ila.[2] Wannan ƙungiyar ba takai Hamas da Fatahu samun magoya baya ba,[3] samuwar wannan ƙungiyar a garin Ƙudus ya temaka mata wajan cigaba sosai [4] Kamar yanda wasu kafafan yaɗa labarai suka ba da rahoto, wannan ƙungiyar ta ƙunshi ɓoyayyan tsari na sirri.[5]
Adawa da yarjejeniyar Oslo (2003), ƙauracewa zaɓen majalisar dokoki (2006), adawa da yarjejeniyar zaman lafiya ta Misra a shekara ta 2014, da matakin warware rikici tsakanin Hamas da gwamnatin Misra (2014) na daga cikin muhimman ayyukan siyasa da ƙungiyar Jihadul-Islam ta aiwatar[6]
An kafa Harkatul Jihadul islam a birnin Gaza a shekara ta 1981 a hannun Fathi Shaƙaƙi, likitan Bafalasɗine,[7] tare da haɗin gwiwar mutane irin su Abdul-Aziz Awda,, Ramadan Abdullah da Nafiz Azzam.[8] A shekarar 1987 a ka kori shuwagabannin ƙungiyar zuwa Lebanon a can suka haɗu da ƙungiyar Hizbullahi Lubnan ta ƙasar Labanon suka sami horo daga dakarun IRGC na Iran.
Hukumar leƙen asiri ta Isra'ila watau Mossad ta kashe Fathi Shaƙaƙi babban sakataren ƙungiyar Jihadul-Islam a shekara ta 1995,[9] daga nan Ramadan Abdullah Shalah (Rasuwu: 2020) ya gaje shi. Ramadan Abdullahi ya taka rawar gani a fagen siyasar wannan yunƙuri.[10] Bayan rashin lafiyar Ramadan Abdullah, an naɗa Ziyad Nakhala a matsayin babban sakataren ƙungiyar a shekarar 2018.[11]

Ƙa'idoji da Mamufofi

Jihadul islam ta ayyana ƙa'idojin ta , waɗanda da ta ginu a kansu : addinin Muslunci shi ne tushen imani da ayyukan wannan gwagwarmaya. A bisa waɗannan ƙa'idoji, dukkanin ƙasar Falasɗinu ƙasa ce ta Musulunci da Larabawa, sannan kuma amincewa da gwamnatin Isra'ila a wannan ƙasa haramun ne, kuma kasancewar Isra'ila a cikin Falasɗinu yana nufin mamayewa da rarraba ƙasashen Musulunci gabaɗaya.[12] Sannan duk wani tsarin mulki da zai nuna Isra'ila ce mai wannan ƙasar, ba za a yarda da shi ba[13]
Ƙungiyar Jihadul-Islam ta Falasɗinu ta bayyana babbar manufarta shi ne `yantar da Falasɗinu gaba ɗaya, ruguza gwamnatin Isra'ila da kafa gwamnatin Musulunci. Sauran manufofin wannan yunƙuri dai su ne: shirya al'ummar Falasɗinu zuwa jihadi na soji da na siyasa, da tsara al'ummar musulmin duniya da kwaɗaitar da su wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansu ga Falasɗinu, da ƙarfafa alaƙa tsakanin Musulmi da `yantar da su da haɗin kai da kira zuwa ga Musulunci da yaɗa koyarwarsa[14]
Harkar Jihadul Islam tana da haɗin gwiwar siyasa da soja da ƙungiyar Hamas,[15] Amma ba ta da dangantaka da ƙungiyar `yantar da Falasɗinu ta (Harkatu Tahir Falasɗiniyya), saboda tsarin ita wannan ƙungiya ta ba ruwansu da addini da kuma son yin sulhu da Isra'ila da kuma amincewa da ita.[16]
Ƙalubalantar Mamayar Da Isra'ila Ta Yi Wa Falasɗinu
