Daƙiƙa:Suratul An'am
Ma'ida Suratul An'am A'araf | |
| Lambar Sura | 6 |
|---|---|
| Juzu'i | 7 da 8 |
| Jerantuwa Ta Sauka | 55 |
| Adadin Ayoyi | 165 |
| Adadin Kalmomi | 3055 |
| Adadin Haruffa | 12420 |
Suratul An'am ita ce sura ta shida a cikin Alƙur'ani, kuma tana daga cikin surorin Makka. Tana cikin juz'i na bakwai da na takwas. An sanya mata suna "Al-An'am", wato dabbobin gida masu ƙafa huɗu, saboda an ambaci dabbobi a cikin ayoyi goma sha biyar na wannan sura.
Babban jigon Suratul An'am shi ne tushen aƙidar addini, wato Tauhidi, Annabci da Tashin Alƙiyama. A cikin surar an kawo hujjoji da tattaunawar Annabi Ibrahim (A.S) da kafirai game da bautar taurari da rana.
Aya ta 20 tana magana ne game da yadda Ahlul-Kitabi suka san siffofin Annabi Muhammad (S.A.W), sannan Ayar Wizru (aya ta 164) ma tana daga cikin shahararrun ayoyin Suratul An'am.
Wasu daga cikin ayoyin hukunce-hukunce na wannan sura sun haɗa da haramcin kashe wanda bai cancanci a kashe shi ba, haramcin zagin kafirai, haramcin ƙirƙira ƙarya ga Allah da Annabi (S.A.W), da kuma haramcin cin naman dabbar da ba a yanka ta da ambaton sunan Allah ba.
A wasu ruwayoyi an bayyana cewa an saukar da wannan sura ga Annabi (S.A.W) gaba ɗaya tare da mala'iku dubu saba'in masu tasbihi. Kuma duk wanda ya karanta ta, waɗannan mala'iku za su riƙa yi masa tasbihi har zuwa ranar Alƙiyama.
Gabatarwa
- Sanya suna
An sanya wa wannan sura suna An'am (dabbobin gida masu ƙafa huɗu) saboda an yi magana game da waɗannan dabbobi a cikin ayoyi goma sha biyar na surar, wato daga aya ta 136 zuwa ta 150. A cikin wannan sura, an ambaci kalmar An'am sau shida.[1]
- Wurin da Aka Saukar da Ita da Tsarin Saukarwa
Suratul An'am tana daga cikin surorin Makka. A tsarin jerin saukar surorin Alƙur'ani, ita ce sura ta 55 da aka saukar wa Annabi Muhammad (S.A.W). Amma a tsarin da aka tsara Alƙur'ani a cikin mus'haf na yanzu, ita ce sura ta 6,[2] kuma tana cikin juz'i na 7 da na 8 na Alƙur'ani.
- Yawan Ayoyi da Sauran Siffofinta
Suratul An'am tana da ayoyi 165, kalmomi 3055,[3] da haruffa 12420.[4] Dangane da tsawonta, tana daga cikin Sab'u Ɗiwal, wato dogayen surorin Alƙur'ani, kuma ta ƙunshi fiye da juz'i ɗaya na Alƙur'ani.[5]
Suratul An'am tana daga cikin surorin da ake kira Jam'iyyun Nuzul, domin bisa ga wasu ruwayoyi, an saukar da dukkan ayoyin surar ga Annabi (S.A.W) gaba ɗaya a lokaci guda.[6] Haka kuma, saboda surar ta fara da godiya da yabon Allah, tana daga cikin surorin da ake kira Hamidat.[7]
Abun Ciki
A cewar Allama Ɗabaɗaba'i, babban jigon Suratul An'am, kamar sauran surorin Makka, shi ne tushen aƙidar addini, wato Tauhidi, Annabci da Tashin Alƙiyama, musamman ma tana jaddada imani da Allah Makaɗaici. A cewar Tafsir Almizan, mafi yawan ayoyin surar suna gabatar da hujjoji a kan Tauhidi, Annabci da Tashin Alƙiyama, domin ƙaryata aƙidar mushrikai. Haka kuma, surar ta bayyana wasu daga cikin hukunce-hukuncen fiƙihu, musamman abubuwan da Shari'a ta haramta.[8]
Ruwayoyi Da Labarai
- Tattaunawar Annabi Ibrahim (A.S) tare da Azara (Aya ta 74)
- Hujja da tattaunawar Annabi Ibrahim (A.S) da mushrikai game da bautar Taurari, Rana da Wata (Aya ta 76-81)
Shahararrun Ayoyi
Ayar Wizru (aya ta 164), da kuma aya ta 20, wadda ta yi bayani kan yadda Ahlul-Kitabi suka san siffofin Annabi (S.A.W) tun kafin zuwansa. Haka kuma, aya ta 160, wadda ta bayyana cewa wanda ya aikata kyakkyawan aiki zai samu lada ninki goma, suna daga cikin shahararrun ayoyin Suratul An'am.
