Daƙiƙa:Suratul Baƙara
Fatiha Suratul Baƙara Ali Imran | |
| Lambar Sura | 2 |
|---|---|
| Juzu'i | -1da 2 da 3 |
| Jerantuwa Ta Sauka | 87 |
| Adadin Ayoyi | 286 |
| Adadin Kalmomi | 6156 |
| Adadin Haruffa | 26256 |
| Makkiya/Madaniyya | Madiniyya |
Suratul Baƙara ita ce sura mafi girma kuma ta biyu a cikin Alƙur'ani Mai Girma. Tana daga cikin surorin Madina, kuma tana cikin juzu'ai na farko, na biyu da na uku na Alƙur'ani. An sanya mata suna Baƙara ne saboda labarin saniyar Banu Isra'il da ya zo a ayoyi na 67 zuwa 73.
An bayyana cewa babban manufar Suratul Baƙara ita ce shiryar da mutane tare da sanar da cewa wajibi ne mutum ya yi imani da duk abin da Allah Ya saukar ta hannun Annabawansa, ba tare da nuna bambanci tsakanin Manzanni ba. Sannan surar ta ƙunshi bayanai kan ginshiƙan imani da kuma hukunce-hukuncen ibada, zamantakewa, siyasa da tattalin arziƙi.
Daga cikin manyan labaran da surar ta ƙunsa akwai labarin Annabi Adam da mala'iku, labarin Banu Isra'il, labarin Annabi Ibrahim da yadda Allah Ya nuna masa yadda ake raya matattu, da kuma labarin yaƙin Ɗalut da Jalut.
Haka kuma, Suratul Baƙara ta ƙunshi wasu fitattun ayoyi na Alƙur'ani, kamar Ayatul Kursiyu, Ayar "Amanar Rasulu" Ayar Alƙibla, da kuma ayar da ta fi tsawo a cikin Alƙur'ani, wato aya ta 282. A cikin wani hadisi daga Annabi Muhammad (S.A.W), an ruwaito cewa Suratul Baƙara ita ce sura mafi falala a cikin Alƙur'ani, kuma Ayatul Kursiyu ita ce aya mafi falala a cikinsa.
Gabatarwa
- Sanya Suna
Sunan Suratul Baƙara (Saniya) ya samo asali ne daga labarin saniyar Bani Isra'il (a cikin ayoyi 67 zuwa 73).[1] Fusɗaɗin (Tanti) Alƙur'ani, Sanamul Alƙur'an, Sayyidul Alƙur'an da Zahra wasu sunaye ne na Suratul Baƙara.[2] Suratul Baƙara da Suratul Ali Imran ana kiran su da suna Zahrawan[3] kuma a cikin wani hadisi daga Imam Ali (A.S), an kira su da Jamalul Alƙur'an.[4]
- Wuri da Matsayin Saukowa
Suratul Baƙara tana daga cikin surori Madaniyya, kuma ita ce sura ta 87 da aka saukar wa Annabi (S.A.W). Amma a tsarin da ake da shi na Mus'haf yanzu, ita ce sura ta biyu, kuma tana a juz'i na farko, na biyu da na uku na Alƙur'ani.[5]An yi imanin cewa ita ce sura ta farko da aka saukar a Madina bayan Suratul Muɗaffifin kuma kafin Suratu Ali ImranAn ɗauke ta a matsayin.[6]
- Adadin Ayoyi da Sauran Siffofi
Suratul Baƙara tana da ayoyi 286, kalmomi 6,156 da haruffa 26,256. Ita ce sura mafi girma a Alƙur'ani kuma tana ɗaukar kusan kashi 2.5 juzu'i na Alƙur'ani.[7] Suratul Baƙara ita ce sura ta farko daga cikin surori bakwai masu tsawo (Tiwal) kuma ta farko daga cikin surori 29 da aka fara da haruffan da aka yanke (Muƙaɗɗa'at),[8] kuma an fara ta da haruffan Muƙaɗɗa'at "Alif Lam Mim".[9] Kalma mafi girma "Fasayakfikahumullah" da kuma aya mafi tsayi a Alƙur'ani (Aya ta 282) suna cikin wannan sura. [10]
Abun Ciki
Allama Ɗabaɗaba'i ya bayyana cewa babban manufar Suratul Baƙara ita ce sanar da cewa wajibi ne mutum ya yi imani da duk abin da Allah Ya saukar ta hannun Annabawansa, ba tare da nuna bambanci tsakanin Manzanninsa ba. Haka kuma, ya bayyana cewa daga cikin muhimman batutuwan da surar ta ƙunsa akwai suka ga kafirai da munafukai, da kuma tsawatar wa Ahlul-Kitabi saboda bidi'o'in da suka ƙirƙira.[11]
Suratul Baƙara ta ƙunshi batutuwa masu yawa da suka shafi fannoni daban-daban. A cikin Suratul Baƙara an tattauna batutuwan da suka shafi ginshiƙan imani, da kuma hukunce-hukuncen ibada, zamantakewa, siyasa da tattalin arziki.[13] A cikin Tafsir Namuna, an taƙaita muhimman batutuwan surar kamar haka:
- Tauhidi da sanin Allah;
- Tashin ƙiyama da rayuwa bayan mutuwa
- Mu'ujizar Alƙur'ani
- Yahudawa da munafukai da matakan da suka ɗauka wajen adawa da Musulunci
- Tarihin Annabawa, musamman Annabi Ibrahim (A.S) da Annabi Musa (A.S)
- Hukunce-hukuncen sallah
- Hukunce-hukuncen azumi
- Jihadi a tafarkin Allah
- Hajji da canja alƙibla
- Hukunce-hukuncen aure da sakin aure
- Hukunce-hukuncen kasuwanci da bashi;
- Hukunce-hukuncen riba
- Ciyarwa saboda Allah (infaki).