Ƙudus Brigades (Saraya Al-ƙuds), shi ne reshen soja da tsaro na ƙungiyar Jihadul-islam, an kafa shi ne a ƙarni na ashirin. Kafin wannan sunan ana kiransa da dakarun Mujahidul-Islam kafin wannan ana kiransa da Kata'ib Saif al-Islam[17] Saraya al-ƙuds ita ce mafi girman rundunar soji a Gaza bayan reshen soja na Hamas[18] Isra'ila ta kashe wasu kwamandojin Jihadul-islam, waɗanda suka haɗa da: Fathi Shaƙaƙi (1995), Isam Barahma (1992), Hani Abid (1994), Mahmud Al-Khawaja (1995), Mahmud Ɗiwaliba (2002), Mahmud Zamɗa (2003), Bashir Al-Dabbash (2004), Khalid Al-Dahduh (2006 ), Daniyal Mansur (2014 AD)[19] da Hassam Abu Harbid (2021), kwamandan reshen soji na Saraya al-ƙuds [19]
Hare-Hare Da Ofireshin
Ɓangaran soja na Jihadul-islam ya kai hare-hare da dama kan yankuwan da Isra'ila ta mamaye,misalin u Baitul Lid, Dizengoff, Kafer Darum, Netsarim, Gabashin Jabaliya, Moraj[20] da Bashaer al-Intisar.[21]
Gwagwarmayar Neman Haƙƙi Ta Shekarar 1987 Miladiyya
A shekarar 1987 Harkar Jihadul-islam ta taka rawar gani a gwagwarmaya ta farko ta Falasdinu (1987).
Jawabin Abdul-Aziz Auda a masallacin Izzud-din Ƙassam na daga cikin muhimman abubuwa a farkon wannan intifada.[22] Isra'ila ta bayyana Ramadan Abdullah a (2000) a matsayin shugaban aiwatar da hare-hare kanta.[23] Shigar da dakarun sojan Jihadul-islam cikin wannan intifada[24] shi ne musabbabin kisan wasu kwamandojin rundunar sojansu da Isra'ila ta yi.
Tarayya a Cikin Yaƙin Tufanul Al-Aƙsa
A cewar wasu kafofin watsa labarai na Turai, ƙungiyar Jihadul-Islam ta shiga cikin yaƙin ɗufan Al-aƙsa (2023), wanda ya yi sanadin mutuwar Isra'ilawa 1400 tare da kame wasu daruruwan Isra'ilawa[25] inji Isra'ila[26] Wannan ƙungiyar ta bayyana cewa ta kama mutane sama da 30 kuma ta hanyar musayan fursunoni kaɗai za ta sake su.[27]
Ba'arin wasu kasashe misalin Amurka, Ingila, Kanada da Japan da kuma tarayyar kasahsen turai sun sanya ƙungiyar Jidaul Islam cikin jerin Kungiyoyin ta'addanci.[28]
Tasirantyuwa Da Juyin Juya halin Muslunci Na Iran
Tun Farko kafa ƙungiyar Jihadul Muslunci ta tasIrantu da tunanin juyin juya halin muslunci na Iran karkashin jagorancin Imam Khomaini.[29] bisa wannan tunani ne suka rike muslunci da koyarwarsa matsayin fitila da jagora cikin gwagwarmaya da jihadi.[30] Fathi Shaƙaƙi gabanin kafa wannan kungiya, ya rubuta littafi mai taken (Imam Al-Khomaini Al-Halli Al-Islami Wal Al-Badil) ma'ana Imam Khomaini hanya samun warwara ta muslunci, da wannan dalili ne Kasar Misra ta kama shi ta tsare shi[31] Ya bayyana tunanin Imam Khomaini da juyin juya halinsa a matsayin mafi kyawun madadin sauran hanyoyin cimma manufofin duniyar musulmi musamman 'yancin Falasɗinu[32] Jihadi domin wannan yunƙuri na goyon bayan Imam Khomaini da tunaninsa da ƙarfafa haɗin kan Shi'a da Ahlus-Sunna ana zarginsa da cewa ya zama shi'a.[33] ƙungiyar jihadil Islami ta nesanta kanta da wannan zargi tare da bayyana cewa sun dora dukkanin ayyunkansa kan koyar mazhabobin Ahlus-sunna[34]
