Daƙiƙa:Wasiyyoyin Sayyida Faɗima (S)

Wasiyyar Sayyida Fatima (S) ta ƙunshi wasiyyoyinta rubutattu da kuma na baka waɗanda ta yi wa Imam Ali (A.S) da sauran mutane. A cikin wasiyyoyinta rubutattu, ta naɗa Imam Ali (A.S), sa'an nan Imam Hassan (A.S), sannan Imam Husaini (A.S) a matsayin waɗanda za su kula da aiwatar da wasiyyarta da kuma tafiyar da dukiyarta. Haka nan, ta ware rabo na musamman ga matan Manzon Allah (S.A.W), da ƴar Abu Zar Gifari, da kuma wasu gungun mabuƙata.
A wasu littattafan tarihi, an ruwaito cewa a cikin wasiyyoyinta na baka, ta buƙaci a taƙaita adadin mutanen da za su halarci jana'izarta, kuma ta yi umurni da a ɓoye wurin da za a binne ta. Haka nan, akwai ruwayoyin da suka bayyana karara cewa ta hana wasu mutane halartar jana'izarta. Waɗannan bayanai sun zo a cikin littattafan Shi'a da kuma wasu littattafan Ahlus-Sunna.
An ɗauki wasiyyar Nana Faɗima (A.S) ta a binne ta da daddare a ɓoye a matsayin wata hanya ta nuna rashin amincewa da kwace halifanci, da kuma yaƙi da waɗanda suka zalunce ta bisa aƙidar Shi'a.
Nau'ukan Wasiyyoyin Nana Faɗima (A.S)
Dangane da ruwayoyin da ke cikin littattafan tarihi na Shi'a da Ahlus-Sunna, an ce Nana Fatima (A.S) ta yi wasiyya da dama, rubutattu ko na baka. Daga cikinsu akwai wasiyya guda wadda ta shafi yadda za a tafiyar da dukiyarta, da kuma wasiyya guda biyu waɗanda ta yi wa Imam Ali (A.S) da Asma'uu bint Umaisi game da yadda za a yi mata sallah, likkafani, da kuma jana'iza.[1]
Wasiyyar Nana Fatima (A.S) rubutacciyya ta keɓanta ne ga batutuwan dukiya da abubuwan da suka shafi hakan. Bisa ga ruwayoyi, ko dai da hannunta ta rubuta wasiyyar, ko kuma Imam Ali (A.S) ne ya rubuta ta bisa buƙatarta.[2]
Wasiyya Game da Yadda Za A yi Sallah da Likkafani Da Binnewa
A kwanakinta na ƙarshe a duniya, Nana Fatima (A.S) ta yi wasiyya guda biyu ga Imam Ali (A.S) game da yadda za a yi mata sallah, likkafani, da kuma jana'iza: ɗaya rubutacce, ɗaya kuma na baka.[3] A cikin waɗannan wasiyyoyin, ta bayyana Imam Ali (A.S) a matsayin bawa mafi sani kuma mafi tsoron Allah a cikin bayin Allah, sannan ta ba shi wasu shawarwari. Baya ga umarnin a binne ta da daddare, ta kuma buƙaci bayan mutuwarta, ya auri Umama Ƴar Abul Asi Bin Rabi, domin ita (Umama) tana jin ƙan ƴaƴan Nana Fatima (A.S) kamar yadda ita ma take ji.[4]
Binnewa Da Daddare Da Hana Wasu Mutane Halartar Jana'iza
Dangane da rahotannin da suka zo a littattafan hadisi, Nana Fatima (A.S) ta yi wa Imam Ali (A.S) wasiyya cewa, waɗanda suka zalunce ta kada su halarci jana'izarta.[5] Ta rantsar da Ali (A.S) cewa Abubakar da Umar[6] da mabiyansu kada su yi mata sallah.[7] Mutane ƙalilan ne kawai aka umarci su sani su kuma halarci jana'izar, su ne: Ummu Salama, Ummu Aiman, Fidda, Hassanaini, Abdullahi Bin Abbas, Salmanul Farisi, Ammar Bin Yasir, Miƙdad, Abu Zar, da Huzaifa.[8] Ɗaya daga cikin wasiyyoyin Nana Fatima (A.S) shi ne a binne ta da daddare[9] kuma a ɓoye wurin kabarinta.[10]
Haka nan, ta yi wasiyya cewa Ali (A.S) shi ne zai zama mai kula da wankan gawa, likkafani, sallah, da kuma binnewa. Sannan ta buƙaci bayan mutuwarta, ya zauna kusa da gawar ta yana karatun Alƙur'ani da addu'a domin hakan ya kawo mata kwanciyar hankali. A ƙarshe, ta damƙa amanar Imam Ali (A.S) ga Allah, sannan ta ba shi shawarar ya kyautata wa yaranta.[11]
Me Ya Sa Nana Fatima (A.S) Ta Yi Wasiyyar A Binne Ta Da Daddare Kuma A Ɓoye?
