Hadis Wilaya

Daga wikishia
Haramin Imam Ali (Ali)

Hadis Wilaya (arabic: حديث الولاية) wani hadisi ne da aka nakalto shi daga Annabi (S.A.W) wanda ya kasancewa daya daga dalilan da `Yan Shi’a suke jingina da su kan tabbatar da Imamanci Ali Bn Abi Talib (A.S) wannan hadisi ya zo da lafuzza daban-daban daga litattafan Shi’a da Ahlus-sunna, misali:

هوَ وَلِیُّ کُلِّ مُؤْمِنٍ بَعْدی

Shi ne shugaban dukkanin Mumini a bayana. Yan shi’a sun fassara kalmar waliyu da ta zo cikin wannan hadisi da ma’anar Imami jagora, da tsanantuwa da imamancin ne suke tabbatar da wilaya ta Imam Ali (A.S) sun tafi kan cewa Kalmar waliyu tana da wannan ma’ana hatta cikin Kamus din lugga, a wasu wurare daga bangare Shaikaini (Dattawa guda biyu) da kuma Sahabbai da Tabi’ai da wasu ba’arin Malaman Ahlus-sunna suma duka sun amfani da shi da wannan ma’anar, amma Ahlus-sunna sun yi da’awa kan cewa wai wannan kalma ta waliyu tana nufin masoyi kuma ba ta da wata alaka da mas’alar Imamanci da wilayar Imam Ali (A.S).

Matani

Jafar Bn Sulaiman ya karbo daga Imran Bn Hassin cewa Manzon Allah (S.A.W) ya aika wasu gungun mutane yaki tareda sanya Ali Bn Abi Talib a matsayin kwamandan su, sun samu Ganima a cikin wannan yaki da suka je, sai ya zama basu gamsu da yanda Ali Bn Abi Talib (A.S) Ya rarraba ganimar ba, mutane hudu daga cikin su suka yi yanke shawara cewa za su gaya Annabi (S.A.W) abinda ya faru, lokacin da suka isa wurin Annabi (S.A.W) sai kowannensu yayi bayanin abinda ya faru: ya Manzon Allah sun kasancewa haka Ali ya aikata? Sai fuskar Manzon Allah (S.A.W) ta canja saboda fushi ya ce musu me kuke so daga Ali? Me kuke nufi da Ali ne? hakika Ali daga ni yake ni ma daga gare shi nake kuma Ali bayana shi ne Majibancin dukkanin Mumini. [1] Mabanbantan Nakali Hakika an nakalto hadisin wilaya daga litattafan shi’a da sunna da mabanbanta lafuzza, daga cikin su:

«علی ولیّ کل مؤمن بعدی»

Ali shi ne Majibancin dukkanin Mumini a bayana. [2]

«هو ولی کل مؤمن بعدی»

Shi ne Majibancin dukkanin Mumini a bayana. [3]

«انت ولی کل مؤمن بعدی»

Matsayinka daga gareni kamar matsayin Haruna daga Musa yake. [4]

أنت ولی کل مؤمن بعدی و مؤمنه

Kai ne Majibancin dukkanin Mumini a bayana. [5]

«انت ولیی فی کل مؤمن بعدی»

Kai ne Majibancin dukkanin Mumini a bayana. [6]

«فانه ولیکم بعدی»

Tabbas shi ne Majibancinku a bayana. [7]

ان علیا ولیکم بعدی

Tabbas Aliyu shi ne Majibancinku a bayana. [8]

هذا ولیکم بعدی

Wannan shi ne Majibancinku a bayana. [9]

«انک ولی المؤمنین من بعدی»

Tabbas kai ne Majibancin Muminai a bayana. [10]

«انت ولیی فی کل مؤمن بعدی»

Kai ne Majibancin Muminai a bayana. [11]

و انت خلیفتی فی کل مؤمن من بعدی»

Kuma kai ne Halifana a kan kowanne Mumini a bayana. [12]

«و فهو اولی الناس بکم بعدی.

