Daƙiƙa:Musa (Annabi)
| Na Uku cikin Annabawa Ulul Azmi | |
|---|---|
Musa a dutsen Ɗur, aikin Farhad Rafi'i | |
| Suna | Musa |
| Suna a cikin Kur'ani | Musa |
| Maimaitauwar sunan a Kur'ani | Karo 136 cikin ayoyi 131 cikin surori 36 |
| Sunan a cikin littafi Mai tsarki | Moses |
| Laƙabi | Kalimullahi |
| Haihuwa | Shekaru 250 kafin haihuwar Annabi Ibrahim (A.S) a Misra |
| Rasuwa | Kusan ƙarnoni 17 kafin haihuwar Almasihu a lokacin rashin matsugunin Bani Isra'il a jeji |
| Tsawon rayuwa | Shekara 120 |
| Mahallin rayuwa | Madyana |
| Iyaye | Imran•Yukabad |
| Mutanensa | Bani Isra'il |
| wurin da aka aiko shi | Ɗur Sina |
| Bayan | Annabi Ibrahim |
| Kafin | Annabi Isa |
| Halifan | Haruna ne ya kasance magajinsa |
| Addini | Yahudanci |
| Mu'ujiza | Canja Sanda Zuwa Maciji•Raba teku gida biyu•Yadul Baida (Farin hannu) |
| Labarinsa a Kur'ani | Suratul Isra'i•Kashe Baƙibɗe•Ƙetarar Da Bani Isra'ila Daga Teku•Bautar Ɗanmaraƙin Bani Isra'ila•Ƙissar Khidir Da Musa•Wuri Mai Albarka•Maganar Allah Tare da Musa |
| Mabiya | Asiya Matar Fir'auna•Muminu Ale Fir'auna•Yahudawa |
| Masu Adawa | Fir'auna•Samiri |
Musa, (Larabci: النبي موسى عليه السلام) ya kasance ɗaya daga cikin Annabawa Ulul Azmi ma'abocin shari'a kuma shugaban Banu Isra'il. Haƙiƙa ƙissoshi da labarai da mu'ujizozin Annabi Musa sun kasance a cikin Kur'ani fiye da na sauran annabawa. Ɗaya daga cikin laƙubbansa na asali shi ne Kalimullahi, ya samu wannan laƙabi ne sakamakon Allah ya yi magana da shi kai tsaye ba tare da wani shamaki a tsakaninsu ba.
Sashe daga ƙissoshin Kur'ani game da Musa sune kamar haka: rakiya da ya yi wa ɗaya daga cikin waliyyan Allah, bisa abin da ya zo a riwayoyin Shi'a ya kasance Khidir da kuma ƙissar wurga Musa cikin kogi. Bisa ƙissa ta ƙarshe, mahaifiyar Musa sakamakon tsoron kashe mata ɗa da sojojin Fir'auna ka iya yi, sai ta sanya shi cikin akwatu ta jefa shi cikin kogi, wannan akwatu ta dinga yawo cikin ruwa har Musa ya isa fadar Fir'auna, Musa ya taso ya girma a cikin fadar Fir'auna. Labarin rikici da ya kaure tsakanin Musa da wani Baƙibɗe yana daga cikin sauran ƙissoshin Kur'ani wanɗada bisa abin da ya zo cikinsu an kashe wani Baƙibɗe kuma saboda hakan ne Musa ya gudu daga Misra ya tafi Madyana.
Annabi Musa (A.S) ya auri ɗiyar Annabi Shu'aibu a Madyana, ya biya sadakinta da yin kiwo na shekara goma, bayan ya cika shekaru 40 ne ya fara karɓar wahayi a garin Ɗur aka aiko masa da annabta, tare da karɓo koyarwa da uamrnonin ubangiji waɗanda daga jumla akwai tauhidi, lazimtar bautawa Allah, yin sallah da batun mas'alar Ma'ad (Ranar tashin alƙiyama). Musa tare da rakiyar ɗan uwansa Haruna ya je wurin Fir'auna ya nemi ya saki Banu Isra'il; amma Fir'auna duk da cewa ƙarara a fili ya ga mujizozzi daga Musa bai gasgata da'awar Musa ba sai ya ci gaba da azabtar da Banu Isra'il. Musa bisa umarnin ubangiji, ya samu nasarar tafiya tare da Banu Isra'il kuma cikin taimakon mujiza ya tsaga teku gida biyu ya fice daga Misra. Cikin Kur'ani da riwayoyi an naƙalto wasu mujizozi na daban da Musa ya kasance tare da su; daga jumla akwai canja sanda zuwa Maciji da kuma farin hannu.
Ƴanshi'a sun yi imani cewa baki ɗayan annabawa har da Musa tun daga haihuwa har zuwa ƙarshen rayuwa sun kasance Ma'asumai; amma wasu daga malaman tafsiri na Ahlus-Sunna tare da jingina da ba'arin wasu abubuwa da suka faru a lokacin rayuwar Musa waɗanda aka ambace su a Kur'ani, daga jumla kashe Baƙibɗe da wurgi da allo cikin fushi, sun yi shakku kan kasancewarsa Ma'asumi. Malaman tafsiri na Shi'a tare da bayanin shaidu sun yi ƙarin bayani da cewa waɗannan abubuwa ba su da ma'anar raddi da watsi da ma'asumancin Sayyidina Musa.
Musa Mafi Girman Annabi Cikin Bani Isra'il
Musa Bin Imran[1] ya kasance mafi girman annabin cikin Bani Isra'il kuma shugabansu[2] wanda ya ƴantar da su daga hannun mutanen Misra ya kawo su ƙasar da aka yi musu alƙawari.[3]
Sayyidina Musa (A.S) ya kasance ɗaya daga cikin annabawa biyar Ulul Azmi,[4] ma'ana wanda aka baiwa shari'a,[5] sunansa ya zo har sau 136 cikin Kur'ani[6] haka kuma an naƙalto mujizozinsa masu yawa cikin Kur'ani.[7] Ƙissoshin Musa sun zarce na sauran annabawa a cikin Kur'ani.[8] Haƙiƙa Musa ya kasance siriki ga Annabi Shu'aibu (A.S).[9] Sayyidina Yusha'u ne ya kasance wasiyyi da magajin Musa (A.S).[10]
Kur'ani ya bayyana Musa a matsayin annabi kuma manzo.[11] Sakamakon saƙo da aka aiko shi da shi da kuma magana da ya yi da Allah ya samu fifiko kan al'ummarsa[12] an baiwa Musa Alluna[13] da Attaura.[14] Kuma ya kasance ma'abocin littafi daga sama da shari'a[15] Haƙiƙa shari'ar da aka bawa Musa ta kasance mafi kusanci da Muslunci daga sauran addinai.[16]
«وَاذْکرْ فِی الْکتَابِ مُوسَی إِنَّهُ کانَ مُخْلَصًا وَکانَ رَسُولًا نَّبِیا...وَقَرَّبْنَاهُ
Ka ambata a cikin Littafin Musa. Lallai shi mutum ne da aka tsarkake, kuma Manzo ne, Annabi. Mun kusanto da shi yana mai ganawa da mu.