Wasiyyar Nana Fatima (A.S) na a binne ta da daddare kuma a ɓoye kabarin, ana ɗaukar ta a matsayin wata alama ta nuna rashin amincewa da waɗanda bisa aƙidar Shi'a suka kwace halifanci suka kuma zalunce ta. An ce bayan Nana Fatima (A.S) ta yanke ƙauna daga samun taimakon musulmi wajen dawo da haƙƙinta da na Imam Ali (A.S), ta so kabarin nata ya kasance a ɓoye, kuma halifan musulmi kada ya halarci sallar jana'izarta, domin wannan tambaya ta tarihi ta ci gaba da kasancewa har abada.[12] A cikin ruwayoyin Ahlul-baiti (A.S) ma, an jaddada rashin jin daɗinta ga "Shaikhaini" (Abubakar da Umar); kamar yadda Imam Ali (A.S) ya bayyana cewa dalilin binne ta da daddare shi ne fushin da take yi da wasu mutane.[13] Ibn Abil Hadid, wani masanin tarihi daga Ahlus-Sunna, shi ma ya ruwaito cewa ta yi wasiyyar a binne ta da daddare a matsayin alamar nuna rashin amincewa da halayen wasu daga cikin sahabbai, kuma ta hana su halartar sallarta da jana'izarta.[14] Michel Kadi, marubuci kirista, ya bayyana wannan wasiyyar a matsayin ƙololuwar nuna adawa da nuna rashin amincewa daga Nana Fatima (A.S) .[15] Haka nan, ana kallon wannan wasiyyar a matsayin hujja ta zaluncin da aka yi mata,[16] kuma ana ambatonta a matsayin babban darasi a cikin wa'azozi, rubuce-rubucen juyayi, waƙen juyayi kuma jawabai a lokutan tunawa da ita.
Wasiyya Ga Asma'uu Bint Umaisi
Dangane da ruwayoyin tarihi, Nana Fatima (A.S) ta bayyana damuwarta ga Asma'uu bint Umaisi dangane da yadda za a ɗauki gawarta a kan wani abin ɗauka bayan mutuwarta, har mutane su iya hango siffar jikinta. Asma'u ta shirya mata wani akwatin ɗaukar gawa (tabut) wanda take gani a ƙasar Habasha, wanda yake rufe dukkan jiki.[17] Sa'ad da Nana Fatima (A.S) ta gan shi, sai ta yi wa Asma'uu addu'a.[18] Wasu masana suna ganin wannan akwatin ɗaukar gawa shi ne na farko da aka ƙera a Musulunci.[19]
Haka nan, an ruwaito cewa Nana Fatima (A.S) ta yi wasiyyar cewa bayan rasuwarta, Asma'uu da Ali (A.S) ne kawai za su yi mata wanka, kuma kada wani ya shiga. Bisa wannan umarni, a lokacin da Nana Fatima (A.S) ta rasu, sai A'isha ta yi ƙoƙarin shiga, amma Asma'u ta hana ta. A'isha ta je ta yi ƙara ga Abubakar, inda ta nuna cewa Asma'u ta hana ta shiga kuma ta shirya wani ɗakin ɗaukar gawa (Haudaj) don jana'izar Fatima. Abubakar ya tsaya a ƙofar gidan, ya kuma tsawatar wa Asma'u kan hana A'isha shiga da kuma ƙera wannan ɗakin ɗaukar gawan. Asma'u ta amsa da cewa Nana Fatima (A.S) ce ta ba ta umarnin cewa bayan mutuwarta kada a bar kowa ya shiga, kuma ita ce ta ba ta umarnin ƙera akwatin ɗaukar gawan. Daga nan sai Abubakar ya janye kuma ya ce a aiwatar da duk abin da aka yi wasiyya da shi.[20] A wani ruwayar kuma, an ce Salma, kuyangar Manzon Allah (S.A.W), ita ma ta kasance tare da Asma'u a lokacin wankan Nana Fatima (A.S) kuma ta taimaka wa Imam Ali (A.S).[21]