Aya Ta 17
Idan Allah Ya shafe ka da wata cuta ko wata illa, babu mai iya kawar da ita sai Shi. Idan kuma Ya kawo maka wani alheri, to Shi ne Mai iko a kan komai.
An bayyana manufar Suratul An'am da cewa ita ce kawar da tushen abubuwan shirka. Saboda haka, ayar tana yin Allah wadai da karkata ga wanin Allah, kuma tana bayyana cewa kada mutum ya koma ga gumaka ko abubuwan bautar ƙarya domin magance matsaloli, kawar da cuta ko neman amfanin duniya. Domin idan wata cuta ko wata illa ta same ka, babu mai iya kawar da ita sai Allah; kuma idan wani alheri ko ni'ima ta same ka, to hakan yana faruwa ne da ikon Allah.[10] An kuma bayyana wannan aya da cewa tana nuna rinjayen nufin Allah a kan dukkan sauran nufi, tare da yin watsi kai tsaye da aƙidar masu imani da asalin alheri da sharri guda biyu, waɗanda suke ganin akwai tushe biyu masu zaman kansu na alheri da sharri.[11]
A mahangar Allama Ɗabaɗaba'i, manufar Suratul An'am ita ce bayyana tauhidi da tabbatar da cewa Allah shi ne Ubangiji guda ɗaya na mutum da dukkan halittu. A fahimtarsa, kalmar "Durru" a cikin wannan aya ba ta nufin azabar Ranar Alƙiyama ba, sai dai wata cuta ko wata illa da babu wanda zai iya kawar da ita sai Allah. Saboda haka, mutum ya kamata ya dogara da alherin Allah kaɗai, domin Shi ne Ubangijin da ya cancanci a bauta wa, kuma babu abin da zai iya hana cikar nufinsa, domin Shi Mai iko ne a kan komai.[12]
A cikin Tafsir Namuna kuma an bayyana cewa wannan aya tana ƙaryata aƙidar sanawiyyat (Tushe Biyu), wato imani da tushe biyu na alheri da sharri. Tun da babu sharri tsantsa a duniya, idan aka danganta durr (illa) ga Allah, abin da ake nufi shi ne wani abu da a zahiri yake kama da cire ni'ima, amma a haƙiƙaninsa yana iya zama alheri, domin yana iya kasancewa domin faɗakar da mutum, tarbiyyantar da shi, kawar da girman kai da tawaye, ko kuma saboda wasu hikimomi da maslahohi.[13]
Muhimman Abubuwan Lura
- Akwai wasu ayoyin Alƙur'ani masu ma'ana makamanciyar abin da wannan aya ta ƙunsa, musamman game da wahalhalun da suke samun mutane kamar tsanani, talauci, rashin lafiya da damuwa (Durru). Daga cikin waɗannan ayoyi akwai: Suratul A'araf, aya ta 95; Suratu Yunus, aya ta 12; Suratur Rum, aya ta 33; Suratuz Zumar, ayoyi na 8 da 49; Suratu Hud, aya ta 10; Suratu Fussilat, aya ta 50; Suratun Nahl, aya ta 53; Suratul Isra'i, aya ta 67, da sauransu.A cikin waɗannan ayoyin, Suratu Yunus, aya ta 107 ce ta fi kama da wannan aya: Idan Allah Ya shafe ka da wata cuta, babu mai iya kawar da ita sai Shi. Idan kuma Ya nufe ka da wani alheri, babu mai iya hana falalarSa. Yana saukar da ita ga wanda Ya so daga cikin bayinSa. Kuma Shi Mai yawan gafara ne, Mai jin ƙai.