A cewar Muhammad Husaini Fadlullahi daga malaman shi'a, saƙon Sayyidina Musa bai iyakantu da wasu jama'a ko wani wuri ba, bari dai saƙo ne na duk duniya;[18] Amma wasu masana bisa dogara da ayoyin Kur'ani da Attaura sun yi amanna da cewa addini yahudu da littafin Attaura kaɗai yana magana ne da mutanen Bani Isra'il (Ƴaƴan Yaƙub) bai shafi sauran al'ummu ba.[19]
Maganar Da Musa Ya Yi Tare da Ubangiji
Siffar "Kalimullah" wace take da ma'anar mutumin da ya yi magana tare da Allah, siffa ce da ta keɓanta da Musa.[20] Na'am wasu masana sun yi imani cewa a lokacin da Annabin Muslunci (S.A.W) ya je Mi'iraj shi ma kai tsaye ya yi magana da Allah.[21]
Allah ta'ala ya yi magana kai tsaye tare da Musa.[22] Nasir Makarim Shirazi ya tafi kan cewa Allah yana halittar wasu igiyoyin sauti cikin sararin samaniya ko kuma wani jiki, to ta haka ne ake magana da shi.[23] Kishiyar wannan magana, Sayyid Muhammad Husaini Ɗabaɗaba'i ya yi imani cewa Allah bai yi bayanin yadda yake magana da bayinsa ba, saboda haka ba zamu iya fahimtar yadda yake maganar ba daga ayoyin Kur'ani.[24] A cewarsa, maganar Allah tare da Musa ta kasance tare da tsani ko samaki ba[25] al'amari na gaske, kuma duk da cewa yana da tasiri na yau da kullun amma bai buƙaci sasanni da gaɓɓai na zahiri kamar misalin baki ba.[26]
Tarihin Rayuwa
Annabi Musa (A.S) ɗan Imran, ya kasance daga zuriyar Lawi Bin Yaƙub.[27] Sunan babansa a Attaura Imram, wanda a karin harshen Larabci suke kiransa da Imran, musulmi suma suna kiransa da Imran.[28] Haihuwar Musa (A.S) ta kasance da nisan shekaru 250 daga wafatin Annabi Ibrahim (A.S).[29] Mas'udi a cikin Isbatul Wasiyya, ya ce nisan da yake tsakanin Musa da Ibrahim (A.S) ya kai shekaru 468.[30]
Haihuwar Musa (A.S) ta zo daidai da lokacin da Fir'auna ya ba da umarni kashe duk wani jariri namiji da aka haifa da kuma kame jarirai mata cikin Bani Isra'il.[31] Kan asasin Attaura, Fir'auna sakamakon tsoro da yake ji na Bani Isra'il ka iya ƙwace masa mulki da haɗa kai da maƙiyansa, sai ya ba da umarnin kashe ƴaƴansu maza.[32] Nasir Makarim Shirazi, daga malaman tafsiri na Shi'a, ya yi imani kan asasin ayoyin Kur'ani, haƙiƙa Fir'auna domin raunana Bani Isra'il ya ba da umarnin kashe ƴaƴansu maza.[33] Wasu suna cewa dalilin fitar wannan umarni wani mafarki ne da Fir'auna ya yi wanda cikinsa ya ga wata wuta tana tunkaro ƙasar Misra, tana ta kashe Misrawa amma ba ta shafar Bani Isra'il.[34] A wani naƙalin, Fir'auna a cikin mafarki ya ga an haifi wani yaro daga Bani Isra'il da zai rusa masa mulki.[35]
Haihuwa Ƙuruciya Zuwa Guduwa Daga Misra
Kan asasin ayoyin Kur'ani, bayan haihuwar Annabi Musa (A.S) ubangiji ya yi wahayi ga mahaifiyarsa[36] ya umarce ta da ta baiwa ɗanta nono, kuma idan ta fuskanci barazana ga rayuwarsa[37] ta sanya cikin akwatu[38] ta jefa shi cikin kogi ka da ta damu ka da ta ji tsoro[39]
Mahaifiyar Musa bayan shayar da shi nono (Bisa abin da ya zo a Attaura ta shayar da shi nono wata uku[40]) sakamakon tsoron faruwar hatsarin da take tsammani, sai ta sa Musa cikin akwatu ta jefa shi cikin kogi.[41] Ta aika ƴarta ta bi bayan wannan akwatu.[42] Allah domin kawar da damuwar da take ciki sai ya ba ta ƙarfin zuciya[43] Ya yi mata alƙawarin zai dawo da shi gare ta kuma zai sanya shi annabi cikin annabawansa.[44]
Wani mutum daga dangin Fir'auna ya ɗauko Musa daga cikin kogi.[45] Amma Attaura ta bayyana cewa ɗiyar Fir'auna ce ta ɗauko Musa daga kogi.[46] Kan asasin Kur'ani, matar Fir'auna (Asiya[47]) ta kira Musa matsayin hasken idanunta da Fir'auna ta kuma yi fatan cewa nan gaba zai amfanar da Fir'auna kai hatta ma ta yiwu Fir'auna ya riƙe shi matsayin ɗa a gare shi.[48]
Bayan Musa ya tsira daga kogi, sai yaƙi karɓar nono duk wata mata da aka kawo ta shayar da shi, har zuwa lokacin da ƴar uwar Musa ta ba da shawara, aka kawo babarsa matsayin mai shayarwa da za ta shayar da shi, da haka ne Allah ya dawo da Musa wurin mahaifiyarsa.[49] Nasir Makarim Shirazi tare da jingina da ayoyin Kur'ani ya yi imani cewa Musa ya taso ne a gida tare da mahaifiyarsa a wasu lokuta ana ɗaukarsa a kai shi wurin matar Fir'auna.[50] Makarim Shirazi ya amfana daga magaanar da Fir'auna ya yi zuwa ga Musa (Ashe kai ɗin nan ba mu rene ka ba tun kana yaro ƙarami a wurinmu ?)[51] ya fitar da ma'anar cewa Musa aƙalla ya zauna a fadar Fir'auna na ɗan wani lokaci.[52] kan asasin Attaura Musa a lokacin yarintarsa ya kasance ne tare da babarsa sai da ya girma ne ya je fadar Fir'auna.[53]
An ce Musa ya samu wanna suna ne ta fuskacin ciro shi9 daga ruwa da bishiya. "Mu" a harshen ƙibɗanci yana nufin ruwa "Sa" kuma tana nufin bishiya.[54]
Shekarun girman Musa a lokacin da rikici ya faru tsakanin wani mutum daga Bani Isra'il da wani Bamisre Baƙibɗe, bayan Musa ya kai naushi da hannu sai ya kashe wannan Bamisre.[55] Bayan faruwar wannan waƙi'a ne sai ma'aikatan Fir'auna suka ɗauri aniyar kashe Musa[56] domin tseratar da ransa sai ya gudu daga Misra.[57]

Rayuwa A Madyana, Annabta Da Kuma Dawowa Misra
Bayan rikici da Musa ya yi da Baƙibɗe da kashe shi, domin tsira daga hannun jami'an tsaron Fir'auna sai ya gudu zuwa Madyana.[58]A can ne ya haɗu da wasu ƴanmata guda biyu Safra'u da Liya[59] da ya taimaka musu cikin shayar da dabbobinsu ruwa.[60] Mahaifin waɗanan ƴanmata guda shi ne Annabi Shu'aibu,[61] bayan samun labarin Musa da ya yi sai ya kira shi[62] ya shawarce shi da aiki da kuma aura masa ɗaya daga cikin ƴaƴansa.[63]
Musa ya zauna a Madyana tare da aurar ɗiyar Shu'aibu da kuma yi masa kiwo.[64] Bisa abin da ya zo a Kur'ani da tafsiran Shi'a, Musa ya yi kiwo na shekara goma a Madyana, ya rayu tare da Shu'aibu yana masa kiwo.[65] Bayan nan, a kan hayarsa ta dawowa Misra, cikin dare yana tare da iyalansa sai hanya ta ɓace masa,[66] can sai ya hango wata wuta daga ɓangaren Ɗur sai ya tafi wurin wannan wuta domin nemo labari ko kuma tsono wannan wuta domin iyalansa su ji ɗimi.[67] Bayan Musa ya je kusa da wannan wuta, sai ya ji wani ƙarar wani sauti: "Ya Musa Ni ne Allah, ubangijin talikai."[68] "Ni kaɗai zaka bautawa ka yi sallah domin tunawa da ni."[69]
Musa a Ɗur sina, aka zaɓe shi annabi[70] Allah ya umarce shi ya jefa sandarsa[71] Sai ya jefa sandar, kwatsam sai wannan sanda ta jirkice zuwa Maciji.[72] Allah ya ce masa ka da ya ji tsoro ya ɗauki wannan sanda, wannan sanda za ta koma yadda take a farko;[73] Haka kuma ya ba shi umarni ya saka hannunsa cikin wuyan rigarsa, sai hannun ya zama fari yana haskaka.[74]] An yi la'akari da waɗannan mujizozi da Musa ya yi a dutsen Ɗur a matsayin shiri da tanadi domin maimaita su a fadar Fir'auna.[75]
Fara Da'awa Zuwa Fitar Da Bani Isra'il Daga Misra
Bisa abin da ya zo a Kur'ani, Allah ya aika da Musa zuwa ga mutanen Fir'auna.[76] Sai Musa ya ce Allah ni dai ina jin tsoro ka da su ƙaryata ni[77] Musa ya bayyana cewa ba zai iya jurewa ƙaryatarsu ba.[78] Harshensa bai iya magana[79] Mutanen Fir'auna suna zargin Musa da aika lefin kashe Baƙibɗe.[80] Musa ya roƙi Allah ya sanya Haruna matsayin manzo gare shi da zai taimaka masa.[81] Musa ya je wurin Fir'auna tare da rakiyar Haruna[81] Ya buƙaci Fir'auna ya saki Bani Isra'il.[82]