- Ƙisasi
- Haramcin wasu nau'ukan nama.
- Haramcin caca.
- Haramcin giya
- Hukunce-hukuncen wasiyya.[14]
Labarai Da Riwayoyin Tarihi
A cikin Suratul Baƙara akwai labarai da bayanai na tarihi da yawa, ciki har da:
- Halittar Adam: Ayoyi 30-39.
- Bishiya da aka hana: Ayoyi 35-37.
- Ceton Bani Isra'il daga Fir'auna: Ayoyi 49-50.
- Bautar maraƙi ta Bani Isra'il: Ayoyi 51-54 da 92-93.
- Neman Bani Isra'il na ganin Allah: Aya ta 55.
- Mu'ujizar fitowar maɓuɓɓugan ruwa goma sha biyu: Aya ta 60.
- Neman abinci iri-iri da ɗimuwar Bani Isra'il: Aya ta 61.
- Alƙawarin Bani Isra'il: Ayoyi 63-64 da 83-85.
- Rashin biyayyar Bani Isra'il a ranar Asabar: Ayoyi 65-66.
- Sanuwar Bani Isra'il: Ayoyi 67-74.
- Labarin Harut da Marut: Aya ta 102.
- Gwajin Ibrahim da gina Ka'aba: Ayoyi 124-127.
- Canjin Alƙibla: Ayoyi 142-150.
- Ɗalut da Jalut: Ayoyi 246-251.
- Muhawarar Ibrahim da Namarudu: Aya ta 258.
- Tsuntsaye huɗu na Ibrahim: Aya ta 260.
- Labarin Uzairu: Aya ta 259.
Dalili da Sababin Saukar Wasu Ayoyi
An ruwaito sababi da dalilan saukar kusan ayoyi tamanin na Suratul Baƙara.[16] Daga cikin waɗannan akwai:
Isgilanci Da Munafukai Suka Yi Wa Musulmi
Ibn Abbas ya fassara aya ta 14 a kan Abdullahi Bin Ubayyu da sahabbansa munafukai; sun kasance a fili suna yabon Sahabban Annabi (S.A.W) amma a zuciya suna ƙin su kuma suna yi wa Musulmi izgili.[17]
Kiristoci Da Suka Kasance Abokan Salman , Waɗanda Aka Yi Musu Busharar Aljanna
Shaik Ɗusi game da aya ta 62 Suratul Baƙara
Shaik Ɗusi ya ruwaito daga Suddi cewa aya ta 62 ta Suratul Baƙara ta shafi Salmanul Farsi da abokansa Kirista, waɗanda suka musulunta ta hanyar Kiristanci kafin aiko Annabi. An yi musu alƙawarin cewa wani Annabi zai zo, kuma idan suka sadu da shi za su yi imani da shi.[18]
Labarin Saniyar Banu Isra'il
Ayoyi na 67 zuwa 73 na Suratul Baƙara sun ba da labarin Saniyar Banu Isra'il, tare da bayyana yadda suka kasance masu yawan neman hujjoji da uzurori wajen aiwatar da umarnin Allah.[19] A cikin Tafsir Namuna, an bayyana cewa an yi wani kisan kai a cikin Banu Isra'il, sai saɓani ya tashi tsakanin ƙabilunsu kan wanda ya aikata kisan. Domin a yanke hukunci, sai suka je wurin Annabi Musa (A.S). Da umarnin Allah ta bakin Annabi Musa (A.S), suka yanka wata saniya, sannan aka bugi gawar mamacin da wani ɓangare na jikinta. Da ikon Allah, mamacin ya farfaɗo ta hanyar mu'ujiza, ya kuma bayyana wanda ya kashe shi.[20]
Halaccin Wasu Hukunce-hukunce A Dararen Watan Ramadan
Ali Bin Ibrahim Ƙummi ya ruwaito daga Imam Jafar Sadiƙ (A.S) cewa a farkon Musulunci, kusantar iyali (jima'i) ya kasance haram ne tun daga farkon zuwa ƙarshen watan Ramadan. Haka kuma, idan mutum ya yi barci kafin lokacin buɗa baki, ba zai iya cin abinci ba har sai lokacin buɗa bakin dare na gaba.[21]
A cewar wannan ruwaya, a lokacin Yaƙin Ahzab (Khandaƙ), wani dattijo daga cikin sahabban Annabi ya yi barci a lokacin buɗa baki, sannan washegari ya suma yayin da yake haƙa ramin yaƙi. Haka kuma wasu Musulmi suna yin kusantar iyali da matansu a dararen Ramadan. Waɗannan abubuwan ne suka zama dalilin saukar aya ta 187 a cikin Suratul Baƙara, wadda ta sauya hukuncin da ya gabata.[22]
Haramcin Auren Mushrikai
Aya ta 221 Suratul Baƙara ta sauka ne game da Marsad Bin Abi Marsad. Ya tafi Makka bisa umurnin Annabi (S.A.W) don ya fitar da wasu gungun Musulmai daga Makka. A can, wata mace daga mushirikai ta yi masa tayin neman aure, amma Marsad ya sanya hakan a kan izinin Annabi (S.A.W). Bayan ya koma Madina kuma ya faɗa wa Annabi (S.A.W) abin da ya faru, sai aka saukar da aya ta hana Musulmai yin aure da mushirikai.[23]
Wasu Mashahuran Ayoyi
Ayar Halifancin Mutum
Kuma lokacin da Ubangijinka ya ce wa mala'iku: Lalle Ni Mai sanya halifa ne a cikin ƙasa ...