Wasiyyar Nana Fatima (S) Game da Dukiyarta
Dangane da abin da ya zo a wasiyyar Nana Fatima (A.S) ta rubutacce game da dukiyarta, ta ware wasu rabo daga cikinta ga matan Manzon Allah (S.A.W) da kuma mabuƙatan Bani Hashim. Ta kuma naɗa Imam Ali (A.S), sa'an nan Imam Hassan (A.S), sannan Imam Husaini (A.S) a matsayin manyan ƴaƴanta maza a matsayin waɗanda za su kula da aiwatar da wannan wasiyya.[22] Bisa ga wannan wasiyya, an sadaka da oƙiya tamanin[Tsokaci 1] daga gonakinta a matsayin waƙafi, don a riƙa rarraba ribar da aka samu duk shekara a watan Rajab (Bayan an cire kuɗin kula da gonar) ga waɗannan gurfan da aka ambata: oƙiya 45 ga matan Manzon Allah (S.A.W), sauran kuma ga mabuƙata.[23]
A cikin wannan wasiyya, an kuma ware wa ƴar Abu Zar Gifari rabo, inda aka ba ta wani ɓangare na dukiya da kayan ɗaki. Bugu da ƙari, an tsara cewa tufafin Nana Fatima (A.S) su koma ga ɗaya daga cikin ƴaƴanta mata guda biyu.[24] Haka nan, an damƙa wa Imam Ali (A.S) ikon yanke hukunci kan yanayin gonakin idan wani abu ya faru. A ƙarshe, an ambaci Allah, Miƙdad, Zubair, da Ali (A.S) a matsayin shaidun wannan wasiyya, kuma an bayyana cewa an rubuta wasiyyar ne a lokacin da take cikin ƙoshin lafiya.[25]
Hiɗanul Saba'a (Gonaki Bakwai)
"Hitan Sab'ah" su ne gonaki bakwai waɗanda suka kasance mallakin wani Bayahude mai suna Mukhairiƙ, wanda ya ba su kyauta ga Manzon Allah (S.A.W),[26] shi kuma Manzon Allah (S.A.W) ya mayar da su waƙafi ga Nana Fatima (A.S).[27] Bisa ga wata ruwaya daga Imam Baƙir (A.S) ana amfani da kuɗin shigar waɗannan gonaki don ayyukan alheri da kuma taimaka wa addinin Musulunci, inda aka damƙa amsar su ga Imam Ali (A.S), sannan Imam Hassan (A.S), sannan Imam Husaini [28](A.S), kuma bayan su, sai ya koma hannun manyan ƴaƴan Nana Fatima (A.S).
Ummul Iyyal
Ummul Iyyal wani ƙauye ne da ke tsakanin Makka da Madina,[29] wanda yake da wani maɓuɓɓugar ruwa da ke ɓallewa, kuma ruwan yana shayar da dabino fiye da dubu ashirin. An kiyasta cewa kudin shigar wannan ƙauye a kowace shekara ya kai kimanin dinari dubu tamanin.[30] Ummul Iyyal mallakin Nana Fatima (A.S) ne, kuma ta yi wasiyyar cewa a riƙa amfani da kudin shigarsa a matsayin sadaka.[31]
Bayanin kula
- ↑ Zamani, Waṣaya‑ye Haḍrat Faṭima (s), shafi na 70. Ashuri‑ye Langarudi, Moruri bar Waṣiyat‑name‑ye Haḍrat Faṭima Zahra (Alayha al‑salam), shafi na 68
- ↑ Majlisi, Bihar al‑Anwar, jildi na 100, shafi na 184. Nuri, Mustadrak al‑Wasa'il, jildi na 14, shafi na 54. Mo'ezzi‑ye Malayeri, Jami' al‑Ahadith al‑Shi'a, jildi na 19, shafi na 106.
- ↑ Majlisi, Bihar al-Anwar, jildi na 43, shafi na 178.