Musa ya nuna Fir'auna da mutanen da suke tare da Fir'auna mu'ujizozi, daga ciikinsu akwai jirikicewar sanda zuwa maciji da farin hannu domin su gasgata maganarsa[83] Amma Fir'auna sai ya tuhumi Musa da aikata tsafi.[84] Daga ƙarshe dai Fir'auna ya shirya majalisi da zai haɗa Musa da matsafa don su kunya ta shi. Bayan hallarar matsafa da Musa a wannan majalisi sai Musa ya lalata tsafi da sihiri da matsafan da Fir'auna ya gayyato suka yi, daga ƙarshe dai wannan matsafa suka yi imani.[84] Tare da haka, Fir'auna bai sallamawa Musa da buƙatunsa ba, sai Allah ya saukar da bala'o'i kan Misrawa.[85] Allah ya umarci Musa cikin dare shi da Bani Isra'il su fita daga cikin Misra.[86] Bayan ficewar Bani Isra'il daga Misra, sai Fir'auna tare da sojojinsa suka bi bayansu.[87] Bani Isra'il sun tsinci kansu cikin halin kewaye su, a gefu guda teku a ɗayan gefan kuma Fir'auna da sojojinsa.[88] Annabi Musa (A.S), bisa umarnin Allah ya buga sandarsa kan ruwa sai hanya wannan ruwa ya rabe gida biyu.[89] Bani Isra'il suka tsira;[90] Shi kuma Fir'auna da mutanensa suka nutse cikin wannan ruwa.[91]
- Kuma Ku Duba : Muminu Ale Fir'auna da Ƙetarar Da Bani Isra'ila Daga Teku
Hijira Zuwa Ƙasar Da Aka Yi Alƙawari
Bayan gajeran lokaci daga tsira daga Misra, Annabi Musa ya tafi ganawa da ubangiji.[92] Bani Isra'il a lokacin da Musa ya fita, sun sassaƙa wani ɗanmaraƙi na zinariya suka dinga bauta masa.[93] Lokaci da Musa ya dawo ya same su suna bautawa ɗanmaraƙi, cikin fushi ya yi wurgi da allauna biyu da aka saukar masa a dutsen Ɗur Sina kan ƙasa ya karya su.[94] Haka kuma Allah ya zargi Bani Isra'il.[95] Annabi Musa tare da zaɓaɓɓun mutane guda saba'in daga Bani Isra'il ya tafi ganawa da ubangiji.[96][Tsokaci 1] Ba'ari daga cikinsu sun sanyawa Musa sharaɗi cewa ba za su imani ba sai sun ga Allah da idanunsu.[97]
Domin bayyanar da gazawarsu daga ganin Allah, sai walƙiya ta sauka kan dutse sai baki ɗayansu suka faɗi matattu sakamakon walƙiya da ƙarar sauti mai ban tsoro.[98] Wasu masana suna ganin wannan walƙiya azaba ce daga ubangiji.[99] Sai Musa (A.S) ya cewa Allah : "Shin zaka halaka mu saboda da aikin da wawayen cikinmu"[100] Ya roƙi Allah ya sake raya su, Allah ya karɓi addu'ar Musa ya tashe su a raye bayan kashe su.[101]

Rashin Matsuni Da Jeji
Bayan halakar da Fir'auna, Banu Isra'il a kan hanyarsu ta zuwa ƙasar mai tsarki (A cewar wasu Sham)[102] wace aka musu alƙawari, sun isa wurin wasu ƙarfafan mutane wanda ya zama wajibi su yaƙe su.[103] Bani Isra'il sai suka gujewa yaƙi da wannan mutane suka gayawa Musa cewa kai da ubangijinka ku je ku yi yaƙi da wannan mutanen mu muna nan a zaune babu inda za mu motsa.[104] Sai Allah ya haramta musu shiga ƙasa mai tsarki har tsawon shekaru 40.[105] Ya musu azaba da rayuwa cikin rashin matsuguni har tsawon shekaru 40.[106] A lokacin ɗimuwa da rashin matsuguni, matsaloli masu yawa sun faru da Bani Isra'il, wanda daga ƙarshe Allah ya warware musu.[107] Allah ya sanya gajimare ya zama inuwa a gare su[108] kuma domin kawar da yunwa daga cikinsu sai ya aiko musu da "Mannu da Salwa"[109]
Kan asasin ayoyin Kur'ani, Musa (A.S) ya roƙi Allah ruwa domin Bani Isra'il, sai Allah ya ce masa ya buga sandarsa kan dutse, bayan buga sandarsa sai idaniyar ruwa goma sha biyu ta buɗe kamar dai adadin ƙabilun Bani Isra'il, ruwa ya kwarara daga kan wannan dutse, ko wace ƙabilu ta samu idaniyar ruwa guda ɗaya.[110]
Wasu masana suna ganin wannan ƙissa da mu'ujizar Musa (A.S) sun faru ne a lokacin ɗimuwa da rashin matsuguni a jeji[111] Wasu kuma suna gani sun faru kafin ɗimuwa da rashin matsuguni.[112] An ce labarin neman ganin Allah, da nutsewar Ƙaruna cikin ƙasa, bautar ɗanmaraƙi, saniyar Bani Isra'il, saukar da alluna da tsaga dutse baki ɗayan waɗannan abubuwa sun faru ne a lokacin rashin matsugunin Musa da mabiyansa.[113]
Wafati
Annabi Musa (A.S) ya yi wafati a lokacin rashin matsuguni a jeji[114] yana da shekaru 120[115] ko 126.[116] Bisa abin da ya zo a wata riwaya daga Annabi (S.A.W) Musa ya rayu har shekara 126,[117] Kuma ya yi wafati bayan fiye da ƙarni 17 kafin haihuwar Almasihu.[118] Bisa abin da ya zo a wasu riwayoyin, kabarinsa ya kasance a ɓoye.[119]
Annabta
An baiwa Sayyidina Musa (A.S) annabta a lokacin da ya cika shekaru 40,[120] a Ɗur Sina[121] an fara saukar masa da wahayi lokaci da yake jikin wata bishiya[122] anan ne aka zaɓe shi annabi.[123] Haƙiƙa Musa ya kasance daga annabawa Ulul Azmi.[124] Wasu malaman tafsiri kan asasin ayar Kur'ani "Ni ne na zaɓe ka domin saƙo"[125] sun yi imani cewa a wannan waje ne da wannan kalma aka aiko shi annabi.[126] Bayan zaɓarsa annabi sai Allah ya bashi wasu umarnoni kamar haka:
- Da farko ya fara da tauhidi[127]: "Ya Musa ni ne Allah, ubangijin talikai"[128]
- Bayan nan sai Allah ya umarce shi da bauta masa.[129]
- Ya umarce shi da yin sallah domin tunawa da Allah.[130]
- Sai kuma bayanin batun Ma'ad (Ranar tashin alƙiyama).[131]
Umarnoni Guda Goma Da Attaura
Umarnoni Guda Goma:'
- Ni ne ubangiji, kuma Allanka
- Ka da yi wa kanka wasu alloli koma bayana
- Ka da ka yi amfani da suna na a wurin da bai dace ba
- Ka tuna da ranar Asaban kuma ka tsarkake ta
- Ka girmama mahaifanka
- Ka da ka aikata kisa
- Ka ka yi zina
- Ka da ka yi sata
- Ka ka yi ƙarya
- Ka da ka yi kwaɗayi cikin dukiya wani da matan wani
Baya Umarnoni goma waɗanda suka kasance rubuce a kan alluna an saukar da su ga Musa (A.S).[132] abin nufi da Attaura sune litattafai guda biyar na Musa (A.S). Yahudawa suna la'akari da waɗannan litattafai matsayin wahayin da aka saukarwa da Musa (A.S).[133] Waɗannan litattafai (Asfar) sun haɗa da littafin halitta (Genesis), Fita (Exodus), Lawiyawa (Leviticicus, Adadi (Numbers), da Tasniya (Deuteronomy).[134] Na'am wani lokaci Attaura tana nufin duk wani tsarkakakken littafin Yahudawa.[135] Musulmi sun yi imani da cewa Attaura da take hannun Yahudawa a yau an jirkita ta.[136]
Shari'a
Malaman tafsiri bisa la'akari da wasu ayoyin Kur'ani, sun tabbatar da kasancewar Musa (A.S) daga annabawa wanda aka ba shi littafi da shari'a.[137] Shari'a a keɓantacciyar ma'ana tana nufin ladubba da dokoki wanda Allah ya saukarwa da bayinsa da suka haɗa da hukunce-hukuncen fiƙihu da kyawawan halaye.[138]
Shari'a A Cikin Kur'ani
Malaman tafsiri, tare da la'akari da shari'ar sayyidina Musa (A.S) sun dogara da rukuni uku daga ayoyin Kur'ani[139]
- Rukunin ayoyin[140] da suka yi bayanin aika Musa wurin Fir'auna da Ƙibɗawa.[141]
- Rukuni daban da yake nuni kan cewa aika Musa wurin Bani Isr'ail ya kasance ne tare da littafi.[142] Ba'arin malaman tafsiri sun bayyana cewa abin nufi daga (Littafi) a wannan aya ya kasance Attaura[143] wace daɗi kan tauhidi da take tattare da shi[144] ta tattaro umarnoni da hani da shari'ar sayyidina Musa (A.S) ga mutanen Bani Isra'il.[145]
- Ba'ari daban daga Attaura yana nuni kan gamewar da'awar Musa (A.S)[146] da kuma ingancin shari'arsa, bawai kaɗai ta iyakantu ne da Bani Isr'ail ba, bari dai shari'a ce ga dukkanin mutanen duniya.[147]
Shari'ar Musa A Cikin Attaura
Bisa bayanin ba'arin masana, haƙiƙa shari'ar Musa ta haɗo hukunce-hukuncen shari'a guda 613.[148] Daga ciki akwai 248 da suka kasance wajibai da kuma hukunce-hukunce 365 da suka shafi abubuwan da shari'a ta haramta.[149] Daga cikin madogarai na jigo a wurin Yahudawa da suke ciro ladubba da hukunce-hukuncen shari'arsu daga ciki, shi ne hukunce-hukuncen Musa (A.S) da suka zo a Attaura, musamman a cikin litattafai guda uku, Lawiyawa, adadi da tasiniya daga Asfar guda biyar na Attaura:[150]
- .Littafin Lawiyawa (Sifri na uku daga Asfar biyar na Attaura)ya haɗo dokoki da hukunce-hukunce da layya da hadayoyinsu.[151] Haka kuma dokoki da hukunce-hukunce da suka shafi dabbobi da namansu ya halasta da waɗanda ya haramta,[152] ɗahara da najasa,[153] kaffarar zunubai,[154] lefukan jima'i misalin zina da uƙubar zunubai,[155] dokokin bukukuwa masu tsarki,[156] hukunce-hukuncen waƙafi[157] duka an yi bayaninsu a cikin wannan littafi.