Wannan aya ita ce sanarwar maye gurbin (Khilafah) na ɗan adam a duniya daga Allah.[24] Mala'iku sun yi tambaya game da yiwuwar ɓarna da zubar da jini na ƴan Adam, kuma Allah ya amsa cewa iliminsa ya ƙunshi dukkan abubuwa.
Ayar Sihiri
Sun bi abin da shaiɗanu suke karantawa a kan mulkin Sulaiman... Wannan aya tana nuni da yaɗuwar sihiri a tsakanin wasu daga cikin Yahudawa, kuma tana ba da amsa ga zargin cewa Annabi Sulaiman (A.S) da Haruta da Maruta sun kasance masu sihiri.[25]
Ayar Nasakh (Shafewa)
Abin da Muka shafe daga aya ko kuma Muka mantar da shi, Mukan zo da mafi alheri daga gare ta ko kuma misalinsa...
Wannan aya tana nuna maye gurbin wasu hukunce-hukunce da ayoyi bisa ga hikimar Allah[26] kuma tana nuna ikonsa wajen ƙayyade dokoki da gyara al'amuran bayinsa.[27] Dalilin saukarta shi ne izgilin mushirikai da Yahudawa ga Annabi game da canza wasu hukunce-hukunce da Alƙibla.[28]
Ayar Ibtila Ibrahim
Kuma lokacin da Ubangijinsa ya jarrabi Ibrahim da wasu kalmomi, sai ya cika su...
Wannan aya tana magana ne game da jarrabawar Annabi Ibrahim (A.S). Malaman Shi'a sun yi imani cewa aya ta jarrabawa tana nuni ne ga ma'asumcin Imam, kuma abin da ake nufi da kalmar "Imam" a cikinta wani matsayi ne dabam da Annabta da manzanci.[29] saɓanin haka, malaman Ahlus-Sunnah sun gabatar da wasu misalai kamar Annabta ko Risala don ma'anar kalmar "Imam".[30]
Ayar Istirja'i
Waɗanda idan wata masifa ta same su, sai su ce: Mu na Allah ne, kuma zuwa gare Shi za mu koma.
Wannan aya tana bayyana masu haƙuri da cewa su ne waɗanda idan wata masifa ta same su, suke da imani cewa su na Allah ne kuma gare Shi za su koma.[31]
Saboda wannan aya, Musulmi suna karanta wannan ayar a lokacin da wata masifa ta same su.[32] A cikin ruwayoyi kuma, an ambaci cewa karanta wannan aya a lokacin masifa yana daga cikin abubuwan da ke sa mutum ya kasance daga cikin mazauna Aljanna.[33]
Ayar Amsa Addu'a
Idan bayina suka tambaye ka game da Ni, to, lalle Ni Ina kusa...