A cewar Khalid al-Baɗash, memba a ofishin siyasa na ƙungiyar Jihadul-Islam, Iran ita ce babbar mai goyon bayan wannan yunƙuri na gwagwarmayar Falasɗinu,[35] Taimakon Iran ya kama daga kuɗi, makaman yaƙi, koyar da sojoji dabarun yaƙi, da al'amuran siyasa[36]Cibiyar Nazarin Siyasar Larabawa, ta bayyana cewa, Harkatul Jihadul Islami rta kasance `yar kallo a lokacin yaƙin basasar Siriya (Farawa: 2011). da kuma harin da ƙawancen ƙasashen Larabawa suka kai wa ƙungiyar Ansarullah ta Yaman (Farawa: 2015), wanda ya sa dangantakarta da Iran ta yi sanyi na wani lokaci[37]
Tashar Talabishin
Cibiyar sadarwar tauraron ɗan Adam ta Falasɗinu Alyoum tana da alaƙa da ƙungiyar Jihadul-slami, wanda babbar cibiyarta ke a Gaza. An sanar da matsalolin kuɗi a matsayin dalilin rufe ofishin wannan cibiyar sadarwa na Urushalim (2015),.[38] daga nan a shekarar 2016 Isra'ila ta rufe ta gabaki ɗaya.[39]
| Layi | Suna | Kafawa | Wanda Ya Kafa | Fitattun Mutane | Shugaba | Mazhaba | Tushe | Logo | Kafofin Labarai |
|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|
| 1 | Harkatu Amal | 1974m | Imam Musa Sadar | Musɗafa Camaran | Nabihu Birri | Shi'a | Labanun |
|
Tashar Talabijin Ta NBC |
| 2 | Ƙungiyar Jihadul-Islam | 1981m | Fatahi Shaƙaƙi | Ramadan Abdullahi Husam Abu Harbid | Ziyad Nakhala | Ahlus-Sunna | Gaza |
|
Tashar Falasɗinil Yaumi |
| 3 | Hizbullahi Lubnan | 1982m | Sayyid Abbas Musawi Sayyid Hassan Nasrullah | Na'im Ƙasim | Shi'a | Labanun | Example | Tashar Al-Manar | |
| 4 | Failaƙ Badar | 1985m | Adnan Ibrahim Abu Mahadi Al-Muhandis | Hadi Al-Amiri | Shi'a | Iraƙ |
![]() |
Tashar Al-Ghadir | |
| 5 | Hamar (Harkar gwagwarmayar Muslunci) | 1987m | Shaik Ahmad Yasin | Abdul-Aziz Rantisi Isma'il Haniyye | Kwamitin wucin gadi na Hamas | Ahlus-Sunna | Falasɗinu |
|
|
| 6 | Dakarun Ƙudus (Failak Ƙudus) | 1990m | Sayyid Ali Khamna'i | Ahmad Wahidi Ƙasim Sulaimani | Isma'il Ƙa'ani | Shi'a | Iran |
![]() |
|
| 7 | Harkatu Ansarullahi Yaman | 1990m | Husaini Al-Husi | Badrud-Dini Al-Husi | Abdul-Malik Al-Husi | Zaidiyya | Yaman |
|
Shabakatu Al-Masira |
| 8 | Kata'ibu Hizbullahi Iraƙ | 2003m | Abu Mahadi Al-Muhandis | Abu Husaini Humaidawi Abu Baƙir As-sa'idi Arzan Allawi | Ahmad Muhsin Farhi Alhumaidawi | Shi'a | Iraƙ |
|
Shabakatu Al-Ittija |
| 9 | Kata'ibu Sayyidush Shuhada Iraƙ | 2003m | Abu Musɗafa Khazali Haj Abu Yusuf | Abu Ala Al-wala'i | Shi'a | Iraƙ |
|
||
| 10 | Asa'ibu Ahlil Haƙƙi | 200m | Ƙaisu Khazali | Abdul_hadi Addaraji Muhammad Al-bahadili | Ƙaisu Khazali | Shi'a | Iraƙ | Example | Shabakatu Al-Ahad | |
| 11 | Harkatu Nujaba | 2013m | Akram Ka'abi | Abu Isa Iƙlim Mushataƙ Kazim Alhawari | Akram Ka'abi | Shi'a | Iraƙ |
|
|
| 12 | Dakarun Zainabiyyu | 2013m | Wasu jama'a daga Fakistan | Zainab Ali Jafari Aƙid Malik Muɗahhar Husaini | Shi'a | Fakistan |
|
||
| 13 | Dakarun Faɗimiyyun | 2013m | Wasu mutane daga mayaƙan Afganistan | Ali Rida Tawassuli Sayyid Muhammad Husaini Sayyid Ahmad Sadat | Shi'a | Afganistan |
|
||
| 14 | Hashadush Sha'abi | 2014m | Hadi Amiri Abu Mahadi Al-Muhandis | Falihu Fayyaz | Shi'a | Iraƙ |
|
Bayanin kula
- ↑ «حدث الساعة.. معلومات تهمک معرفتها عن الجهاد الإسلامی التی أنجبت أسری عملیة جلبوع»، Gidan yanar gizo na gidan labarai na Al Jazeera.