- .A cikin littafin adadi (Sifri na huɗu daga Asfar guda biyar na Attaura) ba'arin hukunce-hukunce suna magana ne kan mata da suka fuskanci munana zato daga mazajensu,[158] hukunce-hukunce da suka shafi haramcin kisa da uƙubar da aka tana da kan aikata kisa,[159]dokokin bakance,[160] dokokin layya,[161] wajiban zunuban Lawiyyawa,[162] karkasa ganimomi duka sun zo cikin wannan littafi.[163]
- .Cikin littafin tasniya (Sifri na ƙarshe daga Asfar guda biyar na Attaura) waɗannan hukunce-hukunce da aka yi bayaninsu sune: umarnoni goma,[164] ayyana alƙalai domin warware riginginmu,[165] ba da shaida a kotu[166] dokoki da hukunce-hukuncen yaƙi,[167] hukunce-hukuncen aure.[168]
Mujizozi
Kan asasin aya ta 101 suratul isra'i da aya ta 12 suratul namli, sayyidina Musa (A.S) ya kasance tare da alamomi tara daga mujizozi. Malaman tafsiri sun yi saɓani game da wane abubuwa ne suka kasance mujizozi guda tara.[169]170] A ra'ayin Allama Ɗabaɗaba'i da Makarim Shirazi waɗannan mujizozi sun kasancJjirkiwar sanda zuwa ƙaton maciji, farin hannu (Ƙyallin hannu) aiko da ambaliyar ruwa, ƙwaron fara, kwaɗi, kwarkwata, jarrabtuwa da jini, da fari da ɗaukewar ruwan sama da kuma ƙarancin kayan marmari.[170] Waɗannan mujizozi guda tara, sune mujizozi na Musa (A.S) da ya jewa Fir'auna da su, amma mujizozin nasa sun wuce guda tara.[171]
Cikin Kura'ni an yi maganar mujizozi guda goma sha shida na Annabi Musa (A.S), ba'arin mujizozinsa da suka zo cikin adadin ayoyi daban-daban sune: Tsaga kogi gida biyu ya zo cikin ayoyi 17,[172] Canja sanda zuwa ƙaton maciji a cikin ayoyi guda 8[173] Ƙyallin hannu a cikin ayoyi biyar,[174] Shimfiɗa dutse a saman kawunan Bani Isra'il a cikin ayoyi huɗu,[175] saukar tsawa kan Bani Isra'il cikin ayoyi uku[176] da kuma saukar da mannu sa salwa (Abinci) ga Bani Isra'il a cikin ayoyi uku,[177] sauran mujizozinsa sun kasance: amfani da gajimare da ma'anar inuwa,[178] jarrabtar mutane da juyar da ruwan kogin Nil zuwa jini da zubar jini daga hanci (Haɓo),[179] fari na ƙamfar ruwa sama,[180] aiko da ɗufana (Ambaliyar ruwa)[181] ƙwaron Fara[182] Kwarkwata[183] da kwaɗo,[184] da kuma raya wani mutum da aka kashe daga Bani Isra'il.[185]
Jirkitar Sanda Zuwa Maciji
Mujizar jirkitar sandar Musa zuwa maciji, ta zo cikin surori biyar da ayoyi takwas.[186] bisa abin da ya zo cikin Kur'ani, sanar Musa ta jirkita zuwa maciji a wurare uku:
- .Jirkitar sanda zuwa maciji a kan dutsen Ɗur: Bisa abin da ya zo cikin surori uku, Ƙasas, Namli da Ɗaha,[187] Sandar Annabi Musa bayan ya wurga ta kan ƙasa,[188] ta koma ƙaton maciji.[189]
- .Jirkitar sanda zuwa ƙaton Maciji a gaban Fir'auna: Bisa abin da ya zo da ayoyin Kur'ani, lokacin da Musa ya je wurin Fir'auna domin kiransa zuwa hanyar gaskiya, Fir'auna ya nemi musa ya kawo shaidu da suke tabbatar da gaskiyar da'awarsa, sai Musa ya jefa sandar da take hannun ƙasa, sai ta jirkice ta zama Maciji.[190]
- .Jirkitar sanda zuwa Maciji a gaban matsafan Fir'auna: Kan asasin abin da ya zo a surorin Shu'ara, A'araf da Ɗaha, bayan Musa ya canja sandarsa zuwa Maciji a gaban Fir'auna[191] kuma ya amsa buƙatar Fir'auna ta yin musabaƙa tare da matsafan da ya gayyata, sai Musa ya wurga sandarsa ƙasa sai wannan sanda ta jirkice ta zama Maciji kuma ta haɗiye baki ɗayan igiyoyin da matsafa waɗanda suka bayyana a macizai.[192] Daga ƙarshe dai waɗannan masu sihiri da Fir'auna ya gayyato bayan ganin ayoyi da Musa ya nuna sai suka yi imani[193] Sai dai cewa duk da Fir'auna bai miƙa wuya ba, sai ya zarge su da haɗa baki da Musa.[194]
Yadul Baida (Hannu Mai Haskaka)
Mujizar yadul baida, malaman tafsiri daga cikinsu Sayyid Abdullahi Shubbar[195] da Fadlu Bin Hassan Ɗabrisi[196] sun fassara ta da hannu mai haskaka, amma sauran malaman tafsiri kamar Shaik Ɗusi[197] da Muhammad Jawad Mugniyya[198] sun fassara ta da farin hannu, daga cikin mujizozi guda tara na sayyidina Musa (A.S) da ambatonsu ya zo a Kur'ani.[199] An ambaci wannan mujiza cikin surorin A'araf, Ɗaha, Shu'ara, Namlu da Ƙasas.[200] Bisa ayoyin Kur'ani, wannan mu'ujizozi ta faru ne sau ɗaya, kafin tafiyar Musa ganawa tare da Fir'auna da kuma shiri da tanadin Musa[201] ta kuma ƙara faruwa a gaban Fir'auna.[202]
Raba Teku Gida Biyu
Bisa abin da ya zo a aya ta 50 suratul baƙara, Allah ta'ala ya raba teku gida biyu domin Bani Isra'il ya kuma tseratar da su, a gefe guda kuma ya halakar da Fir'auna da mutanensa.[203] Cikin wannan aya samsam ba yi bayanin yadda tekun ya dare gida biyu ba; amma a aya ta 63 suratul Shu'ara ya zo cewa Allah ya yi wahayi ga Musa ya ce masa ya doka sandarsa kan teku, sai Musa ya zartar da wannan umarni, sai teku ya rabe gida biyu bayan doka sanda kansa.[204] Haka nan cikin wata ayar daban, an yi ishara kan nutsewar Fir'auna.[205]
Ƙissar Musa Tare da Khidir
Samfuri:Main:Ƙissar Musa Tare da Khidir Labarin Musa da Khidir wata ƙissa ce ta Kur'ani game da haɗuwa da rakiyar da Musa (A.S) ya yi wa Khidir a wata tafiya da suka yi.[206] Cikin wannan ƙissa Musa (A.S) bayan haɗuwa da wani mutum wanda cikin Kur'ani aka kira shi da "Bawa daga bayin Allah wanda da aka ba shi rahama da ilimi" sai Musa ya nemi yi masa rakiya da kuma koyan ilimi daga gare shi.[207] A cikin riwayoyin Shi'a, an bayyana wannan mutimi da Khidir (A.S).[208]
Wannan rakiya ta kasance bisa roƙo da dagewar Musa (A.S).[209] Da farko Khidir bai lamunta Musa ya raka shi ba, amma daga baya sai ya gindaya masa sharuɗɗa da cewa Musa ba zai tambaye shi kan duk wani abu da ya gani daga gare shi ba.[210] Cikin wannan tafiya, Khidir ya aikata abubuwa guda uku: Huda wani jirgin ruwa,[211] Kashe wani matashi[212] da sabunta ginin wani bango.[213] Musa (A.S) cikin duk wurare guda ukun sai da ya nuna rashin amincewarsa[214] da wannan dalili ne suka raba hanya da juna.[215] Khidir a ƙarshe, ya yi bayani dalilin aikata abubuwa uku da ya yi[216] Wannan ƙissa ta zo sau ɗaya a cikin Kur'ani, akwai muhawara tsakanin malaman tafsiri, malaman aƙida da sufaye game da wannan batu.[217]