Wannan aya tana bayyana kulawar Allah wajen amsa addu'o'in bayinsa da kuma kusancinsa gare su.[34] Allama Ɗabaɗaba'iya bayyana cewa wannan aya tana ƙunshe da sirrika masu yawa na balaga da ma'anoni na ruhaniya.[35]
Ayar Shira (207)
Kuma daga cikin mutane akwai wanda yake sayar da ransa don neman yardar Allah... Wannan aya ta sauka ne game da sadaukarwar Imam Ali (A.S) a Lailati al-Mabit, lokacin da ya kwanta a gadon Annabi (S.A.W) don kare rayuwarsa.[36] Wannan aya ta yaba wa waɗanda suke shirye su sadaukar da rayukansu domin samun yardar Allah.[37]

Ayatul Kursiyu
Allah, babu abin bautawa da gaskiya face Shi, Rayayye, Mai tsayawa da kansa kuma Mai tsayar da komai... Ayatul Kursiyu tana da babban matsayi da shahara a tsakanin Musulmi, kuma sun kasance suna ba ta kulawa ta musamman. Annabi Muhammad (S.A.W) ya kira wannan aya da aya mafi girma a cikin Alƙur'ani.[38]
Allama Ɗabaɗaba'i ya bayyana cewa dalilin girman Ayatul Kursiyu shi ne kasancewarta tana ƙunshe da muhimman bayanai masu zurfi game da Tauhidi tsantsa da kuma ikon Allah na tsayawa da kansa da kuma tsayar da dukkan halittu. Ya kuma yi imanin cewa, ban da sunayen zatin Allah, sauran kyawawan sunayenSa suna komawa ne ga wannan sifar ta Allah ta kasancewarSa Mai tsayar da komai.[39]
Ayar Rashin Tilashi A Addini
Babu tilastawa a cikin addini...
An yi imani da cewa aya ta 256 Suratul Baƙara tana nuna cewa babu tilastawa wajen karɓar addini, musamman Musulunci, ga kafirai, mushirikai da sauransu.[40] Kuma dalilin saukarta shi ne amsa buƙatar wani Sahabi na mayar da ɗansa daga Kiristanci zuwa Musulunci.[41]

Ayar Infaƙi
Waɗanda suke ciyar da dukiyoyinsu da dare da rana...
Wannan aya ta sauka ne game da sadaka da kuma yadda ake yin ta.[42] Malaman tafsiri sun yi imanin cewa dalilin saukar aya shi ne game da Imam Ali (A.S). Ya ba da zinare guda huɗu: ɗaya da dare, ɗaya da rana, ɗaya a bayyane, da kuma ɗaya a ɓoye.[43] Wannan aya ta shafi duk wanda ya yi sadaka ta irin wannan hanya.[44]
Ayar Amanar Rasul
Manzon Allah ya yi imani da abin da aka saukar zuwa gare shi daga Ubangijinsa, da muminai...
Ayoyin Amana Rasul, waɗanda aka fi sani da ayoyin Amana Rasul, su ne ayoyi 285 da 286 na Suratul Baƙara. Imani ga Allah, gaskata Annabawa, imani da tashin ƙiyama, kiyaye haƙƙin bautar Allah, imani na zuciya da biyayya ta aiki na muminai, gafarar Allah, rashin ɗora wa mutum abin da ya fi ƙarfinsa, da kuma sauƙin addinin Musulunci, daga cikin batutuwan da aka ambata a cikin waɗannan ayoyi biyu.[45]
Ayoyin Hukunce-hukunce
Malaman fiƙihu sun yi amfani da wasu ayoyi daga Suratul Baƙara wajen fitar da hukunce-hukuncen shari'a.[46] A cikin teburin da ke ƙasa, an ambaci wasu daga cikin ayoyin hukunce-hukuncen (Ayat al-Ahkam) na Suratul Baƙara:
| Aya | Rubutun aya | Babi | Maudu'i |
|---|---|---|---|
| 21 | Ya ku mutane! Ku bauta wa Ubangijinku, Wanda Ya halicce ku da waɗanda suka gabace ku | Ibada | Wajabcin ibada kan dukkanin mutane |
| 27 | Waɗanda suke warware alƙawarin Allah bayan sun ƙulla shi | Bakance (Alwashi), alƙawarin da Rantsuwa | Haramcin karya alƙawari da sakamakonsa |
| 29 | Shi ne Wanda Ya halitta muku duk abin da yake cikin ƙasa | Abinci da abin sha | Asalin halaccin da kuma halalcin dukkan abubuwa waɗanda ba su da ɓarna |
| 43 | Ku tsayar da sallah, ku bayar da zakka, kuma ku yi ruku'i tare da masu ruku'i | Sallah da zakka | Wajabcin tsayar da sallah da ba da zakka |
| 114 | Kuma wane ne ya fi zalunci fiye da wanda ya hana a ambaci sunan Allah a cikin masallatanSa... | Sallah | Haramcin hana ko ƙirƙirar shamaki ga gudanar da sallah a cikin masallatai |
| 124 | Ka tuna lokacin da Ubangijinsa Ya jarrabi Annabi Ibrahim da wasu umarni, sai ya cika su gaba ɗaya. Sai Allah Ya ce: "Lalle Ni Zan sanya ka shugaba (Imami) ga mutane... | Sallah | Adalcin limamin jam'i, Imamanci |