- ↑ «نشأت بمصر، ولعبت دوراً کبیراً بالانتفاضة.. قصة حرکة الجهاد وسر استهداف إسرائیل لها بحربها الأخیرة»،Gidan yanar gizon Larabci Post.
- ↑ «نشأت بمصر، ولعبت دوراً کبیراً بالانتفاضة.. قصة حرکة الجهاد وسر استهداف إسرائیل لها بحربها الأخیرة»Gidan yanar gizon Larabci Post.
- ↑ «نشأت بمصر، ولعبت دوراً کبیراً بالانتفاضة.. قصة حرکة الجهاد وسر استهداف إسرائیل لها بحربها الأخیرة»، Gidan yanar gizon Larabci Post
- ↑ «رويكرد جهاد اسلامي فلسطين در مبارزه با اسرائيل و تفاوتهايش با حماس در چيست؟»Gidan yanar gizo na Euronews.
- ↑ «رویکرد جهاد اسلامی فلسطین در مبارزه با اسرائیل و تفاوتهایش با حماس در چیست؟»، Gidan yanar gizo na Euronews.
- ↑ «حرکة الجهاد الإسلامی»، Gidan yanar gizo na gidan labarai na Al Jazeera.
- ↑ «نشأت بمصر، ولعبت دوراً کبیراً بالانتفاضة.. قصة حرکة الجهاد وسر استهداف إسرائیل لها بحربها الأخیرة», Shafin Larabci Post.
- ↑ «تاریخ حرکة الجهاد الإسلامی فی فلسطین موضوعًا لمحاضرة وحدة الدراسات الاستراتیجیة»،Yanar Gizo na Cibiyar Bincike da Nazarin Larabci
- ↑ «ما هی حرکة "الجهاد الإسلامی" التی تتهمها إسرائیل بقصف المستشفی المعمدانی فی غزة؟»، France24 website.
- ↑ «ما هی حرکة "الجهاد الإسلامی" التی تتهمها إسرائیل بقصف المستشفی المعمدانی فی غزة؟»، France24 website..
- ↑ «نبذة عن حرکة الجهاد الإسلامی فی فلسطین»Gidan yanar gizo na Aljazeera News Network.
- ↑ «نبذة عن حرکة الجهاد الإسلامی فی فلسطین»،Gidan yanar gizo na Aljazeera News Network.
- ↑ «نبذة عن حرکة الجهاد الإسلامی فی فلسطین»، Gidan yanar gizo na Aljazeera News Network
- ↑ «ما هی حرکة الجهاد الإسلامی وما علاقتها بحماس؟»، Shafin Al-Hurrah.
- ↑ «رویکرد جهاد اسلامی فلسطین در مبارزه با اسرائیل و تفاوتهایش با حماس در چیست؟»،Gidan yanar gizo na Euronews.
- ↑ «حدث الساعة.. معلومات تهمک معرفتها عن الجهاد الإسلامی التی أنجبت أسری عملیة جلبوع»Gidan yanar gizo na Aljazeera News Network.
- ↑ «حرکة الجهاد الإسلامی»،TRT Yanar Gizo na Larabci.
- ↑ «حدث الساعة.. معلومات تهمک معرفتها عن الجهاد الإسلامی التی أنجبت أسری عملیة جلبوع»،Gidan yanar gizo na gidan labarai na Al Jazeera.