Ismar Musa
- Ku Duba: Ismar Annabawa
Bisa abin da Sayyid Murtada ya faɗa, Shi'a saɓanin Ahlus-Sunna, sun yi imani da cewa baki ɗayan Annabawa tun daga haihuwarsu har ƙarshen rayuwa su ma'asumai ne ba sa aikata ko wane irin zunubi.[218]
Kashe Baƙibɗe
Kashe Baƙibɗe, magana ce kan wani rikici da ya faru tsakanin wani Baƙibɗe tare da wani mutum daga Bani Isra'il wanda daga ƙarshe wannan Baƙibɗe ya rasa ransa ta hannun Musa (A.S).[219] Bayanin wannan ƙissa ya zo a aya ta 15 suratul ƙasas.[220] Ba'arin masana sun yi imani cewa kashe Baƙibɗe ba ya dacewa da ma'asumancin Musa (A.S)[221] Sun kafa hujja da wannan dalilai kamar haka:
- Idan Baƙibɗe dama can ya cancanci a kashe shi, to me yasa a aya ta 15 suratul ƙasas, Musa (A.S) bayan kashe shi ya ce: "Wannan aiki yana daga aikin Shaiɗan".[222] Kuma a cikin aya da ta zo a bayanta ya ce: "Ya Allah na zalunci kaina ka gafarta mini";[223] Haka kuma a aya ta 20 suratul Shu'ara ya ce: "Na aika wannan aiki ne a lokacin da bani da labari"?[224]
- Idan kuma Baƙibɗe bai cancanci kisa ba, to kenan Annabi Musa (A.S) ya kashe wanda bashi da lefi ya kuma aikata lefi kenan, wanda hakan ba ya dacewa da kasancewarsa ma'asumi.
Kishiyar wannan ra'ayi, wasu daga malaman tafsiri sun yi imani da cewa wannan Baƙibɗe dama can ya cancanci kisa, kuma kashe shi ba za a lissafa shi a lefi ba; na'am zai fi kyawu ace ya jinkirta kashe shi; saboda kashe shi da ya yi ya jawo masa wahala da tilasta masa ficewa daga Misra, waɗannan malamai suna ganin aikin da Musa ya yi yana daga jinsin aikin da ake kira da Tarkul Aula (Barin abin da ya fi dacewa) kuma suna cewa neman gafara da ya yi shima ya kasance daga barin Tarkul Aula.[225]
Ba'arin malaman tafsiri na Ahlus-Sunna, sun tafi kan cewa kashe Baƙibɗe ya kasance kisa na kuskure kuma shi kisa na kuskure yana cikin ƙananan zunubai, Musa (A.S) ya yi istigfari ne saboda aikaƙata ƙaramin zunubi.[226]
Wurgar Da Alluna Cikin Fushi
Daga cikin abubuwa da ake la'akari da su matsayin cin karo da kasancewar Musa (A.S) ma'asumi shi ne martaninsa lokacin da ya sami Banu Isra'il suna bautar ɗanmaraƙi bayan dawowarsa daga dutsen Ɗur.[227] A cikin aya ta 150 suratul a'araf ya zo cewa yayin da Musa ya dawowa wurin mutanensa daga dutsen Ɗur kwatsam sai ya same su suna bautar ɗanmaraƙi, cikin fushi sai ya wurgar da allunan da suke hannun ƙasa, ya kama gashin kan ɗan uwansa ya jawo shi gare shi.[228] Wannan labari ya zo hatta cikin Attaura kamar haka "Yayin da Musa ya dawo sansanin Bani isra'il sai ya same su suna rawa suna bautawa ɗanmaraƙi, sai hakan ya fusata shi ya jefar da allunan da suke hannunsa ƙasa suka kakkarye".[229]
Amsoshi kan wannan batu sun kasance kamar haka:
- Fadlu Bin Hassan Ɗabrisi marubucin tafsirin Majma'ul Bayan ya tafi kan ra'ayin cewa Musa (A.S) cikin wannan mataki da ya ɗauka yana so ya nuna cewa abin da suka yi abu ne mai tsananin munnan da fusatarwa, kuma da wannan salo ne zai fahimtar da su irin munin da aikinsu yake da shi, domin nan gaba ka da su sake maimaita wannan kuskure, saboda haka abin da ya yi ba ya cin karo da kasancewarsa ma'asumi.[230]
- Allama Ɗabaɗaba'i, saɓanin da ya faru tsakanin Musa da Haruna ba wani abu da za a kalle shi matsayin abin da bai dace ba, malamin ya kafa hujja da cewa shi wannan saɓani ba saɓani da ya kai ya kawo ba, saɓani ne da ya faru daga bambancin ra'ayi da matafiya da kuma isma, kaɗai ya keɓantu ne da umarnoni na Allah.[231]
- Bisa abin da Zamakhshari ya faɗa malamin tafsiri Ahlus-Sunna, fushin da Musa (A.S) ya yi a wannan wuri ya kasance ne domin Allah da kuma kishin addini.[232]
Ba'arin masana sun tafi kan ra'ayin cewa a Attaura ta yau da take hannun mutane, bawai kaɗai ba ta yi magana kan ismar Musa (A.S) ba, a a bari ma dai tama naƙalto ayyukan saɓo ta jinginawa annabawa musamman ma Musa (A.S)[233] kuma wannan ayyuka sam ba sa dacewa da kasancewarsu ma'asumai.[234] Wasu kuma suna ganin cewa amfani da kalmar adalci a wasu wurare cikin Attauara kamar "Ya Nuhu"” kai da iyalanka ku shiga cikin jirgin ruwa, saboda na sameka a wannan zamani a gabana matsayin adali[235] matsayin hujja kan isma da tsarkakar annabawa kuma daga wannan jumla ne suka fahimci cewa annabawa ba sa aikata kuskure.[236]
Ku Duba Wannan
Bayanin kula
- ↑ Hijazi, al-Tafsir al-Wadihi, 1413 AH, juzu'i. 1, shafi. 746.
- ↑ Shabestari, Aalam-ul-Quran, 2008, shafi. 937.
- ↑ Khorramshahi, "Musa (AS)", Juzu'i na 2, shafi na 2180.
- ↑ Zuhaili, Tafsir al-Wasit, 1422H, juzu'i. 2, shafi. 1181.
- ↑ Shabestari, Aalam-ul-Quran, 2008, shafi. 937.
- ↑ Rahbarian, "Musa", shafi na 1123.
- ↑ Rahbarian, "Musa", shafi na 1123.
- ↑ Rahbarian, "Musa", shafi na 1123.
- ↑ Alami, Tarajimu Aalam al-Nisa, 1407 AH, juzu'i na 2, shafi na 145.
- ↑ Qomi, Tafsir al-Qomi, 1404 AH, juzu'i. 1, shafi. 82.
- ↑ Suratul Maryam, aya ta 51.
- ↑ Suratul A'araf, aya ta 144
- ↑ Ibn Atiyah, Almuharrar Al-Awjiz, 1422H, juzu'i na 1, shafi na 148.
- ↑ Zaheili, al-Tafsir al-Munir, 1418 AH, juzu'i. 21, shafi. 216.
- ↑ Rahbarian, "Musa", shafi na 1123.
- ↑ Hijazi, al-Tafsir al-Wadih, 1413 AH, juzu'i. 1, shafi. 746.
- ↑ Suratul Maryam, aya ta 51-52.
- ↑ Fadlallah, Tafsiri Min Wahayi-ul-Qur'an, 1419 AH, juzu'i. 14, shafi. 28.
- ↑ Ahmadi، «نظریهای درباره محدود بودن شریعت حضرت موسی و حضرت عیسی به بنیاسرائیل»،Portal Jami Ulume Insani.
- ↑ Fadlallah, Tafsir Min Wahayi-ul-Quran, 1419 AH, juzu'i. 20, shafi. 202.