- ↑ Fattal Nishaburi, Rawdat al‑Wa'izin, jildi na 1, shafi na 151..
- ↑ Fattal Nishaburi, Rawdat al‑Wa'izin, jildi na 1, shafi na 151.
- ↑ Majlisi, Bihar al‑Anwar, jildi na 29, shafi na 112; kuma jildi na 31, shafi na 619. amili, As‑Ṣahih min Sirat al‑Imam Ali, jildi na 10, shafi na 296.
- ↑ Fattal Nishaburi, Rawdat al‑Wa'izin, jildi na 1, shafi na 151.
- ↑ Ṭabari, Dala'il al‑Imama, shafi na 133. Majlisi, Bihar al‑Anwar, jildi na 43, shafi na 208.
- ↑ Fattal Nishaburi, Rawdat al‑Wa'izin, jildi na 1, shafi na 151. Majlisi, Bihar al‑Anwar, jildi na 31, shafi na 619.
- ↑ Tabari, Dala'il al‑Imama, 1413H, shafi na 133. Majlisi, Bihar al‑Anwar, jildi na 43, shafi na 208.
- ↑ Majlisi, Bihar al‑Anwar, jildi na 79, shafi na 27. Nuri, Mustadrak al‑Wasa'il, jildi na 2, shafi na 316.
- ↑ Qa'imi, Dar Maktab‑e Faṭima (Alayha al‑salam),shafi na 313–314. Zamani, Wasaya‑ye Haḍrat Faṭima (s), shafi na 72.
- ↑ Majlisi, Bihar al‑Anwar, jildi na 43, shafi na 209.
- ↑ Ibn Abi al‑Hadid, Sharh Nahj al‑Balagha, jildi na 16, shafi na 214.
- ↑ Katib al‑Masihi: Az‑Zahra' araḍat al‑zulm wa Intafadat li‑Himayat Siyasat al‑Haqq al‑Ilahi, webgah‑e Shabake‑ye al‑Kawthar
- ↑ Ostad Andelib‑e Hamadani dar Goft‑o‑Gu ba Shafaqna: Dafn‑e Makhfiyaneh va Shabaneh‑ye Haḍrat Zahra (s) Bozorgtarin Sand‑e 'Mazlumiyyat va E'teraż' Ast, Kamfanin dillancin labarai na Shafaqna
- ↑ Majlisi, Bihar al‑Anwar, jildi na 43, shafi na 189.
- ↑ Shaik Ṭusi, Tahzib al‑Ahkam, jildi na 1, shafi na 469. Hurru Amili, Wasa'il al‑Shi'a, jildi na 3, shafi na 220.
- ↑ Nu'uman Maghribi, Da'a'im al‑Islam, Dar al‑Ma'arif, jildi na 1, shafi na 233. Shaikh Ṭusi, Tahzib al‑Ahkam, jildi na 1, shafi na 469.
- ↑ Bayhaqi, Al‑Sunan al‑Kubra, Dar al‑Fikr, jildi na 4, shafi na 35. Dulabi, Az‑Zurriya al‑Ṭahira al‑Nabawiyya, shafi na 154. Ibn Abd al‑Barr, Al‑Isti'ab, jildi na 4, shafi na 1898. Muttaqi Hindi, Kanz al‑Ummal, 1409H, jildi na 13, shafi na 687.
- ↑ Ibn Abd al-Barr, Al-Isti'ab, jildi na 4, shafi na 1862. Ibn Athir, Usdul al-Ghabah, Dar al-Kitab al-Arabi, jildi na 5, shafi na 478. Mizzi, Tahzib al-Kamal, 1413H, jildi na 35, shafi na 197. Ṣafadi, Al-Wafi bi al-Wafayat, jildi na 15, shafi na 190.
- ↑ Majlisi, Bihar al-Anwar, jildi na 100, shafi na 184.
- ↑ Nuri, Mustadrak al-Wasa'il, jildi na 14, shafi na 54. Mu'azzi Malayeri, Jami' al-Ahadith al-Shi'a, jildi na 19, shafi na 106
- ↑ Nuri, Mustadrak al-Wasa'il, jildi na 14, shafi na 54.
- ↑ Majlisi, Bihar al-Anwar, jildi na 100, shafi na 184. Nuri, Mustadrak al-Wasa'il, jildi na 14, shafi na 54. Mu'azzi Malayeri, Jami' al-Ahadith al-Shi'a, jildi na 19, shafi na 106.