Shi ne Mafi cancantar mutane gareku a bayana. [13]

Abin da ya Kunsa

Yan shi’a sun tafi kan cewa wannan hadisi na Wilaya ya kunshi sakon Imamanci da wilayar Aliyu Bn Abi Talib (A.S) [14] sun fassara Kalmar waliyu da ma’anar shugabanci da jagoranci [15] amma Ahlus-sunna sun tafi kan cewa kwata-kwata wannan hadisi baya shiryarwa zuwa ga halifanci da shugabancin Aliyu Bn Abi Talib (A.S) suna masu da’awar cewa Kalmar waliyu a cikin Kamus din Lugga tana bada ma’anar masoyi da mataimaki [16] yan shi’a a yunkurin su na tabbatar da da’awarsu suna fadin: a Kamus din Lugga Kalmar waliyu tana bada ma’anonin Majibanci, Halifa,, Ma’abocin zabi da kuma Imami, a farko-farko bayyana sakon muslunci da bayansa anyi amfani da wannan kalma da ma’anar Halifa da shugaba. Sun kafa hujja da yanda Halifa na farko [17] da na biyu [18] da Sahabbai [19] da Tabi’ai [20] da wasu ba’arin Malaman Ahlus-sunna [21] duka suka yi da wannan kalma kan ma’anar shugaba da Halifa.

inganci

Abdul-Kadir Bagdadi da Ibn Hajar Askalani sun fadi cewa Tirmizi ya nakalto hadisin Wilaya da karfaffan isnadi daga Imran Bn Hasin. [22] haka ma Muttaki Hindi ya tafi kan ingancin wannan hadisi. [23] Hakim Naishaburi ya shima ya tafi kan ingancin isnadin hadisin amma Muslim da Bukari ba su kawo shi ba cikin Sahihaini. [24] hakama Shamsudini Zahabi da Nasirul Albani sun bayyana ingancin wannan hadisi. [25]

Masadir

Hadisin wilaya ya zo cikin litattafai misalign Sahihu Tirmizi, Musnad Ahmad, [26] Jami’ul Ahadis Suyudi [27] Kanzul Umma; [28] Musnad Abi Dawud [29] Fada’ilul Sahaba, [30] Al’ahadul Masani [31] Sunanu Nasa’i [32] Musnad Abu Ya’ala [33] Sahihu Bn Hibban [34] Almujamu Kabir Dabarani [35] Tarikul Madina Damashak [36] Albidaya Wannihaya [37] Al’isabatu [38] Aljauhar fi Nasabi Imam Ali wa Alihi [39] Kazanatul Adab wa Lubbi lisanul Albabi [40] Alghadir [41] Al’isti’ab [42] Kashaful Gummati. Erbali, Kashf al-Ghumma, 1405 AH, shafi na 177.