- ↑ Boroujerdi, Tafsire Jami, 1366, juzu'i na 2, shafi na 462
- ↑ Mughniyah, Tafsir al-Kashif, 1424 AH, juzu'i. 2, shafi. 495.
- ↑ Makarem Shirazi, Tafsir-e-Namune, 1374, juzu'i. 6, shafi. 363.
- ↑ Tabataba'i, Al-Mizan, 1417 AH, juzu'i. 2, shafi. 316.
- ↑ Tabatabaei, Al-Mizan, 1393 AH, juzu'i. 16, shafi. 32.
- ↑ Tabataba'i, Al-Mizan, 1417 AH, juzu'i. 2, shafi. 315.
- ↑ Malahavish, Bayan al-Ma'ani, 1382 AH, juzu'i na 2, shafi na 394.
- ↑ Khorramshahi, Daneshnameh Qur'ani Wa Qur'ani Pajuhi, Juzu'i na 2, shafi na 2180.
- ↑ Mostafavi, Al-Tahqiq, 1360 AH, juzu'i. 11, shafi. 206.
- ↑ Masoudi, Isbatul Wasiyya, Nashar Ansari, juzu'i. 1, shafi na 64.
- ↑ Boroujerdi, Tafsire Jami, 1366, juzu'i. 5, shafi na 147.
- ↑ Khuruj, Fasali na 1, aya ta 9-10.
- ↑ Makarem Shirazi, Tafsir-e-Namune, 1374, juzu'i. 16, shafi na 12-13.
- ↑ Jurjani, Jala Al-Azhan, 1377, juzu'i na 7, shafi na 153.
- ↑ Moghdisi, AlBada'u Wa al-Tarikh, Maktabat Al-Taqfah al-Diniya, vol. 3, ku. 83.
- ↑ Mughniyah, Tafsir al-Kashif, 1424 AH, juzu'i. 6, shafi. 51.
- ↑ Suratul Qasas, aya ta 7.
- ↑ Suratul Taha, aya ta 38.
- ↑ Tabatabaei, Al-Mizan, 1393 AH, juzu'i. 16, shafi. 10.
- ↑ Kiatabe Khuruj, Fasali na 2, Aya ta 3.
- ↑ Tayyib, Atyab al-Bayan, 1378, juzu'i. 10, shafi. 207.
- ↑ Suratul Qasas, aya ta 11.
- ↑ Suratul Qasas, aya ta 10.
- ↑ Suratul Qasas, aya ta 7.
- ↑ Suratul Qasas, aya ta 8.
- ↑ Khuruj, Fasali na 2, aya ta 9.
- ↑ Malahavish, Bayan al-Ma'ani, 1382 A.H., juzu'i na 6, shafi na 239; Moghdisi, al-Bada'u Wa al-Tarikh, Maktabat Al-Taqfah al-Diniya, vol. 3, ku. 84.
- ↑ Suratul Qasas, aya ta 9.
- ↑ Tabataba'i, Al-Mizan, 1417 AH, juzu'i. 16, shafi. 13.
- ↑ Makarem Shirazi, Tafsir Numno, 1374, juzu'i. 16, shafi.
- ↑ Suratul Shu'ara, aya ta 18.
- ↑ Makarem Shirazi, Tafsir Numno, 1374, juzu'i. 16, shafi.
- ↑ Khuruj, Fasali na 2, aya ta 9-10.
- ↑ Suratul Qasas, aya ta 15.
- ↑ Suratul Qasas, aya ta 15.
- ↑ Suratul Qasas, aya ta 20.
- ↑ Suratul Qasas, aya ta 21.
- ↑ Taleghani, Partuye Az Qur'ani, 1983, juzu'i na 3, shafi na 88.
- ↑ Moghdisi, Al-Bada'u Wal al-Tarikh, Maktabat Al-Taqfah al-Diniya, juzu'i na 3, shafi na 85.
- ↑ Suratul Qasas, aya ta 24.
- ↑ Qomi, Tafsir al-Qommi, 1367, juzu'i. 2, ku. 138; Maqdisi, Al-Bada'u Wal Tarikh, Maktaba al-Thaqafa al-Diniyah, vol. 3, ku. 85.
- ↑ Suratul Qasas, aya ta 25.
- ↑ Suratul Qasas, aya ta 27.
- ↑ Suratul Qasas, aya ta 27-28.
- ↑ Makarem Shirazi, Tafsir-e-Namune, 1374, juzu'i. 16, shafi. 72.
- ↑ Tabatabaei, Al-Mizan, 2014/2015, juzu'i. 16, shafi. 31.
- ↑ Suratul Naml, aya ta 7.
- ↑ Suratul Qasas, aya ta 30.
- ↑ Suratul Taha, aya ta 14.
- ↑ Suratul Taha, aya ta 13.
- ↑ Suratul Taha, aya ta 19.
- ↑ Suratul Taha, aya ta 20.
- ↑ Suratul Taha, aya ta 21.
- ↑ Suratul Taha, aya ta 22.
- ↑ Qaraati, Tafsir al-Noor, 2004, juzu'i. 7, ku. 333.
- ↑ Suratul Shuara, aya ta 10-11.
- ↑ Suratul Shuara, aya ta 12.
- ↑ Tabarsi, Majma' al-Bayan, 1372, juzu'i. 7, shafi. 292.
- ↑ Suratul Shuara, aya ta 13.
- ↑ Makarem Shirazi, Tafsir-e-Numno, 1374, juzu'i. 15, shafi. 197.
- ↑ Tabarsi, Jame'ul al-Jame, 1377, juzu'i. 3, shafi. 152.
- ↑ Suratul Shuara, aya ta 15.
- ↑ Suratul Shuara, aya ta 17.
- ↑ Suratul Shuara, aya ta 34.
- ↑ Suratul Shuara, aya ta 38-48
- ↑ Tayyib, Atyab al-Bayan, 1378, juzu'i. 2, shafi. 30..
- ↑ Tayyib, Atyab al-Bayan, 1378, juzu'i. 2, shafi. 30..
- ↑ Makarem Shirazi, Tafsir-e-Numno, 1374, juzu'i. 15, shafi. 243.
- ↑ Suratul Shuara, aya ta 63.
- ↑ Suratul Shuara, aya ta 35.
- ↑ Suratul Baqarah, aya ta 50.
- ↑ Hosseini Shirazi, Tabyin al-Qur'an, 1423 AH, shafi. 170.
- ↑ Suratul A'araf, aya ta 148.
- ↑ Tabari, Jami'ul al-Bayan, 1412 AH, juzu'i. 2, shafi. 388.
- ↑ Suratul A'araf, aya ta 152.
- ↑ Suratul A'araf, aya ta 155.
- ↑ Suratul Baqarah, aya ta 55.
- ↑ Makarem Shirazi, Tafsir-e-Namune, 1995, juzu'i. 1, shafi. 258.
- ↑ Mughniyah, Tafsir al-Kashif, 1424 AH, juzu'i. 1, shafi. 105.
- ↑ Suratul A'araf, aya ta 155.
- ↑ Makarem Shirazi, Tafsir-e-Numno, 1995, juzu'i. 1, shafi. 258.
- ↑ Moghdisi, Al-Bada'u Waal-Tarikh, Maktabat Al-Taqfah al-Diniya, juzu'i. 3, shafi. 87.
- ↑ Fakhr Razi, Mafatih al-Ghayb, 1420 AH, juzu'i. 11, shafi. 333.
- ↑ Suratul Ma'idah, aya ta 24.
- ↑ Suratul Ma'idah, aya ta 26.
- ↑ Suratul Ma'idah, aya ta 26.
- ↑ Makarem Shirazi, Tafsir-e-Numno, 1995, juzu'i. 1, shafi. 261..
- ↑ Suratul Baqarah, aya ta 57.
- ↑ Makarem Shirazi, Tafsir-e-Numno, 1995, juzu'i. 1, shafi. 261.
- ↑ Makarem Shirazi, Tafsir-e-Numno, 1995, juzu'i. 1, shafi. 272.
- ↑ Moghdisi, Al-bada'u Wa al-Tarikh, Maktabat Al-Taqfah al-Diniya, juzu'i na 3, shafi.87; Mughniyeh, Al-Kashif, 1424 AH, juzu'i na 1, shafi na 111.
- ↑ Talghani, Partoye az Quran, 1983, juzu'i. 1, shafi. 171.
- ↑ Moghdisi, Al-Bada'u Wa al-Tarikh, Maktabat Al-Taqfah al-Diniya, juzu'i na 3, shafi na 88.
- ↑ Maqdisi, Al-Bada'u Wal al-Tarikh, Maktaba Al-Thaqafa Al-Diniya, juzu'i. 3, shafi. 87; Tha'labi Nishaburi, Al-Kashf Wa Al-Bayan, 1422 AH, juzu'i. 4, shafi. 45.
- ↑ Tabarsi, Majma' al-Bayan, 1372, juzu'i. 3, shafi. 277.