- Jimlar "in yamassaka" (Idan Allah ya shafeka) wadda aka maimaita sau biyu a cikin ayar, dangane da samun durr (sharri/illa) ko alheri ga mutum, tana ɗauke da kalmar "massu" (Shafa). Wannan kalma tana nuna ƙanƙanta da rashin girman abin da ya sami mutum, ko alheri ne ko sharri, idan aka kwatanta shi da ikon Allah marar iyaka. Duk da haka, wannan wahala ko illa mai ƙanƙanta tana iya yi wa mutum, wanda halitta ce mai iyaka, nauyi har ya kasa jurewa.[14]
- Ayoyi na 18 da 19 na Suratul An'am gaba ɗaya suna isar da saƙon cewa duk wani alheri ko sharri da ya sami mutum yana faruwa ne da izinin Allah da nufinsa. Amma wannan ba yana nufin cewa an tilasta wa mutum yin abin da yake yi ba. A cikin tsarin halitta, kowane sababi da dalili yana yin tasirinsa gwargwadon izini da nufin Allah. Saboda haka, idan mutum ya zaɓi wani dalili ko sababi, dole ne ya yi tsammanin sakamakon da wannan dalili yake haifarwa bisa tsarin halitta. [15]
Haka kuma, ƙarshen aya ta 18: (Kuma Shi ne Mai rinjaye a bisa bayinSa, kuma Shi ne Mai hikima, Masani.) tana ƙunshe da muhimman ma'anoni guda biyu: Na farko: Ma'anar "Al-ƙahir" (Mai rinjaye) ita ce Allah yana da cikakken rinjaye a kan halittu, ta yadda wanda aka rinjaya ba shi da ikon ƙin karɓar rinjayenSa. Misali, ruwa yana kashe wuta ya hana ta ci gaba da tasiri, ko kuma wuta tana mai da ruwa tururi ko ta busar da shi. Duk waɗannan tasirori suna faruwa ne da izinin Allah da nufinsa. Wannan shi ne ma'anar rinjayen Allah. Na biyu: Duk da cewa Allah yana da cikakken iko da rinjaye marar iyaka, duk ayyukanSa suna gudana ne bisa hikima da cikakken sani. Wannan shi ne abin da kalmomin ƙarshen ayar suke tabbatarwa: kuma Shi ne Mai hikima, Masani.[16][Tsokaci 1]
Aya Ta 20
Waɗanda Muka ba wa Littafi, suna saninsa [wato Annabi Muhammad (S)] kamar yadda suke sanin 'ya'yansu. Waɗanda suka jefa kansu cikin hasara ba za su yi imani ba.
An sake ambaton wannan aya a Suratul Baƙara aya ta 146.[17] An saukar da ita ne a matsayin amsa ga mushrikai waɗanda suka yi iƙirarin cewa sun tuntuɓi Ahlul-Kitabi, amma ba su samu wani bayani game da Annabi Muhammad (S.A.W) ba. Alƙur'ani ya bayyana cewa[Tsokaci 2] Ahlul-Kitabi ba wai kawai sun san cewa Annabi (S.A.W) zai bayyana ba ne, har ma sun san cikakkun siffofinsa da alamominsa.[18]
Kamar yadda aka ruwaito daga Abdullahi Bin Salam, wanda yana daga cikin malaman Yahudawa sannan ya karɓi Musulunci, ya ce: "Na fi saninsa fiye da yadda nake sanin ɗana.[19] Wasu malamai sun fahimci daga ƙarshen ayar: (Waɗanda suka yi hasarar rayukansu, to ba su yi imani ba.) cewa ilimi da sanin gaskiya kaɗai ba su isa su ceci mutum ba. Akwai mutanen da suka san Allah, suka san Annabi, kuma suka san addini, amma saboda ƙiyayya, taurin kai da ƙin gaskiya suka zama cikin masu hasara. Haka kuma, ɓoye gaskiya bayan an san ta na iya jawo wa mutum mummunan ƙarshe da hasara.[20]
Ayar Mafatihul Gaibi
Kuma maɓallan gaibu suna wurinSa Shi kaɗai. Babu wanda ya san su sai Shi. Kuma Ya san abin da yake a ƙasa da abin da yake cikin teku. Babu wata ganye da take faɗuwa face Ya san ta, kuma babu wata ƙwaya a cikin duhun ƙasa, kuma babu wani ɗanye ko busasshe face yana cikin Littafi bayyananne.