Bincike kan isnadin hadisin

Malam Mubarakfuri ya yi da’awa kan cewa Kalmar (ba’adi) a wasu kofin hadisin babu ita sam, ya tuhumi Marawaitan Shi’a da kara Kalmar cikin hadisin, domin tabbatar da wannan tuhuma da ya yi ya jingina da littafin Musnad Ahmad domin ya nakalto hadisin da isnadi masu yawa kuma cikin dukkaninsu babu kalma (ba’adi) [43] na’am sai dai kuma a Ahmad Bn Hanbal cikin Musnad din [44] da kuma Fada’ilul Sahaba ya kawo hadisin tareda Karin Kalmar (ba’adi). [45] Mubarakfuri Abu Ya’ala Muhammad Bn Abdur-Rahman wandya rayu tsakanin karni 1283-1353 ya yi da’awar Jafar Bn Sulaiman da Ibn Ajlaha Alkindi su kadai ne suka rawaito wannan hadisi, sakamakon shi’ancinsu ba a karbar riwayarsu ko kuma shi yana hukunta yan shi’a da matsayin ma’abota bidi’a kuma yana fadin yan bidi’ar da suke nakalto hadisan da suke karfafar Mazhabarsu ba a karbarta, [46] sai dai cewa kuma Albani yana cewa babban ma’aunin karbar riwaya a gurin Ahlus-sunna shi ne fadar gaskiya da kuma dandakewar Marawaici amma Mazhabar Marawaici bata da tasiri cikin karbar riwaya daga gareshi ko akasin haka, da wannan dalili ne Bukhari da Muslim a Sahihaini suka nakalto riwaya daga mutanen da suka saba da Mazhabar Ahlus-sunna misalin Kawarijawa da yan Shi’a. [47] Albani Muhammad Nasirudini wanda ya rayu tsakanin 1914-1999 m yana cewa an nakalto wannan hadisi cikin litattafan Ahlus-sunna da isnadin da babu dan shi’a ko guda daya cikin su, [48] Assayid Ali Milani ya ce: wannan hadisi ya zo ta hanyar Sahabbai 12 daga cikin su akwai Imam Ali (A.S) Imam Hassan (A.S) [49] Abu Zar, Abu Sa’id Kudri da Barra’u Bn Azib. [50] Galibin nakalin yana tukewa zuwa ga Imran Bn Hasin da Ibn Abbas da Buraidatu Bn Hasib. [51] Jafar Bn Sulaiman daga marawaitan Sahihu Muslim [52] Shamsudini yana kiransa da Imam [53]kuma ya nakalto daga Yahaya Bn Ma’in da ya bayyana shi a matsayin Sika 55. Albani ya bayyana cewa Jafar Bn Sulaiman yana daga cikin Marawaitan da ake dogara da su kuma mutum ne mai karfin riwaya dandakewa ya kasance mabiyin Ahlil-baiti kuma baya kira zuwa ga mazhabarsa, yana cewa babu sabani wurin manyan Malamanmu cewa idan Marawaici mai fadin gaskiya ya kasance daga yan bidi’a sai dai kuma baya kira zuwa ga Mazhabarsa babu matsala riko da hadisansa. [54] Wasu ba’ari daga Malaman Ahlus-sunna sun wassaka Ibn Ajlaha [55] sun kuma bayyana hadisinsa a matsayin hadisin da yake kan martabar Hasanu a inganci [56] Albani ya bayyana cewa hadisan Ibn Ajlaha shaida ce kan ingancin hadisan Jafar Bn Sulaiman [57] Mubarakfuri ya ce Ibn Taimiyya yayi da’awar cewa hadisin wilaya wata karya ce da aka danganta ta Annabi (S.A.W) [58] Albani ya bayyana mamakinsa kan yadda Ibn Taimiyya ya yi inkarin wannan hadisi [59]