- ↑ Masoudi, Isbatul Wasiyya, Nashar Ansariyan, shafi na 64.
- ↑ Sheikh Saduq, Kamal al-Din, 1395 AH, juzu'i. 2, shafi. 524..
- ↑ Mostafavi, Al-Tahqiq, 1360, juzu'i. 14, shafi. 276.
- ↑ Masoudi, Isbatul Wasiyya, Nashar Ansariyan, shafi na 63.
- ↑ Shabar, tafsirin al-kur’an a-Kareem, 1412 AH, shafi na 308.
- ↑ Suratul Naml, aya ta 7.
- ↑ Suratul Qasas, aya ta 30.
- ↑ Suratul Taha, aya ta 13.
- ↑ Shabestari, Aalam-ul-Quran, 2008, shafi. 937.
- ↑ Suratul Taha, aya ta 13.
- ↑ Tabataba'i, Al-Mizan, 1417 AH, juzu'i. 14, shafi. 139.
- ↑ Tabarsi, Majma' al-Bayan, 1372, juzu'i. 7, ku. 10.
- ↑ Suratul Taha, aya ta 13.
- ↑ Suratul Taha, aya ta 14.
- ↑ Suratul Taha, aya ta 14.
- ↑ Suratul Taha, aya ta 15.
- ↑ Mousavi Sabzevari, Muhaabih al-Rahman, 1409 AH, juzu'i. 10, shafi. 109.
- ↑ Bustani, Da'iratul Darul Mara'if, juzu'i. 7, shafi. 264.
- ↑ Bustani, Da'iratul Darul Mara'if, juzu'i. 7, shafi. 264.
- ↑ Musapour, "Attaura", Juzu'i. 8, shafi na 443.
- ↑ Makarem Shirazi, Tafsir-e-Numno, 1995, juzu'i. 1, shafi. 210.
- ↑ Sheikh Tusi, Al-Tabyan, Dar Ihya al-Turaht al-Arabi, juzu'i. 9, shafi. 287; Fakhr Razi, Al-Tafsir al-Kabir, 1420 AH, juzu'i. 27, ku. 587; Tabataba'i, Al-Mizan, 1393 AH, juzu'i. 2, shafi. 141.
- ↑ Al-Azhari, Tahdhib al-Lughah, 1421 AH, juzu'i. 1, shafi. 272.
- ↑ Karimi, Barrasi Mas'ale Jahani Budane Risalate Musa Wa Isa(A.S.) Az Negahe Qur'an Wa Ahadaini,” shafi na 120.
- ↑ Suratul Yunus, aya ta 75; Suratul Ghafir, aya ta 23 da ta 24; Suratul Zukhruf, aya ta 46; Suratul Shu'ara, aya ta 16 da ta 17.
- ↑ Subhani, Mafahim Alqur'an, 1421 AH, juzu'i na 3, shafi na 79-80.
- ↑ Suratul Isra’i, aya ta 2; Suratul Sajdah, aya ta 23; Suratul Ghafir, aya ta:53.
- ↑ Fakhr Razi, Tafsir al-Kabir, 1420 AH, juzu'i. 20, shafi. 297; Alusi, Ruh al-Ma'ani, 1415 AH, juzu'i. 8, shafi. 15.
- ↑ Fakhr Razi, Tafsir al-Kabir, 1420 AH, juzu'i. 20, shafi. 297.
- ↑ Makarem Shirazi, Fiqhu Maqarin, 1427 AH, juzu'i na 1, shafi na 587; Shalabi, Maqaranatu Adyanil Yahudiyya, 1992 AD, shafi na 238.
- ↑ Suratul An'am, aya ta 91; Suratul Anbiya, aya ta 48.
- ↑ Subhani, Mafahimul Alqur'an, 1421 AH, juzu'i na 3, shafi na 86.
- ↑ Soleimani, "Ahkame Attaura 613", shafi na 153.
- ↑ Soleimani, "Jarayime Dar Kifari Yahud", shafi na 142.
- ↑ Levy, Ahkame Wa Muqarrarat Hazrate Musa, 1375, shafi na 22.
- ↑ Hawks, Qamus Kitabe Muaqaddas, 2015, shafi na 760.
- ↑ Attaura, SIfru Lawiyan, Babi na 11, aya ta 1-47.
- ↑ Attaura, Leviticus, Babi na 12, ayoyi na 1-7 da Babi na 15, ayoyi na 1-33.
- ↑ Attaura, Sifru Lawaiyan, babi na 16, aya ta 5-27.
- ↑ Attaura,Sifru Lawaiyan 18:6-30 da 20:10-21; Ku duba Sifri Tasniya 22:14-20.
- ↑ Attaura, Sifru Lawiyan, babi na 23, aya ta 5-44.
- ↑ Attaura, Sifru Lawiyan, babi na 27, aya ta 14-31.
- ↑ Attaura, Sifru A'adad, Babi na 5, aya ta 12-31.
- ↑ Attaura, Sifru A'adad, Babi na 35, aya ta 16-32.
- ↑ Attaura, Sifru A'adad, Babi na 6 aya ta 1-21.
- ↑ Attaura, Sifru A'adad, Babi na 15, aya ta 1-31.
- ↑ Attaura, Sifru A'adad, Babi na 18.
- ↑ Attaura, Sifru A'adad, Babi na 31, aya ta 26-54.
- ↑ Attaura, Sifru Tasniyya, Babi na 4, aya ta 4-21.
- ↑ Attaura,Sifru Tasniya, Babi na 1, ayoyi 15-18 da Babi na 16, ayoyi 18-21 da Babi na 17, ayoyi 6-12.
- ↑ Attaura, Sifru Tasniya, babi na 19, aya ta 15-21.
- ↑ Attaura, Sifru Tasniya, surori 20, ayoyi 1-20.
- ↑ Attaura, Sifru Tasniyya, Babi na 24, aya ta 1-5.
- ↑ Tabarsi, Majma' al-Bayan, 1406 AH, juzu'i. 6, shafi na 684-685.
- ↑ Tabataba'i, Al-Mizan, 1393 AH, juzu'i. 13, shafi. 217; Makarem Shirazi, Tafsir Namune, 1374 AH, juzu'i. 12, shafi na 311 da 312.
- ↑ Tabataba'i, Al-Mizan, 1393 AH, juzu'i. 13, shafi. 217; Makarem Shirazi, Tafsir Namune, 1374 AH, juzu'i. 12, shafi na 311.
- ↑ Tabataba'i, Al-Mizan, 1394 AH, juzu'i. 13, shafi. 217; Makarem Shirazi, Tafsir Namune, 1374 AH, juzu'iu. 12, shafi na 311 da 312. Nikmanesh, Barrasi Mu’ujizate No Gane Hazrate Musa..., 1387H, shafi. 69; Al-Baqarah, 50; Al-A'araf, 136-138; Yunus, 90; Al-Isra’i, 103; Taha, 77 da 78; Shu'ara, 63 da 66; Kasas, 40; Zukhruf, 55; Dukhan, 23-24; Dhariyat, 40; Qamar, 42; Naze'at, 25.
- ↑ Nikmanesh, Barrasi Mu’ujizate No Gane Hazrate Musa..., 1387, shafi na 69; Al-A'raf, 107 da 117; Taha, 20 da 69; Shu'ara, 32 da 45; Naml, 10; Qasas, 31.
- ↑ Nikmanesh, Barrasi Mu’ujizate No Gane Hazrate Musa..., 2008, shafi na 69; Al-A'raf, 108; Taha, 22; Shu'ara, 33; Naml, 12; Qasas, 32.
- ↑ Nikmanesh, Barrasi Mu’ujizate No Gane Hazrate Musa..., 2008, shafi na 70; Al-Baqarah, 63 da 93; An-Nisa, 154; Al-A'raf, 171.
- ↑ , , Nikmanesh, Barrasi Mu’ujizate No Gane Hazrate Musa..., 2008, shafi na 69; Al-Baqarah, 55-56; An-Nisa, 153.
- ↑ Nikmanesh, Barrasi Mu’ujizate No Gane Hazrate Musa..., 2008, shafi na 70; Al-Baqarah, 57; Al-A'raf, 160; Taha, 80.
- ↑ , Nikmanesh, Barrasi Mu’ujizate No Gane Hazrate Musa..., 2008, shafi na 70; Al-Baqarah, 57; Al-A'raf, 160.
- ↑ , Nikmanesh, Barrasi Mu’ujizate No Gane Hazrate Musa..., 2008, shafi na 69; A'raf, 133.
- ↑ , Nikmanesh, Barrasi Mu’ujizate No Gane Hazrate Musa..., 2008, shafi na 69; A'raf, 130.
- ↑ , Nikmanesh, Barrasi Mu’ujizate No Gane Hazrate Musa..., 2008, shafi na 69; A'raf, 133.