- ↑ «حدث الساعة.. معلومات تهمک معرفتها عن الجهاد الإسلامی التی أنجبت أسری عملیة جلبوع»،Gidan yanar gizo na gidan labarai na Al Jazeera.
- ↑ «نشأت بمصر، ولعبت دوراً کبیراً بالانتفاضة.. قصة حرکة الجهاد وسر استهداف إسرائیل لها بحربها الأخیرة»، Gidan yanar gizon Larabci Post.
- ↑ «نشأت بمصر، ولعبت دوراً کبیراً بالانتفاضة.. قصة حرکة الجهاد وسر استهداف إسرائیل لها بحربها الأخیرة», Shafin Larabci Post.
- ↑ «نشأت بمصر، ولعبت دوراً کبیراً بالانتفاضة.. قصة حرکة الجهاد وسر استهداف إسرائیل لها بحربها الأخیرة»، , Shafin Larabci Post..
- ↑ الشریف، «حرکة الجهاد الإسلامی فی فلسطین», Gidan yanar gizon Cibiyar Nazarin Falasdinu.
- ↑ «ما هی حرکة "الجهاد الإسلامی" التی تتهمها إسرائیل بقصف المستشفی المعمدانی فی غزة؟»، وبگاه FRANCE.24.
- ↑ «رویکرد جهاد اسلامی فلسطین در مبارزه با اسرائیل و تفاوتهایش با حماس در چیست؟»، Gidan yanar gizo na Euronews.
- ↑ «ما هی حرکة "الجهاد الإسلامی" التی تتهمها إسرائیل بقصف المستشفی المعمدانی فی غزة؟»Gidan yanar gizo na Faransa 24.
- ↑ «درباره جهاد اسلامی فلسطین و گردانهای قدس چه میدانیم؟»، وGidan yanar gizo na yanar gizo na labarai na Euronews.
- ↑ «حرکة الجهاد الإسلامی», Gidan yanar gizon TRT na Larabci.
- ↑ ابو طه، «تأثیر امام خمینی و انقلاب اسلامی در اندیشه و عملکرد جنبش جهاد اسلامی فلسطین»، Portal Imam Khumaini.
- ↑ Arabsorkhi, «جنبش جهاد اسلامی فلسطین از آغاز تا امروز»،Yanar Gizo na Ƙungiyar Ƙungiyoyin Kare Falasdinawa.
- ↑ Abu Taha «تأثیر امام خمینی و انقلاب اسلامی در اندیشه و عملکرد جنبش جهاد اسلامی فلسطین»، Portal Imam Khumaini.
- ↑ Abu Taha«تأثیر امام خمینی و انقلاب اسلامی در اندیشه و عملکرد جنبش جهاد اسلامی فلسطین»، Portal Imam Khumaini.
- ↑ Abu Taha «تأثیر امام خمینی و انقلاب اسلامی در اندیشه و عملکرد جنبش جهاد اسلامی فلسطین»، Portal Imam Khumaini.
- ↑ «فی حوار مع الجزیرة نت خالد البطش یوضح مکاسب الجهاد من الحرب ودور حماس والعلاقة مع إیران»Gidan yanar gizon Al Jazeera News Network.
- ↑ «فی حوار مع الجزیرة نت خالد البطش یوضح مکاسب الجهاد من الحرب ودور حماس والعلاقة مع إیران»،Gidan yanar gizon Al Jazeera News Network.
- ↑ «تاریخ حرکة الجهاد الإسلامی فی فلسطین موضوعًا لمحاضرة وحدة الدراسات الاستراتیجیة», Yanar Gizo na Cibiyar Bincike da Nazarin Siyasa ta Larabawa.
- ↑ «حدث الساعة.. معلومات تهمک معرفتها عن الجهاد الإسلامی التی أنجبت أسری عملیة جلبوع»،Gidan yanar gizo na Aljazeera News Network.
- ↑ «حدث الساعة.. معلومات تهمک معرفتها عن الجهاد الإسلامی التی أنجبت أسری عملیة جلبوع»Gidan yanar gizon Al Jazeera News Network.