- ↑ Ibn Ishaq, Tarakat al-Nabi, 1404H, shafi na 78.Hamawi, Mu'jam al-Buldan, jildi na 5, shafi na 241. Azim-abadi, Awn al-Ma'bud, jildi na 8, shafi na 137
- ↑ Himyari Qummi, Qurb al-Isnad, shafi na 363.Kulaini, Usulul Kafi, jildi na 7, shafi na 47.
- ↑ Kulaini, Usulul Kafi, jildi na 7, shafi na 48. Nu'man Maghribi, Da'a'im al‑Islam, Dar al‑Ma'arif, jildi na 2, shafi na 344.
- ↑ Hamawi, Mu'jam al-Buldan, jildi na 1, shafi na 254.
- ↑ Ibn Hazm, Jamharat Ansab al-Arab, shafi na 140.
- ↑ Hamawi, Mu'jam al-Buldan, jildi na 1, shafi na 254. Ibn al-Jawzi, al-Muntazam, jildi na 1, shafi na 145.
Tsokaci
- ↑ A cikin ma'auni na gargajiya, kowane ukiya (uqiyya) yana daidai da kusan misƙali 7 (misƙal 7).
Nassoshi
- Bayhaqi, Ahmad Ibn Husain, Al-Sunan al-Kubra, Ba a bayyana wurin bugawa ba: Gidan Bugawa na Dar al-Fikr; ba a bayyana shekarar bugawa ba.
- Fattal Nayshaburi, Muhammad Ibn Ahmad, Rawdat al-Wa'izin wa Baṣirat al-Muta'azzin, Qum: Bugawar Raḍi, bugu na farko. 1375 SH.
- Himyari, Abdullah Ibn Ja'far, Qurb al-Isnad, gyara. cibiyar al al-Bayt, Qum: cibiyar al al-Bayt, 1413 AH.
- Hurru Amili, Muhammad, Wasa'ilush Shi'a ila Tahsil Masa'il al-Shari'a, gyara cibiyar al al-Bayt, Qum: cibiyar al al-Bayt, 1414 AH.
- Ibn Abd al-Barr, Yusuf ibn Abdullah, Al-Isti'ab fi Ma'rifat al-Ashab, Mai gyara: Ali Muhammad. Beirut: Dar al-Jil, 1412 AH.
- Ibn Abi al-Hadid, Abd al-Hamid ibn Hibatullah, Sharh Nahj al-Balagha, Beirut: Gidan Bugawa na Raya Kayan Gadon Larabawa. 1385 AH.
- Ibn Hazm, Ali ibn Ahmad, Jumharat Ansab al-Arab, gyara. Kwamitin Malamai, Beirut: Gidan Bugawa na Littattafan Ilimi. 1403 AH.
- Ibn Ishaq, Hammad, Tarakatu al-Nabi,Mai gyara: Akram Ḍiya' al-Umari; ba a bayyana wurin bugawa ba; ba a bayyana shekarar bugawa ba, 1404 AH.
- Ibn Athir, Ali Ibn Muhammad, Usdul al-Ghabah, Beirut: Gidan Bugawa na Littafin Larabci; ba a bayyana shekarar bugawa ba.
- Ibn Dulabi, Muhammad, Az-Zurriyyah al-Ṭahirah al-Nabawiyya, gyara. Sa'd al-Mubarak al-Hasan, Kuwait:Gidan Bugawa na Salafiyya. 1407 AH.
- Ibn al-Jawzi, 'Abd al-Rahman Ibn Ali, Al-Muntazam fi Tarikh al-Umam wa al-Muluk, Masu gyara: Muhammad Abd al-Qadir da Muṣṭafa Abd al-Qadir; Beirut: Gidan Bugawa na Littattafan Ilimi. 1412 AH.
- Kulaini, Muhammad Iibn Ya'qub, Usulul Kafi, ta'liƙin: Ali Akbar Ghaffari, Ba a bayyana wurin bugawa ba: Gidan Bugawa na Littattafan Musulunci.1367 SH.
- Majlisi, Muhammad Baqir, Bihar al-Anwar, Beirut: Cibiyar al-Wafa', 1403 AH.