An bayyana cewa kalmomin "ɗanye da busasshe" suna nuni ne ga dukkan abubuwa gaba ɗaya, wato babu wani abu da ya kuɓuta daga sanin Allah. Malaman tafsiri sun yi saɓanin ra'ayi game da abin da ake nufi da "Littafi bayyananne". [21] A cikin Tafsirin Almizan, an bayyana cewa "Littafi bayyananne" ba wannan duniyar da muke ciki ba ce wadda ta ƙunshi halittu. A maimakon haka, Littafi ne da aka rubuta tsarin halittu da abubuwan da suka shafe su a cikinsa. Wannan Littafi ya riga halittun, kuma zai kasance bayan halittun sun ƙare.[22]
A cikin Tafsir Namuna kuma, an bayyana cewa mafi kusancin fahimta shi ne cewa abin da ake nufi da "Littafi bayyananne" shi ne matsayin ilimin Allah; wato dukkan halittu suna cikin iliminSa marar iyaka. Fassara "Littafi bayyananne" da Allawhul Mahfuz ma tana iya dacewa da wannan ma'ana.[23] Haka kuma, ana karanta aya ta 59 ta Suratul An'am a cikin raka'a ta biyu ta Sallar Gufaila, wadda take daga cikin sallolin nafila da ake yi tsakanin sallar Magariba da Isha'i.[24]
Aya Ta 160
Duk wanda ya zo da kyakkyawan aiki, zai sami lada ninki goma na makamancinsa; kuma duk wanda ya zo da mummunan aiki, ba za a saka masa da komai ba face kwatankwacinsa, kuma ba za a zalunce su ba.
An ruwaito hadisai masu yawa daga Shi'a da Ahlus-Sunna dangane da wannan aya, wato Aya ta 160 ta Suratul An'am.[25]
A wasu daga cikin ruwayoyin an bayyana cewa, lokacin da ayar nan ta sauka: (Duk wanda ya zo da kyakkyawan aiki, zai sami lada mafi alheri daga gare shi,) Annabi Muhammad (S.A.W) ya roƙi Allah Ya ƙara masa lada. Sai Allah Ya saukar da wannan aya: (Duk wanda ya aikata kyakkyawan aiki, zai sami lada ninki goma na shi.) Daga nan kuma Annabi (S) ya sake roƙon Allah Ya ƙara lada. Sai Allah Ya saukar da wannan aya: (Wane ne zai bai wa Allah rance mai kyau, domin Ya ninka masa shi sau da yawa?)[26]
Wasu daga cikin malaman tafsiri sun ambaci muhimman abubuwa biyu yayin bayanin wannan aya. Na farko, amfani da kalmar "جاءَ" (Ja'a) yana nuna cewa ladan da hukuncin azabar da ake magana a kansu a wannan aya suna da alaƙa da Ranar Alƙiyama. Domin a duniya, akwai wasu laifuffuka da mutum zai iya gogewa ko ma a mayar da su alheri ta hanyar tuba. Haka kuma, akwai wasu kyawawan ayyuka waɗanda za su iya lalacewa ko su tafi a banza saboda riya, yin alfahari da ibada, da sauran zunubai. Saboda haka, abin da yake zama ma'auni shi ne aikin da mutum ya zo da shi a gaban Allah a Ranar Alƙiyama. Na biyu, duk da cewa ayar tana magana ne game da aiki na alheri da na sharri, amma bisa ga ruwaya, duk wanda ya yi niyyar aikata alheri yana samun lada saboda wannan niyya. Amma idan mutum ya yi mummunar niyya, ba za a azabtar da shi ba matuƙar bai kai ga aikata wannan mugun aikin ba. Wannan yana daga cikin falalar Allah ga bayinsa.[27]

Aya Ta 164
Kuma babu wani mai ɗaukar nauyi da zai ɗauki nauyin (zunubin) wani.