Bayanin kula

  1. Ibn Shaiba, Al-Musannaf, 1409 AH, juzu'i na 8, shafi na 504, H. 58; Tayalasi, Musnad na Abi Dawud, Darul Marafa, shafi na 111.
  2. Ibn Shaiba, Al-Musannaf, 1409 AH, juzu'i na 8, shafi na 504, H. 58; Nasa’i, Al-Sunan al-Kubari, 1411 AH, juzu’i na 5, shafi na 132; Handi, Kanzal-Amal, 1409 AH, juzu'i na 13, shafi na 142.
  3. Tayalasi, Musnad na Abi Dawud, Dar al-Marifah, shafi na 111; Ibn Hanbal, Musnad, Cordoba Foundation, juzu'i na 4, shafi na 437; Abu Ya’ali Mosuli, Musnad Abi Ya’ali, 1404H, shafi na 293.
  4. Tayalasi, Musnad na Abi Dawud, Dar al-Marifah, shafi na 360; Nasa'i, Halayen Amirul Muminin (AS), 2003, shafi na 98.
  5. Tayalasi, Musnad na Abi Dawud, Dar al-Marifah, shafi na 360; Nasa'i, Halayen Amirul Muminin (AS), 2003, shafi na 98.
  6. Ibn Hanbal, Musnad, Cordoba Foundation, Mujalladi na 1, shafi na 330.
  7. Ibn Hajar, Al-esabah, 1415 Hijira, juzu'i na 6, shafi na 488.
  8. Ibn Kathir, Al-Bedayah da Al-Nehayah, 1407 AH, juzu'i na 7, shafi na 345; Hindi, Kanzal-Amal, 1409 AH, Juzu'i na 11, P. 612, H. 32963; Ibn Asaker, Tarihin Madina Damascus, 1415 Hijira, juzu'i na 42, shafi na 191.
  9. Nasa’i, Al-Sunan Al-Kubra, 1411 Hijira, juzu’i na 5, shafi na 133.
  10. Khatib al-Baghdadi, Tarikh Baghdad, Dar al-Kitab al-Alamiya, juzu'i na 4, shafi na 338
  11. Ibn Hanbal, Musnad, Cordoba Foundation, Mujalladi na 1, shafi na 330.
  12. Ibn Abi Asim, Sunna, 1413 AH, juzu’i na 2, shafi na 550; Tabarani, Al-Mu'jam al-Kabir, Darahiya al-Tratah al-Arabi, juzu'i na 12, shafi na 78.
  13. Tabarani, Al-Mu'jam Al-Kabir, 1404H, juzu'i na 22, shafi na 135.
  14. Milani, Tasheyed Almura'at, 1427 AH, juzu'i na 3, shafi na 164.
  15. Rahimi Esfahani, Velayat wa Rahbari, 1374, juzu'i na 3, shafi na 119-121.
  16. Eiji, al-Mawakif, Alam al-Katb, juzu'i na 1, shafi na 405
  17. Muslim, Sahih Muslim, Kitab al-Jihad wa al-Sir, Babin Al-Hakim: Juzu'i na 3, shafi na 1378, AH 1757; Balazri, Ansab al-Ashraf, 1959, juzu'i na 1, shafi na 590; Tabari, Tarikh al-Umam da al-Muluk, 1387 H., juzu'i na 3, shafi na 211; Ibn Kathir, Al-Bedaya wa Al-Nehaya, 1407H, juzu'i na 5, shafi na 248.
  18. Balazri, Ansab al-Ashraf, 1417 AH, juzu'i na 10, shafi.363; Tabari, Tarikh Al-Umam da Al-Muluk, 1387 H., juzu'i na 4, shafi na 65, 214; Ibn Kathir, Al-Bedaya wa Al-Nehaya, 1407 AH, juzu'i na 7, shafi na 79.
  19. Balazri, Ansab al-Ashraf, 1417 AH, juzu’i na 10, shafi.363; Tabari, Tarikh Al-Umam da Al-Muluk, 1387 H., juzu'i na 4, shafi na 65, 214; Ibn Kathir, Al-Bedaiya wa Al-Nehaya, 1407 AH, juzu'i na 7, shafi na 79.
  20. Masoudi, Moruj Al-Dahahab, 1409 AH, juzu'i na 3, shafi na 122.
  21. Ibn Sa’ad, Tabakat Al-Kubra, 1410H, juzu’i na 5, shafi na 245.
  22. Baghdadi, Khazane al-Adab, 1998, juzu'i na 6, shafi 69; Ibn Hajar, Al-Esabah, 1415 AH, juzu'i na 4, shafi na 468
  23. Hindi, Kanzal-Ummal, 1419 AH, Juzu'i na 11, P. 279, H. 32941.
  24. Hakim Nishaburi, Al-Mustadrak, juzu'i na 3, shafi na 134.