| 125 | Ka tuna lokacin da Muka sanya Gidan (Ka'aba) ya zama wurin komawa ga mutane da kuma mafaka mai aminci. Kuma ku riƙe.. | Hajji | Halatta (shari'antar) aikin Hajji, sallar ɗawafi da sauransu |
| 140 | Kuma wane ne ya fi zalunci fiye da wanda ya ɓoye wata shaida da yake da ita daga Allah... | Shaida | Haramcin ɓoye shaida |
| 144 | Haƙiƙa Mun ga juyawar fuskarka zuwa sama (kana jiran umarnin Allah game da alƙibla), to lallai za Mu juyar da kai zuwa wata alƙibla da za ka yarda da ita... | Sallah | Alƙibla da hukunce-hukuncenta |
| 158 | Lalle ne Safa da Marwa suna daga cikin alamomin (ibadar) Allah... | Hajji | Sa'ayi tsakani Safa da Marwa |
| 168 | Ya ku mutane! Ku ci daga abin da yake cikin ƙasa, wanda yake halal kuma mai kyau... | Abinci da abin sha | Asalin halaccin dukkan abubuwan da ba su da ɓarna |
| 170 | ko da iyayensu sun kasance ba sa fahimtar wani abu kuma ba sa samun shiriya? | Taƙlidi (Makauniyar biyayya) | Rashin halaccin taƙlidi daga wanda ba mujtahidi ba, ba ya kuma daga ƙwararru |
| 173 | Abin da Ya haramta muku kawai shi ne gawa, jini, da naman alade... | Farauta da yanka dabba bisa ƙa'idar shari'a | Haramcin gawa, jini, naman alade, dabbar da ba a yi mata yankan shari'a ba, da sauransu. |
| 177 | Waɗanda suke cika alƙawarinsu idan sun yi alƙawari | Bakance, Alƙawari da Rrantsuwa | Wajabcin cika alƙawari |
| 178-179 | An wajabta muku yin ƙisasi a kan waɗanda aka kashe: ƴantaccen mutum da ƴantaccen mutum, bawa da bawa, mace da mace | Haddodi da diyyoyi | Shari'antar ƙisasi da nau'o'insa. |
| 180 | An wajabta muku idan mutuwa ta kusanci ɗayanku, idan ya bar dukiya mai yawa, yin wasiyya... | Wasiyya | Wajabcin rubuta wasiyya lokacin mutuwa ga makusantan dangi |
| 182 | Duk wanda ya ji tsoron wani mai wasiyya zai yi karkata ko zunubi, sai ya sasanta tsakaninsu, to babu laifi a kansa... | Wasiyya | Kyakkyawan aiki ne a samar da sulhu tsakanin masu husuma |
| 183-185 | Ya ku waɗanda suka yi imani! An wajabta muku azumi... | Azumi | Shari'antar azumi ga Musulmi da kuma bayyana wasu daga cikin hukunce-hukuncensa |
| 187 | An halatta muku a daren azumi yin kusanci da matanku... | Azumi | Hukunce-hukuncen azumi |
| 188 | Kuma kada ku ci dukiyoyinku a tsakaninku ta hanyar da ba ta dace ba... | Kasuwanci | Haramcin cin dukiya ta hanyar ƙarya |
| 190-191 | Ku yi yaƙi a tafarkin Allah da waɗanda suke yaƙar ku, amma kada ku wuce iyaka... | Jihadi | Shari'antar jihadi da kiyaye adalci a cikin jihadi |
| 194 | Duk wanda ya yi zalunci a kanku, to ku rama masa da irin abin da ya yi muku na zalunci... | Haddodi da diyyoyi | Kiyaye daidaito (misali) a cikin ƙisasi |
| 196 | Kuma ku cika aikin Hajji da Umara saboda Allah... | Hajji | Bayyana wasu daga cikin ayyukan Hajji da Umara |
| 198 | Idan kun sauka daga Arafat, to ku ambaci Allah a wurin Mash'aril Haram... | Hajji | Tsayuwa (wuƙufi) a ƙasar Mash'aril Haram da Arafat |
| 203 | Ku ambaci Allah a cikin wasu ƴan kwanaki ƙididdigaggu... | Hajji | Ayyukan ranakun Tashriƙ |
| 217 | Suna tambayarka game da yin yaƙi a cikin wata mai alfarma. Ka ce: Yin yaƙi a cikinsa babban laifi ne... | Jihadi | Hukunce-hukunce watanni masu alfarma |
| 221 | Kuma kada ku auri matan mushirikai har sai sun yi imani... | Nikahu | Haramcin aure tare da mushrikai |
| 222 | Suna tambayarka game da haila. Ka ce: Ita wani abu ne mai cutarwa, saboda haka ku nisanci mata a lokacin haila... | Tsarkaka daga najasa | Hukunce-hukuncen haila |
| 223 | Matanku gonaki ne a gare ku, saboda haka ku je wa gonakinku yadda kuka so... | Nikahu | Dangantakar aure tsakanin ma'aurata |
| 224-225 | Kuma kada ku sanya Allah ya zama abin dogaro da rantsuwoyinku | Bakance, Alƙawi da Rantsuwa | Hana rantsuwa marar amfani (rantsuwar banza) |