Malaman tafsiri sun bayyana cewa wannan aya tana nuna adalcin Allah wajen hukunta masu aikata mugunta, domin babu wani mutum da za a hukunta saboda zunubin wani. Wato, kowane mutum zai ɗauki alhakin abin da ya aikata da kansa. Bisa ga abin da ya zo a cikin Alƙur'ani a cikin Suratun Najmi,[Tsokaci 3] ayoyi na 37–38, irin wannan hukunci yana daga cikin ƙa'idojin da aka samu a wasu addinai ma.[28]
Dangane da alaƙar wannan aya da Aya ta 25 ta Suratun Nahli,[29] an bayyana cewa dalilin da ya sa masu ɓatar da mutane suke ɗaukar wani ɓangare na nauyin zunubin waɗanda suka ɓatar, shi ne saboda su ne suka jawo wa wasu mutane ɓata. Saboda haka, a zahiri ba sa ɗaukar zunubin wani mutum a madadinsa, sai dai suna ɗaukar nauyin zunubin nasu, wato zunubin da suka aikata ta hanyar ɓatar da wasu.[30][Tsokaci 4]
Ayoyin Hukunce-hukunce
Malamai fiƙihu sun yi amfani da fiye da ayoyi 15 daga Suratul An’am wajen fitar da hukunce-hukuncen fiƙihu.[31] Ayoyin da suke ƙunshe da hukuncin shari'a, ko kuma waɗanda ake amfani da su a cikin tsarin fitar da hukunce-hukuncen fiƙihu, ana kiransu Ayatul Ahkam, wato ayoyin da ake samun hukunce-hukuncen shari'a daga gare su.[32] A teburin da ke gaba, an kawo wasu daga cikin Ayatul Ahkam na Suratul An'am
| Lambar Aya | Rubutu | Babi | Maudu'i |
|---|---|---|---|
| 21 | Kuma wa ya fi zalunci fiye da wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, ko ya ƙaryata ayoyinsa | Haramcin jingina ƙarya ga Allah | |
| 72 | Kuma ku tsayar da sallah kuma ku ji tsoronsa | Ibada | Wajabcin tsayar da sallah |
| 108 | Kuma kada ku zagi waɗanda suke kira (suke bautawa) baicin Allah, sai su zagi Allah da ƙiyayya ba tare da ilimi ba | Babin Mu'amala da Jama'a (Hukunce-hukuncen Mu'amala da Jama'a) | Haramcin zagin Kafirai da abubuwan bautarSu |
| 118 | Saboda haka, ku ci daga abin da aka ambaci sunan Allah a kansa | Abinci da abin sha | Yanka dabbobi da sunan Allah |
| 121 | Kuma kada ku ci daga abin da ba a ambaci sunan Allah a kansa ba; kuma lalle hakan fasiƙanci ne | Abinci da abin sha | Haramcin cin naman dabbobin da ba a yanka su da sunan Allah ba |
| 141 | Kuma Shi ne Ya halitta lambuna masu ɗagawa a kan turaku da waɗanda ba a ɗagawa a kan turaku… Ku ci daga 'ya'yansu idan sun yi 'ya'ya, kuma ku bayar da hakkinsa a ranar girbinsa | Zakka | Wajabcin ba da zakkar Amfanin gona |
| 145 | Ka ce: Ban sami wani abin da aka yi wahayi zuwa gare ni wanda aka haramta wa mai ci ya ci ba, face ya kasance mushe ne… To, duk wanda ya shiga cikin larura, ba tare da neman haramun ba kuma ba tare da ya wuce gona da iri ba… | Abinci da abin sha | halaccin cin mushe da waninsa a halinsa larura |