  25. Al-Mustadrak bi-Taaliq Dhahabi, Kitab Marafah al-Sahaba, kismi Zikri Islam Amir al-Mu'minin Ali, juzu'i na 3, shafi na 143, H4652; Albani, Al-Silsha al-Sahiha, juzu'i na 5, shafi na 263.
  26. Ibn Hanbal, Musnad, Cordoba Foundation, juzu'i na 4, shafi na 437.
  27. Siyuti, Jame al-Ahadith, Mujalladi na 16, shafi na 256, H. 7866 da Mujalladi na 27, shafi na 72.
  28. Hindi, Kanzal-Ummal, 1409 AH, juzu'i na 13, shafi na 142
  29. Tayalasi, Musnad Abi Dawud, Dar al-Marifah, shafi na 360.
  30. Ibn Hanbal, Fada'el Sahabba, 1403H, Juzu'i na 2, 605, 620, 649.
  31. Abu Bakr Shaybani, Al-Ahad wa Al-Mathani, 1411 AH, Juzu'i na 4, shafi na 279, AH 2298.
  32. Nasa’i, Al-Sunanul Al-Kubra, 1411H, juzu’i na 5, shafi na 132.
  33. Abu Yali Mosuli, Musnad Abi Yali, 1404H, shafi na 293.
  34. Ibn Hibban, Sahih Ibn Hibban, 1414H, juzu'i na 15, shafi na 373.
  35. Tabarani, Al-Mu'jam Al-Kabir, Darahiya al-Tratah al-Arabi, juzu'i na 12, shafi na 78.
  36. Ibn Asaker, Tarikh Madina, Damascus, juzu'i na 42, shafi na 100.
  37. Ibn Katheer, Al-Bedaiyah wa Al-Nehayah, 1407 Hijira, Juzu'i na 7, shafi na 345.
  38. Ibn Hajar, Al-Esabah, 1415 Hijira, juzu'i na 6, shafi na 488.
  39. Talmsani, Al-Jawhara, Ansari, Mujalladi na 1, shafi na 65.
  40. Baghdadi, Khazane al-Adab, 1998, juzu'i na 6, shafi na 68.
  41. Amini, Al-Ghadir, 1397 AH, Mujalladi na 1, shafi na 51.
  42. Ibn Abdulbar, Istiyab, 1412 Hijira, juzu'i na 3, shafi na 1091
  43. Mubarakfouri, Tohfa Al-Ahvadhi, 1410 AH, Juzu'i na 10, shafi na 146-147.
  44. Ibn Hanbal, Musnad, Cordoba Foundation, juzu'i na 1, shafi na 330, juzu'i na 4, shafi na 437.
  45. Ibn Hanbal, Fada'el Sahaba, 1403H, juzu'i na 2, shafi na 684, 1168 bayan hijira.
  46. Mobarakfouri, Tohfa Al-Ahodhi, 1410 AH, juzu'i na 10, shafi na 146-147.
  47. Albani, Al-Silsha Al-Sahiha, juzu'i na 5, shafi na 262.
  48. Albani, Al-Silsha Al-Sahiha, juzu'i na 5, shafi na 263.
  49. <a class="external text" href="http://www.al-milani.com/farsi/library/lib-pg.php?booid=2&mid=2&pgid=40">متن حدیث ولایت و تصحیح اسناد آن</a>
  50. Milani, Tasheyed Al-Mura'at, 1427 AH, juzu'i na 3, shafi na 238.
  51. <a class="external text" href="http://www.al-milani.com/farsi/library/lib-pg.php?booid=2&mid=2&pgid=40">متن حدیث ولایت و تصحیح اسناد آن</a>
  52. Dahhabi, “Siyar Al-Alam al-Nubala”, 1413 AH, juzu’i na 8, shafi na 200; Misali, Nishaburi, Sahih Muslim, Darul Fikr, juzu'i na 1, shafi na 77, 83, 153.
  53. Dhahabi, Tarikhul Islam, 1413 Hijira, juzu'i na 3, shafi na 631.
  54. Dhahabi Seer Al-Nablah 1413 AH, Juzu'i na 8, shafi na 198.
  55. Albani, Al-Silsha al-Sahiha, juzu'i na 5, shafi na 263.
  56. Manavi, Faiz al-Qadir, 1415 Hijira, juzu'i na 4, shafi na 471.
  57. Albani, Al-Silsha al-Sahiha, juzu'i na 5, shafi na 263.
  58. Mubarakfouri, Tohfa Al-Ahodhi, 1410 AH, juzu'i na 10, shafi na 147.
  59. Albani, Al-Silsha al-Sahiha, juzu'i na 5, shafi na 263.