| 226-227 | Ga waɗanda suke yin rantsuwar ƙauracewa matansu, akwai jira na watanni huɗu... | Sakin aure | Ila'i da hukunce-hukuncensa. |
| 228 | Matan da aka sake su su jira da kansu tsawon tsarki uku | Sakin aure | Iddar saki |
| 229-232 | Saki sau biyu ne; sannan ko dai a riƙe su (mata) cikin kyakkyawar mu'amala, ko kuma a sallame su cikin kyautatawa... | Sakin aure | Hukunce-hukuncen saki |
| 233 | Uwaye su shayar da ‘ya'yansu nono tsawon shekaru biyu cikakku... | Nikahu | Hukunce-hukuncen shayarwa (nonon uwa), da wajabcin shayar da yaro |
| 234 | Waɗanda ake kashewa daga cikinku (ta hanyar mutuwa) kuma suka bar mataye, to waɗannan matan za su jira da kansu tsawon watanni huɗu da kwanaki goma... | Nikahu | Iddar Wafati |
| 235 | Waɗanda suke mutuwa daga cikinku kuma suka bar mataye, to matan za su jira (iddah) na tsawon watanni huɗu da kwanaki goma... | Nikahu | Baiko |
| 236-237 | Babu laifi gare ku idan kun saki mata alhali ba ku taɓa su ba | Sakin aure | Hukunce-hukuncen saki (ɗaura aure) ba tare da an kulla hulɗar aure (jima'i) tsakanin ma'aurata ba |
| 238 | Ku kiyaye salloli da kuma sallar tsakiya... | Sallah | Kiyaye lokutan sallah |
| 240 | Wa waɗanda suke mutuwa daga cikinku kuma suka bar mataye, to su yi wasiyya ga matansu... | Wasiyya | Wasiyya ga mata aure |
| 245 | Wane ne zai bai wa Allah rance mai kyau, sai Ya ninka masa shi ninki mai yawa?... | Bashi | Muhimmancin da kyawun aikin bayar da bashi, musamman bashin alheri (ƙardul hasan) |
| 264 | Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku ɓata sadakokinku ta hanyar nuna alheri | Bashi | Rusa ladar bashi da sadaka |
| 270 | Duk abin da kuka ciyar na wani abu ko kuka yi wani alwashi | Bakance, Alƙawari da Rantsuwa | Wajabcim cika bakance |
| 275-276 | Waɗanda suke cin riba ba za su tashi ba sai kamar yadda wanda shaiɗan ya shafi yake tashi | Sayarwa da saye | Haramcin Riba |
| 278-280 | Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku ji tsoron Allah, kuma ku bar abin da ya rage na riba, idan har ku masu imani ne | Sayarwa da saye | Hukunce-hukuncen Riba |
| 282-283c | Ya ku waɗanda suka yi imani! Idan kun yi mu'amalar bashi zuwa wani ƙayyadadden lokaci, to ku rubuta shi... | Bashi | Rubuta yarjejeniyar bashi da kuma sanya shaidu a kanta, da kuma ladubban bashi. |
| 283 | Idan wasu daga cikinku suka yarda da amincin wasu, to wanda aka ba amana ya mayar da amanar da aka ba shi... | Amana | Mayar da amana ga ahalinta |
Falalolin Surori Da Darajoji Na Musamman
A bisa wata ruwaya daga Majma' al-Bayan, an ruwaito cewa Annabi (S.A.W) ya bayyana Suratul Baƙara a matsayin surar Alƙur'ani mafi falala, sannan Ayatul Kursiyu a matsayin aya mafi falala a cikin Suratul Baƙara.[47] An yi la'akari da cewa fifikon wannan sura ya samo asali ne daga cikakken abin da ta ƙunsa, yayin da fifikon Ayatul Kursiyu ya samo asali ne daga abubuwan tauhidi da ke cikin ma'anarta.[48]
Game da falalar wannan sura kuwa, an ruwaito daga Imam Sajjad (A.S), daga Annabi (S.A.W), cewa duk wanda ya karanta ayoyi huɗu na farkon Suratul Baƙara, da Ayatul Kursiyu da ayoyi biyu da suke bayanta, sannan ya karanta ayoyi uku na ƙarshen surar, ba zai fuskanci wani abin da ba ya so a cikin ransa ko dukiyarsa ba, kuma Shaidan ba zai kusance shi ba, sannan ba zai manta da Alƙur'ani ba.[49]
Bayanin kula
- ↑ Makarim Shirazi, Tafsire Namuna, juzu'i na 1, shafi na 59.
- ↑ Khuramshahi, "Sura-ye Baqara", shafi na 1236; Muhaqqiqiyan, "Sura-ye Baqara", shafi na 700.
- ↑ Khuramshahi, "Sura-ye Baqara", shafi na 1236;
- ↑ Tamimi Amidi, Ghurar al-Hikam, shafi na 338.
- ↑ Khuramshahi, "Sura-ye Baqara", shafi na 1236.
- ↑ Muhaqqiqiyan, "Sura-ye Baqara", shafi na 700.