Nassoshi
- «إلی جانب کتائب القسام ما هی أبرز الحرکات المسلحة فی غزة»،Gidan Yanar Gizo na BBC News, kwanan watan shiga: Oktoba 16, 1402, kwanan wata ziyara: Nuwamba 1, 1402.
- Abu Taha, Anwar «تأثیر امام خمینی و انقلاب اسلامی در اندیشه و عملکرد جنبش جهاد اسلامی فلسطین», Portal Imam Khumaini, Ranar Shiga: Yuni 20, 2017, Ranar Ziyara: Nuwamba 1, 2003.
- «تاریخ حرکة الجهاد الإسلامی فی فلسطین موضوعًا لمحاضرة وحدة الدراسات الاستراتیجیة»،Yanar Gizo na Larabawa Cibiyar Bincike da Nazarin Siyasa, kwanan watan shigarwa: Satumba 19, 1401, kwanan wata ziyara: Nuwamba 1, 1402.
- «حدث الساعة.. معلومات تهمک معرفتها عن الجهاد الإسلامی التی أنجبت أسری عملیة جلبوع», Gidan Yanar Gizon Labarai na Al Jazeera, kwanan shiga: Satumba 17, 1401, kwanan wata ziyara: Nuwamba 9, 1402.
- «حرکة الجهاد الإسلامی»،Gidan yanar gizon TRT Larabci, kwanan watan shigarwa: Oktoba 10, 1402, kwanan wata ziyara: Nuwamba 1, 1402.
- «حرکة الجهاد الإسلامی»،Gidan yanar gizon Al Jazeera News Network, ranar shigarwa: Fabrairu 13, 2013, kwanan wata ziyara: Nuwamba 1, 2013.
- Al-sharif Mahir «حرکة الجهاد الإسلامی فی فلسطین», Gidan yanar gizon Cibiyar Nazarin Falasdinu, kwanan watan shigarwa: Nuwamba 19, 2019, kwanan wata ziyara: Nuwamba 13, 2023.
- «درباره جهاد اسلامی فلسطین و گردانهای قدس چه میدانیم؟», Gidan yanar gizon Euro News Network, ranar shigarwa: Agusta 15, 1401, kwanan wata ziyara: Nuwamba 1, 1402.
- «رویکرد جهاد اسلامی فلسطین در مبارزه با اسرائیل و تفاوتهایش با حماس در چیست؟»،Gidan yanar gizon Euronews, kwanan watan shigarwa: Oktoba 17, 1402, kwanan wata ziyara: Nuwamba 14, 1402.
Hamid, Arabsorkhi «جنبش جهاد اسلامی فلسطین از آغاز تا امروز»، Yanar Gizo na Society for Defence of Palestine People, ranar shigarwa: 25 May 1401, kwanan wata ziyara: 10 Nuwamba 1403.
- «فی حوار مع الجزیرة نت خالد البطش یوضح مکاسب الجهاد من الحرب ودور حماس والعلاقة مع إیران»،Gidan yanar gizon Al Jazeera News Network, ranar shigarwa: Agusta 12, 1401, kwanan wata ziyara: Nuwamba 9, 1402.
- «ما هی حرکة "الجهاد الإسلامی" التی تتهمها إسرائیل بقصف المستشفی المعمدانی فی غزة؟»France24 website.
- «ما هی حرکة الجهاد الإسلامی وما علاقتها بحماس؟», Shafin Al-Hurrah, kwanan watan shiga: 17 Oktoba 1402, ranar ziyarta: 10 Nuwamba 1402.
- «نبذة عن حرکة الجهاد الإسلامی فی فلسطین», Al Jazeera News Network Shafin yanar gizo, kwanan watan shigarwa: Yuli 15, 2005, kwanan wata ziyara: Nuwamba 2, 2003.
- «نشأت بمصر، ولعبت دوراً کبیراً بالانتفاضة.. قصة حرکة الجهاد وسر استهداف إسرائیل لها بحربها الأخیرة»،Shafin yanar gizo na Arab Post, kwanan watan shigarwa: Agusta 17, 1401, kwanan wata ziyara: Nuwamba 9, 1402.