- Mizzi, Yusuf, Tahzib al-Kamal fi Asma' al-Rijal, Gyara. Bashshar 'Awwad, Beirut: al-Risalah, Bugu na huɗu., 1413 AH.
- Mu'izzi Malayiri, Isma'il, Jami' Ahadith al-Shi'a fi Ahkam al-Shari'a,A ƙarƙashin kulawar Ayatullahi al-Uzma Burujirdi. Qum: Mu'allif, 1412 AH.
- Murtaḍa Amili, Sayyid Ja'far, As-Ṣahih min Sirat al-Imam Ali, Qum: Wila' al-Murtaḍa, 1430 AH.
- Muttaqi al-Hindi, Ala' al-Din, Kanz al-Ummal, Gyara: Bakri Hayyan Ṣakhwah al-Safa, Beirut: Cibiyar al-Risalah, 1409 AH.
- Nu'mani Maghribi, Da'a'im al-Islam, gyara. aṣif ibn 'Ali, Cairo: Mawallafar Ma'arif, 1383 AH.
- Nuri, Husain, Mustadrak al-Wasa'il wa Mustanbaṭ al-Masa'il, gyara. Cibiyar Ahulul-Bayt, Beirut: Cibiyar al al-Bayt, Bugu na biyu.1408 AH.
- Qa'imi, 'Ali, Dar Maktab Faṭima (A.S.): Majmu'ah-i az Maqalat wa Sukhanraniha, Tehran: Bugawar mawallafar Amiri.1377 SH.
- Safadi, Ṣalah al-Din, Al-Wafi bi al-Wafayat, gyara. Ahmad Arna'uṭ daTurki Muṣṭafa, Beirut: Gidan Bugawa na Raya Kayan Gado. 1420 AH.
- Siddiqi Azimabadi, Muhammad Ashraf, Awn al-Ma'bud: SharH Sunan Abi Dawud wa huwa Ghayat al-Maqṣud fi Hall Sunan Abi Dawud, Beirut: Gidan Bugawa na Littattafan Ilimi; bugu na uku. 1415 AH.
- Tusi, Muhammad, Tahzib al-Ahkam fi Sharh al-Muqni'ah lil-Shaik al-Mufid, Mai gyara: Hasan Musawi; Tehran: Gidan Bugawa na Littattafan Musulunci; bugu na huɗu. 1364 SH.
- Yaqut al-Hamawi, Mu'jam al-Buldan, Beirut: Gidan Bugawa na Raya Kayan Gadon Larabawa. 1399 AH.
- «استاد عندلیب همدانی در گفت وگو با شفقنا: دفن مخفیانه و شبانه حضرت زهرا(س) بزرگترین سند «مظلومیت و اعتراض» است»، (Malami Andalib Hamadani a cikin tattaunawa da Shafaqna: Binnewar Sirri da dare ta Sayyida Faṭima (A.S.) ita ce babbar hujja ta zalunci da kuma nuna adawa.), Kamfanin dillancin labarai na Shafaqna, ranar wallafa: 24 Nuwamba 2025 Miladiyya, ranar ziyara: 1 Disamba 2025 Miladiyya.
- «کاتب المسیحی: الزهراء عارضت الظلم وانتفضت لحمایة سیاسة الحق الإلهی»، (Marubucin Kirista: Fatima ta yi adawa da zalunci kuma ta tashi domin kare siyasar gaskiyar Allah.), Shafin yanar gizo na Al-Kawthar Network, ranar ziyara: 30 Nuwamba 2025 Miladiyya.
- Ṭabari, Muhammad, Dala'il al-Imamah,Mai gyara: Sashen Nazarin Musulunci; Qum: Cibiyar Al-Batha.1413 AH.
- Ashuri Langarudi, Hassan.، «مروری بر وصیتنامه حضرت فاطمه زهرا(س)»، (Dubawa kan wasiyyar Sayyida Faṭima al-Zahra (A.S).), A cikin jaridar ilimi ta shekara-shekara Rah-Tushah, lamba ta 11, shekara ta 2022 Miladiyya.
- Zamani, Rajab Ali، «وصایای حضرت فاطمه(س)»، (Wasiyyoyin Sayyida Faṭima (A.S).), A cikin mujallar Farhang-e Kowsar, lamba ta 69, shekara ta 2007 Miladiyya.