Nassoshi

  • Abu Bakr Shibani, Ahmed bin Amr, Al-Ahad wa Al-Mathani, bincike: Bassem Faisal Ahmad Jubareh, Riyadh, Dar al-Darayeh, 1411 AH/1991 AD.
  • Abu Ya'ali Mosuli, Ahmad Bin Ali, Musnad Abi Ya'ali, Bincike: Hassan Salim Asad, Darul Ma'mun Gado.
  • Amini, Al-Ghadir, Dar al-Kitab al-Arabi, Beirut, 1977/1397.
  • Baghdadi, Abdul Qadir, Khazaneh al-Adab da Lab Labab lesan al-Arab, bincike: Mohammad Nabil Tariqi da Amil Badie Yaqoub, Beirut, Dar al-Kitab al-Alamiya, 1998. (Bita).
  • Balazri, Ahmed bin Yahya, Ansab al-Ashraf (Juzu'i na 1), Bincike: Muhammad Hamidullah, Masar, Dar al-Maarif, 1959.
  • Balazri, Ahmed bin Yahya, Jamal Man Ansab al-Ashraf, Bincike: Sohail Zakar da Riaz Zarkali, Beirut, Darul Fikr, 1417 AH/1996 Miladiyya.
  • Dahhabi, Muhammad bin Ahmad, Siyar Alamul Nubala, Bincike: Shoaib Arnawut da Muhammad Naeem Arqasousi, Beirut, Mu'assasa Al-Risalah, 1413 AH/1993 Miladiyya.
  • Dhahabi, Muhammad bin Ahmed, Tarikh Al-Islam wa Fayat al-Mashir da al-Alam, bincike: Omar Abd al-Salam Tadmari, Beirut, Dar al-Kitab al-Arabi, 1413 AH/1993 AD.
  • Eji, Abdur Rahman, Al-Maqqeef fi Alam al-Kalam, Beirut, Alam al-Katb, Bita.
  • Erbali, Ali bin Abi al-Fath, Kashf al-Ghummha fi Mafarah Al-Aima, Beirut, Darul-Azwa, 1405 AH/1985 miladiyya.
  • Hakim Neishaburi, Al-Mustadrak Ali Al-Sahiheen, bincike: karkashin jagorancin Abd al-Rahman Marashli, Bina, Bija, Bita.
  • Handi, Motaqi, Kanzul-Ummal, bincike: Sheikh Bekri Hayani, gyare-gyare: Sheikh Safwa Saqqa, Al-Risala Foundation, Beirut, 1989-1409 AH.
  • Ibn Abd al-Barr, Yusuf bin Abd al-Barr, Al-Istiyab fi Marafah al-Ashab, bincike: Ali Muhammad Bejawi, Dar al-Jeel, Beirut, 1412 AH/1992 AD.
  • Ibn Abi Asim Shibani, Amr Ibn Abi Asim, Al-Sunnah, Bincike: Mohammad Naser al-Din Albani, Beirut, Al Maktab al-Islami, 1413 AH/1993 Miladiyya.
  • Ibn Asaker, Ali Ibn Hasan, Tarihin Madina Damascus, Bincike: Mohibuddin Abi Saeed Omar Ibn Ghramah Omari, Beirut, Darul Fikr, 1995 AD/1415 AH.
  • Ibn Hajar Asqlani, Ahmad bin Ali, Al-Esabah fi Tamiyiz Sahabah, Research: Adel Ahmad Abdul Mojood da Ali Muhammad Moawad, Beirut, Dar al-Kitab al-Alamiya, 1415 AH/1995 AD.
  • Ibn Hanbal, Ahmad, Fada'el Sahaba, Bincike: Wasiullah Muhammad Abbas, Beirut, Mu’assasa Al-Risalah, 1403 AH/1983 Miladiyya.
  • Ibn Hanbal, Ahmad, Musnad, Egypt, Cordoba Foundation, Beta.
  • Ibn Hibban, Muhammad Bin Hibban, Sahih Ibn Hibban a matsayin Ibn Balban, Bincike: Shoaib Arnout, Beirut, Al-Risalah Foundation, 1414 AH/1993 Miladiyya.