| 151 | Kuma kada ku kashe rai wanda Allah Ya haramta [a kashe shi], sai da haƙƙi | Haddodi da Diyya da Ƙisasi | Haramcin kashe mutane ba tare da haƙƙi ba |
| 152 | Kuma kada ku kusanci dukiyar maraya, sai da abin da yake mafi kyau, har ya kai ga balagarsa | Gado | Haramcin yin amfani ko gudanar da dukiyar marayu ba tare da kiyaye maslaharsu ba |
| 152 | Kuma ku cika ma'auni da mizani cikin adalci | Mu'amala | Wajabcin kiyaye adalci cikin awo da mizani |
| 162 | Ka ce: Lalle, sallata da ibadata da rayuwata da mutuwata duk na Allah ne, Ubangijin talikai | Ibada | Wajabcin gujewa riya a cikin ibada da sallah |
Falala Da Fa'idoji
Hadisai sun ba Suratul An'am matsayi mai girma. A cikin Tafsir Nurus Saƙalaini, an ruwaito daga Imam Rida (A.S) cewa an saukar da Suratul An'am gaba ɗaya tare da mala'iku 70000, waɗanda suke yin tasbihi, tahalili wato "La haula wa la ƙuwwata illa billah" da kuma kabbara. Duk wanda ya karanta Suratul An'am, waɗannan mala'iku za su ci gaba da yi masa tasbihi har zuwa Ranar Alƙiyama.[33] Irin wannan hadisin kuma an ruwaito shi daga Annabi (S.A.W).[34]
Haka kuma, a cikin littafin Sawabul A'amal, an ruwaito daga Imam Sadiƙ (A.S) cewa an saukar da Suratul An'am gaba ɗaya ga Annabi Muhammad (S.A.W) tare da rakiyar mala'iku 70000. Saboda haka, ya kamata a girmama ta, domin a wurare 70 daga cikinta akwai Ismul A'zam na Allah. Kuma da mutane sun san abin da ke cikin wannan sura, da ba za su taɓa barin karanta ta ba.[35]
Bayanin kula
- ↑ Khurramshahi, Suratul An'am, shafi na 1237.
- ↑ Ma'rifat, Amuzish Ulumul Qur'an, 1371S, juzu'i na 2, shafi na 166.
- ↑ Khurramshahi, Suratul An'am, shafi na 1238.
- ↑ Sa'alabi, Al-Kashfu wal-Bayan, juzu'i na 4, shafi na 131.
- ↑ Khurramshahi, Suratul An'am, shafi na 1238.
- ↑ Makarim Shirazi, Tafsir Namuna, juzu'i na 5, shafi na 143.
- ↑ Sakhawi, Jamalul Qurra'i, Beirut, juzu'i na 1, shafi na 179.
- ↑ Allama Ɗabaɗaba'i, Almizan, juzu'i na 7, shafi na 5
- ↑ Khamagari, Muhammad, Sakhtare Surahaye Kur’ani Karim.
- ↑ Makarim Shirazi, Tafsir Namuna, juzu'i na 5, shafi na 174.
- ↑ Makarim Shirazi, Tafsir Namuna, juzu'i na 5, shafi na 175.
- ↑ Allama Ɗabaɗaba'i, Almizan, juzu'i na 7, shafi na 34.
- ↑ Makarim Shirazi, Tafsir Namuna, juzu'i na 5, shafi na 175.
- ↑ Ɗabaɗaba'i, Almizan, juzu'i na 7, shafi na 35.
- ↑ Almizan, juzu'i na 7, shafi na 35.
- ↑ Ɗabrisi, Majma'ul Bayan, juzu'i na 4, shafi na 435.
- ↑ Amma an bayyana ma'anar wannan aya a wasu ayoyi daban da kalmomi masu bambanci, kamar Suratul A'araf, aya ta 157; Suratul Fath, aya ta 29; da Suratush Shu'ara, aya ta 197. (Ɗabaɗaba'i, Almizan juzu'i na 7, shafi na 40).