- ↑ Khuramshahi, "Sura-ye Baqara", shafi na 1236.
- ↑ Muhaqqiqiyan, "Sura-ye Baqara", shafi na 700.
- ↑ Khuramshahi, "Sura-ye Baqara", shafi na 1236.
- ↑ Khuramshahi, "Sura-ye Baqara", shafi na 1236.
- ↑ Tabataba'i, Al-Mizan, juzu'i na 1, shafi na 43.
- ↑ Khamegar, Muhammad, Sakhtare Surehaye Kur'ane Karim, Tahiyye-ye Mu'assese-ye Farhangi-ye Kur'an wa Itrat-e Nurus-Saqalain, Qum, Nashr Nashra, bugu na 1..
- ↑ Makarim Shirazi, Tafsir-e Namuna, juzu’i na 1, shafi na 58.
- ↑ Makarim Shirazi, Tafsir-e Namuna, juzu'i na 1, shafi na 58.
- ↑ Khamagar, Muhammad, Sakhtare Surahaye Qur'ane Karim, Cibiyar Al'adu ta Alƙur'ani da Ahlulbaiti Nuruth-Thaqalain, Qum, Nashr Nashra, bugu na 1..
- ↑ Wahidi, Asbab Nuzul al-Qur'an, shafi na 24–98.
- ↑ Wahidi, Asbab Nuzul al-Qur'an, shafi na 27.
- ↑ Ɗusi, Tafsir al-Tibyan, Dar Ihya al-Turath al-Arabi, juzu'i na 1, shafi na 284.
- ↑ Makarim Shirazi, Tafsir-e Namuna, juzu'i na 1, shafi na 301.
- ↑ Makarim Shirazi, Tafsir-e Namuna, juzu'i na 1, shafi na 302.
- ↑ Ƙummi, Tafsir al-Ƙummi, juzu'i na 1, shafi na 66.
- ↑ Ƙummi, Tafsir al-Ƙummi, juzu'i na 1, shafi na 66.
- ↑ Ɗabrisi, Majma‘ al-Bayan, juzu'i na 2, shafi na 560.
- ↑ Ɗabaɗaba'i, Al-Mizan, juzu'i na 1, shafi na 114; Makarim Shirazi, Tafsir-e Namuna, juzu'i na 1, shafi na 171.
- ↑ Ɗabaɗaba'i, Al-Mizan, juzu'i na 1, shafi na 114; Makarim Shirazi, Tafsir-e Namuna, juzu'i na 1, shafi na 171.
- ↑ Ɗabaɗaba'i, Al-Mizan, juzu'i na 1, shafi na 250–253.
- ↑ Makarim Shirazi, Tafsir-e Namuna, juzu'i na 1, shafi na 389.
- ↑ Mughniyya, Al-Kashif, juzu'i na 1, shafi na 170; Wahidi, Asbab Nuzul al-Qur'an, shafi na 37; Ɗabarani, Tafsir al-Qur'an al-Azim, juzu'i na 1, shafi na 223–224.
- ↑ A matsayin misali, duba: Sayyid Murtada, Al-Shafi fi al-Imama, juzu'i na 3, shafi na 139–140; Ɗusi, At-Tibyan fi Tafsir al-Qur'an, Dar Ihya al-Turath al-Arabi, juzu'i na 1, shafi na 449; Fadil Miƙdad, Al-Lawami‘ al-Ilahiyya fi al-Mabahith al-Kalamiyya, shafi na 332–333.
- ↑ Tureh, Barresi-ye Tatbiqi-ye Vaje-ye Imam dar Ayat-e Ibtala, shafi na 42–44.
- ↑ Makarim Shirazi, Tafsir-e Namuna, juzu'i na 1, shafi na 525.
- ↑ Kulaini, Al-Kafi, juzu'i na 2, shafi na 93.
- ↑ Ɗabrisi, Majma' al-Bayan, juzu'i na 1, shafi na 437.
- ↑ Ɗabaɗaba'i, Al-Mizan, juzu'i na 2, shafi na 30–31.
- ↑ Ɗabaɗaba'i, Al-Mizan, juzu'i na 2, shafi na 31.
- ↑ Ɗabrisi, Majma' al-Bayan, juzu'i na 1, shafi na 437.
- ↑ Ɗaleƙani, Partovi az Quran, juzu'i na 2, shafi na 100.
- ↑ Ayyashi, Al-Tafsir, juzu'i na 1, shafi na 137.
- ↑ Ɗabaɗaba'i, Al-Mizan, juzu'i na 2, shafi na 337.
- ↑ Mughniyya, Al-Kashif, juzu'i na 1, shafi na 396.
- ↑ Makarim Shirazi, Tafsir-e Namuna, juzu'i na 2, shafi na 278.
- ↑ Ɗabrisi, Majma' al-Bayan, juzu'i na 2, shafi na 667.
- ↑ Ɗusi, At-Tibyan, Beirut, juzu'i na 2, shafi na 357.