  • Ibn Juzi, Abd al-Rahman bin Ali, al-Muntazam fi Tarikh al-Muluk wa al-Umam, bincike: Muhammad Abd al-Qader Atta da Mostafa Abd al-Qader Atta, Beirut, Dar al-Kitab al-Alamiya, 1412 AH/1992 AD.
  • Ibn Kathir, Ismail Ibn Umar, Al-Bedayah da Al-Nehayah, Beirut, Darul Fikr, 1407H/1986 Miladiyya.
  • Ibn Saad, Muhammad, Tabaqat Al-Kubra, bincike: Muhammad Abdulqadir Atta, Beirut, Darul Kutb al-Alamiya, 1410 AH/1990 AD.
  • Ibn Shaiba Koofi, Abdullah bin Muhammad, Al-Musannaf Fi Ahadith da Al-Anqir, bincike: Saeed Al-Laham, Beirut, Darul Fikr, 1409 AH/1989 Miladiyya.
  • Khatib al-Baghdadi, Ahmed bin Ali, TariKH Baghdad, Beirut, Dar al-Kutb al-Ulamiya, Bita.
  • Manawi, Abdul Raouf, Faiz al-Qadeer, Sharh Al-Jamae Al-Saghir, wanda: Ahmad Abd al-Salam, Beirut, Dar al-Kitab al-Islamiya, ya inganta, 1415 AH/1991 Miladiyya.
  • Masoudi, Ali bin Hossein, Muruji Al-Dahab da Maaden Al-Jawhar, bincike: Asad Dagher, Qum, Dar al-Hijra, 1409H.
  • Milani, Seyyed Ali, TasheEed Almura'at da Tafnid al-Makabarat, Qum, Al-Haqaqeeq al-Islamiya Center, 1427 AH/1385.
  • Moghadisi, Motaher bin Taher, Al-bada'u wa Al-Tarikh, Bursa'id, al-Thaqafi al-Diniya School, Bita.
  • Mubarakfouri, Muhammad Abdurrahman, Tuhufatu Ahwazi fi sharh Jami al-Tirmidhi, Beirut, Dar al-Kitab al-Alamiya, 1410 AH/1990 AD.
  • Nasa'i, Ahmed bin Shoaib, Al-Sunan Al-Kubra, bincike: Abdul Ghafar Suleiman Bandari da Seyyid Hassan Kasravi, Beirut, Darul Kutb al-Alamiya, 1411 Hijira/1991 Miladiyya.
  • Nasa'i, Ahmed bin Shoaib, Khasa'is Amir al-Mu'minin (AS), Qom, Bostan Kitab, 2003.
  • Nishaburi, Muslim bin Hajjaj, Sahih Muslim, Beirut, Darul Fikr, Bita.
  • Rahimi Esfahani, Gholam Hossein, Welayat wa Rahbari, Tafarsh, Askarieh Publications, 1374.
  • Tabarani, Suleiman bin Ahmad, Al-Mu'jam Al-Kabir (mujalladi 12), bincike: Hamdi bin Abdul Majid Salafi, Darahiya al-Tarath al-Arabi.
  • Tabari, Muhammad bin Jarir, Tarikh Al'umam wa Al-Muluk, bincike: Muhammad Abolfazl Ibrahim, Beirut, Darul-Trath, 1967 miladiyya/1387H.
  • Talmsani, Muhammad bin Abi Bakr, al-Jawhara fi Nasb al-Imam Ali da iyalansa, Kum, Ansariyan, Bita.
  • Tayalsi, Suleiman bin Dawood, Musnad Abi Daoud al-Tyalsi, Beirut, Dar al-Marafa, Bita.
  • البانی، محمدناصرالدین، السلسلة الصحیحة.
  • Shafin yanar gizo na Sayyid Ali Milani, Matane hadis wilayat da gyaran takardunsa, bita: 20 Khordad 1395.