- ↑ Makarim Shirazi, Tafsir Namuna, juzu'i na 5, shafi na 182.
- ↑ Makarim Shirazi, Tafsir Namuna, juzu'i na 1, shafi na 499.
- ↑ Ƙara'ati, Muhsin, Tafsir Nur, juzu'i na 2, shafi na 430.
- ↑ Ɗabaɗaba'i, Almizan, juzu'i na 7, shafi na 126.
- ↑ Makarim Shirazi, Tafsir Namuna, juzu'i na 5, shafi na 271.
- ↑ Ɗabrisi, Majma'ul Bayan juzu'i na 4, shafi na 481. Abul-Futuh Razi, Raudatul Jinan, juzu'i na 7, shafi na 315.
- ↑ Ɗabaɗaba'i Yazdi, Al-Urwatul Wusƙa (Muhasha), juzu'i na 2, shafi na 246–247.
- ↑ Ɗabaɗaba'i, Almizan, juzu'i na 7, shafi na 393.
- ↑ Suratul Baƙara, aya ta 245. Ayyashi, Kitabut Tafsir, juzu'i na 1, shafi na 131.
- ↑ Ƙara'ati, Muhsin, Tafsir Nur, Cibiyar Farhange Az Darsehaye Az Qur'an, bugu na 11.
- ↑ Ƙara'ati, Tafsir Nur, juzu'i na 3, shafi na 396.
- ↑ «لِيَحْمِلُوا أَوْزَارَهُمْ كَامِلَةً يَوْمَ الْقِيَامَةِ ۙ وَمِنْ أَوْزَارِ الَّذِينَ يُضِلُّونَهُم بِغَيْرِ عِلْمٍ ۗ أَلَا سَاءَ مَا يَزِرُونَ: Domin su ɗauki cikakken nauyin zunubansu a Ranar Alƙiyama, da kuma wani ɓangare na nauyin zunuban waɗanda suke ɓatarwa ba tare da sun sani ba. Ku saurara! Lallai abin da suke ɗauka mummunan nauyi ne..»
- ↑ Makarim Shirazi, Tafsir Namuna, juzu'i na 6, shafi na 65; Ƙara'ati, Tafsir Nur, juzu'i na 3, shafi na 397; Ɗabaɗaba'i, Almizan, juzu'i na 12, shafi na 231.
- ↑ Duba: Irawani, Durusr Tamhidiyye Fi Tafsir Ayatul Ahkam, juzu'i na 2, shafi na 1053.
- ↑ Mu'ini «Ayatul Ahkam»
- ↑ Huwaizi, Nurus Saƙalain, juzu'i na 1, shafi na 696.
- ↑ Ɗabrisi, Majma'ul Bayan, juzu'i na 4, shafi na 421.
- ↑ Shaikh Saduƙ, Sawab al-A'mal, shafi na 105.
Tsokaci
- ↑ «وَ هُوَ اَلْحَكِيمُ اَلْخَبِيرُ» Ma'anarsa ita ce: Duk da ikonSa a kansu, ba Ya yin komai sai abin da hikima take buƙata. Al-Khabir kuwa yana nufin Mai cikakken sani game da abu. Ɗabrisi, Majma'ul Bayan, juzu'i na 4, shafi na 435.
- ↑ Daga wasu ayoyin Alƙur'ani ana fahimtar cewa Ahlul Kitabi gaba ɗaya sun san Annabi Muhammad (S) tare da cikakkun bayanansa. Amma daga wasu ayoyin kuma ana fahimtar cewa malamai da masana na Ahlul Kitabi, wato Yahudawa da Kiristoci, sun san Annabi (S) sosai tare da dukkan siffofinsa, amma suna ɓoye wannan gaskiyar, ba sa bayyana ta ga sauran jama'a. Ɗabaɗaba'i, Almizan, juzu'i na 7, shafi na 40.