- ↑ Makarim Shirazi, Tafsir-e Namuna, juzu'i na 2, shafi na 360.
- ↑ Ɗabaɗaba'i, Al-Mizan, juzu'i na 2, shafi na 440; Sayyid Ƙuɗb, Fi Zilal al-Qur'an, juzu'i na 1, shafi na 344; Makarim Shirazi, Tafsir-e Namuna, juzu'i na 2, shafi na 397.
- ↑ Mu'ini, Ayat al-Ahkam, shafi na 1.
- ↑ Ɗabrisi, Majma' al-Bayan, juzu'i na 1, shafi na 111.
- ↑ Makarim Shirazi, Tafsir-e Namuna, juzu'i na 1, shafi na 59.
- ↑ Huwaizi, Nur as-Saƙalain, juzu'i na 1, shafi na 26.
Nassoshi
- Al-Qur'an Kareem, tarjame Muhammad Mahdi Fuladwand, Tehran, Dar al-Qur'an al-Karim, 1418H/1376SH.
- Ayyashi, Muhammad Bin Mas'ud, Al-Tafsir (Tafsir Ayyashi), binciken Hashim Rasuliy, Tehran, Maktabat al-Ilmiyya al-Islamiyya, bugu na farko, 1380H.
- Balaghi, Muhammad Jawad, Ala'ur Rahman fi Tafsir al-Qur'an, Qum, Nashr-e Wajdani, ba tare da shekara ba.
- Fadil Miƙdad, Miƙdad bn Abdullahi, Al-Lawami' al-Ilahiyya fi al-Mabahith al-Kalamiyya, bincike da sharhi na Shahid Ƙazi Ɗabaɗaba'i, Qum, Ofishin Tabligate Islami, bugu na biyu, 1422H.
- Huwaizi, Abd Ali bn Juma'a, Nur as-Saƙalayn, Qum, Isma'iliyan, 1415H.
- Khurramshahi, Qawamuddin, "Suratul Baƙara", a cikin Ƙamus na Alƙur'ani da Binciken Alƙur'ani, Tehran, Dustan–Nahid, 1377SH.
- Kulaini, Muhammad bn Yaƙub, Al-Kafi, Tehran, Dar al-Kutub al-Islamiyya, 1406H.
- Makarim Shirazi, Nasir, Tafsir-e Namuna, Tehran, Dar al-Kutub al-Islamiyya, bugu na farko, 1371SH.
- Mughniyya, Muhammad Jawad, Tafsir al-Kashif, Qum, Dar al-Kitab al-Islamiyya, 1424H.
- Muhaƙƙiƙiyan, Rida, "Suratul Baƙara", a cikin Ƙamus na Zamani na Alƙur'ani Mai Girma, Qum, Intisharat Salman Azada, 1396SH.
- Mu'ini, Muhsin, "Ayat al-Ahkam", Binciken Musulunci, shekara ta 12, lamba ta 1 da 2, Tehran, bazara da daminar 1376SH.
- Ƙuɗb, Sayyid, Fi Zilal al-Qur'an, Beirut, Dar al-Shuruƙ, 1425H.
- Sayyid Murtada, Ali Bin Husaini, Al-Shafi fi al-Imama, bincike da sharhi na Sayyid Abd al-Zahra Husaini, Tehran, Cibiyar Al-Sadiƙ, bugu na biyu, 1410H.
- Tabataba'i, Sayyid Muhammad Husaini, Al-Mizan fi Tafsir al-Qur'an, Beirut, Cibiyar al-A'lami lil-Matbu'at, 1390H.
- Ɗabrani, Sulaiman Bin Ahmad, Al-Tafsir al-Kabir: Tafsir al-Qur'an al-Azim, Jordan, Dar al-Kitab al-Thaqafi, 2008M.
- Ɗabrisi, Fadl Bin Hasan, Majma' al-Bayan fi Tafsir al-Qur'an, Tehran, Nasir Khusraw, 1372SH.
- Tamimi Amidi, Abd al-Wahid, Ghurar al-Hikam wa Durar al-Kalim, gyaran Sayyid Mahdi Rajai, Qum, Dar al-Kutub al-Islami, 1410H.
- Tureh, Yusuf, "Barresi-ye Tatbiqi-ye Vaje-ye Imam dar Ayat-e Ibtala," Mujallar Bincike ta Hikimat da Falsafe Islami, lamba ta 27, 1388SH.
- Ɗusi, Muhammad bn Hasan, Al-Tibyan fi Tafsir al-Qur'an, Beirut, Dar Ihya al-Turath al-Arabi, ba tare da shekara ba.
- Wahidi, Ali bn Ahmad, Asbab Nuzul al-Qur'an, Beirut, Dar al-Kutub al-Ilmiyya, 1411H.
- Ƙungiyar marubuta, Farhang-name-ye Olum-e Quran, Qum, Pazhuheshgah-e Olum wa Farhang-e Eslami., Qum, Cibiyar Binciken Ilimi da Al'adun Musulunci, 1394H.