- ↑ وَإِبْرَاهِيمَ الَّذِي وَفَّىٰ *أَلَّا تَزِرُ وَازِرَةٌ وِزْرَ أُخْرَىٰ ترجمه: و در کتب ابراهیم، Kuma a cikin littattafan Ibrahimu, wanda ya cika aikinsa yadda ya kamata, an bayyana cewa babu wani mutum da zai ɗauki nauyin zunubin wani a kansa.
- ↑ Tambaya: Idan mutum ba ya ɗaukar zunubin wasu a kansa, to mene ne ma'anar abin da ya zo a cikin Alƙur'ani cewa shugabannin ɓata da karkatacciyar hanya za su ɗauki nauyin zunuban mabiyansu? Amsa: Shugabannin ɓata sun zama sanadin karkatar da wasu mutane. Saboda haka, a zahiri abin da suke ɗauka shi ne zunubin ɓatar da wasu da kuma karkatar da su daga gaskiya. Wannan hukunci sakamako ne na ayyukansu da kansu, ba wai suna ɗaukar zunubin wasu mutane a madadinsu ba. Ɗabaɗaba'i, Al-Mizan, juzu'i na 12, shafi na 231.
Nassoshi
- Abul Futuh Razi, Raudul Jinan wa Ruhul Jinan fi Tafsiril Qur'an, gyara: Muhammad Mahdi Nasih da Muhammad Ja'afar Yahaki, Mashhad, Astani Qudsi Razawi, Bunyadin Binciken Musulunci, bugu na 1, 1408H.
- Qur'an Kareem, Tarjame Muhammad Mahdi Fuladwand, Tehran, Darul Qur'anil Karim, 1418H/1376Sh.
- Arusi Huwaizi, Abdul Ali Bin Juma'a, Tafsir Nurus Saƙalain, bincike: Sayyid Hashim Rasuliy Mahallati, Qum, Intisharatu Isma'iliyan, bugu na 4, 1415H.
- Baƙir Irwani, Durus Tamhidiyya fi Tafsiri Ayatil Ahkam, Qum, Darul Fiƙh, 1423H.
- Daneshname Qur'an Wa Qur'an Pajuhi, ƙarƙashin jagorancin Baha'uddin Khurramshahi, Tehran, Dustan–Nahid, 1377Sh.
- Makarim Shirazi, Nasir, Tafsir Namuna, Tehran, Darul Kutubil Islamiyya, bugu na 1, 1374Sh.
- Makarim Shirazi, Nasir, Tafsir Namuna, Tehran, Darul Kutubil Islamiyya, bugu na 10, 1371Sh.
- Ma'rifat, Muhammad Hadi, Amuzish Ulumul Qur'an, [ba a ambaci wurin bugawa ba], Cibiyar Bugawa Wa Nashre Sazimane Tabligate Islami, bugu na 1, 1371Sh.
- Ƙara'ati, Muhsin, Tafsir Nur, Tehran, Cibiyar Farhnge Darshehaye Qur'an, bugu na 11, 1383Sh.
- Saduƙ, Muhammad Bin Ali, Sawabul A'mal wa Iƙabul A'mal, Qum, Darush Sharif Radi, 1406H.
- Sa'adi Shirazi, Muslih bn Abdullahi, Sharh Bustan, sharhi: Muhammad Khaza'ili, Tehran, Javidan, 1356Sh.
- Sa'alabi, Ahmad bn Muhammad, Tafsirus Sa'alabi (At-Tafsiru al-Kabir), Beirut, Daru Ihya'it Turasil Arabi, 1422H.
- Ɗabrisi, Fadl Bin Hassan, Majma'ul Bayan fi Tafsirul Qur'an, Tehran, Nasir Khusrau, 1372Sh.
- Ɗabaɗaba'i, Sayyid Muhammad Husaini, Almizan fi Tafsirul Qur'an, Beirut, Cibiyar A'lami lil Matbu'at, bugu na 2, 1390H.
- Ɗabaɗaba'i, Sayyid Muhammad Husaini, Almizan fi Tafsirul Qur'an, Qum, Intisharatu Islami, 1417H.