- ↑ , Nikmanesh, Barrasi Mu’ujizate No Gane Hazrate Musa..., 2008, shafi na 69; A'raf, 133.
- ↑ , Nikmanesh, Barrasi Mu’ujizate No Gane Hazrate Musa..., 2008, shafi na 69; A'raf, 133.
- ↑ , Nikmanesh, Barrasi Mu’ujizate No Gane Hazrate Musa..., 2008, shafi na 69; A'raf, 133.
- ↑ , Nikmanesh, Barrasi Mu’ujizate No Gane Hazrate Musa..., 2008, shafi na 69;Al-Baqarah, 67-74.
- ↑ Rahnama da Parchibaff, “Ta'amulli Dar Ta'arif Kalami Mujizeh…”, shafi na 5.
- ↑ Rahnama da Parchibaff, “Ta'amulli Dar Ta'arif Kalami Mujizeh…”, shafi na 8-9.
- ↑ Suratul Taha, aya ta 19.
- ↑ Suratul Qasas, aya ta 31; Suratul Naml, aya ta 10.
- ↑ Suratul Shu'ara, aya ta 32.
- ↑ Suratul Shu'ara, aya ta 32.
- ↑ Suratul A'araf, aya ta 117.
- ↑ Suratul A'araf, aya ta 120, 121; Suratul Taha, aya ta 70; Suratul Shu'ara, aya ta 46-48.
- ↑ Suratul A'araf, aya ta 123; Suratul Taha, aya ta 71; Suratul Shu'ara, aya ta 49.
- ↑ Shabar, Tafsirul Al-Kur’anil Karim, 1412 Hijira, juzu’i na 1, shafi na 180.
- ↑ Tabarsi, Majma' al-Bayan, 1933, juzu'i. 4, shafi. 705..
- ↑ Sheikh Tusi, Al-Tibyan, juzu'i. 4, shafi. 492.
- ↑ Mughniyah, Tafsir al-Kashif, 1424 AH, juzu'i. 3, shafi. 375.
- ↑ Suratul Naml, aya ta 12.
- ↑ Suratul A'araf: aya ta 108; Suratul Taha, aya ta 22; Suratul Shu'ara, aya ta 33; Suratul Naml, aya ta 12; Suratul Qasas, aya ta 32.
- ↑ Suratul Taha, aya ta 22-24.
- ↑ Suratul Shu'ara, aya ta 33-34.
- ↑ Suratul Baqarah, aya ta 50.
- ↑ Suratul Shu'ara, aya ta 63.
- ↑ Suratul Isra'i, aya ta 103.
- ↑ Suratul Kahf, aya ta 60-82.
- ↑ Suratul Kahf, aya ta 65.
- ↑ Fayz Kashani, Tafsir al-Safi, 1415 AH, juzu'i. 3, shafi. 250.
- ↑ Suratul Kahf, aya ta 66.
- ↑ Suratul Kahf, aya ta 67-69.
- ↑ Suratul Kahf, aya ta 69.
- ↑ Suratul Kahf, aya ta 74.
- ↑ Suratul Kahf, aya ta 774.
- ↑ Suratul Kahf, aya ta 71,74 da 77.
- ↑ Suratul Kahf, aya ta 78.
- ↑ Suratul Kahf, aya ta 78.
- ↑ Misali, duba: Gonabadi, Qur'ane Majid Wa Seh Dastane Asrare Amiz Irfane, 1360, shafi na 51.
- ↑ Sayyid Murtaza, Tanziyah al-Anbiya, al-Sharif al-Radi, shafi. 2.
- ↑ Rawandi, Ƙasasul Anbiya, 1368, shafi na 154-155; Makarem Shirazi, Tafsir-Namune, 1353, juzu'i. 16, shafi. 54.
- ↑ Suratul Qasas, aya ta 15.
- ↑ Fakhr al-Razi, Al-Tafsir al-Kabir, 1420 AH, juzu'i. 24, shafi. 585.
- ↑ Fazel Moqdad, Al-Lawamiu Al-Elahiya, 1380, shafi. 259.
- ↑ Suratul Qasas, aya ta 16.
- ↑ Fazel Moqdad, Al-Lawamiu Al-Elahiya, 1380, shafi. 259
- ↑ Sheikh Tusi, Al-Tibiyan, Dar Ihya’ Al-Turahat Al-Arab, vol. 8, ku. 137; Fadel Miqdad, Al-Lawame’ Al-Ilahiya, 1380, shafi. 259.
- ↑ Zamakhshari, Al-Kashaf, 1407 AH, juzu'i. 3, shafi. 398; Alusi, Ruh al-Maani, 1415 AH, juzu'i. 10, shafi. 264.
- ↑ Zamakhshari, Al-Kashaf, 1407 AH, juzu'i na 3, shafi na 398; Alousi, Rooh al-Ma'ani, 1415 AH, juzu'i na 10, shafi na 264. Fakhr Razi, Ismatul al-Anbiya, 1409 AH, shafi. 92.
- ↑ Suratul A'araf, aya ta 150.
- ↑ Attaura, Sifru Khuruj, Babi na 32, Sashe na 19.
- ↑ Tabarsi, Majma' al-Bayan, 1372, juzu'i. 4, shafi. 743.
- ↑ Tabatabaei, Al-Mizan, 1393 AH, juzu'i. 8, shafi. 251.
- ↑ Zamakhshari, Al-Kashaf, 1418 AH, juzu'i. 2, shafi. 161.
- ↑ Misali, duba: Sifru Fedayesh, babi na 19, sakin layi na 21 da sakin layi na 30-38; Sifru Khuruj, babi na 4, sakin layi na 8-14.
- ↑ Kaveh, “Ismate Fiili Anbiyaye Ilahi Dar Kutbe Adyane Buzurge,” shafi na 37-38.
- ↑ Fedayesh, babi na 7, sakin layi na 1.
- ↑ Ashrafi da Rezaei, “Ismate Payambran Dar Qur'an,” shafi na 29.
Tsokaci
- ↑ Wasu sun bayyana wannan ganawa a matsayin miƙatin kwanaki arba'in (Makarim Shirazi, Tafsire Namune, 1374 H.S, juzu'i na 6, shafi na 342–343), yayin da wasu kuma suka yi imani cewa wani miƙati daban ne (Mullah Huwaish, Bayan al-Ma'ani, 1382 H.Q, juzu'i na 1, shafi na 431–432)
Nassoshi
- Alusi, Mahmoud bin Abdullah, Ruhul Ma'ani Fi Tafsir Alƙur'anil Azeem Was Saba'ul Masani, Beirut, Dar al-Kutb al-Ilmiyah, bugu na farko, 1415 AH.
- Ibn Atiyah, Abdul-Haqq bin Ghalib, Al-Muharrarul Wajiz Fi Tafsil Kitabil Aziz: Bincike Abdul-Salam Abdul-Shafi Muhammad, Beirut, Dar al-Kutb al-Ilmiyah, bugu na farko, 1422 AH.
- Azhari, Muhammad bin Ahmad, Tahdhib al-ugah, Beirut, Dar al-Ihya al-Turat al-Arab, 1421 AH.
- Ashrafi, Abbas da Umm al-Baneen Rezaee, “Ismate Payambarabn Dar Qur'an Wa Ahadaini”, Takardar Bincike kan Kimiyyar Alƙur'ani, Lamba ta 12, Bazara ta 2013.
- Etesami, Parvin,«دیوان اشعار، لطف حق», Shafin Ganjur, ranar ziyara: 31 Disamba 1401.
- Al-Alami, Mohammad Hossein, Taajimu Al-Alamin al-Nisa, Beirut, Gidauniyar Al-Alami don Littattafai, 1407 AH.
- Iqbal Lahori, Muhammad,«جاویدنامه، تمهید زمینی - آشکارا می شود روح حضرت رومی و شرح میدهد اسرار معراج را», Shafin Ganjur, ranar ziyara: 31 Disamba 1401.
- Amin, Mahdi, Tarikhe Adyane Az Didgahe Qur'an Wa Hadis, Qom, Bayan Jawan, 1389.
- Borujerdi, Seyyed Mohammad Ibrahim, Tafsir Jame, Tehran, Sadr Publications, bugu na 6, 1366.
- Bostani, Boutros, Daereh al-Ma'rif, Beirut, Dar al-Ma'rifa,
- Tha'labi Neyshaburi, Ahmad ibn Ibrahim, Al-Kashaf Wa Al-Bayan an Tafsir Al-Qur'an, Beirut, Dar Ihya al-Turaht al-Arab, 1422H.
- Jurjani, Hussein bn Hassan, Jala' al-Azhan Wa Jala' al-Azhan, Tehran, Tehran University Press, 1377.
- Hijazi, Muhammad Mahmoud, Tafsirul Al-Wazihi, Beirut, Dar al-Jil al-Jadeed, bugu na 10, 1413H.
- Hosseini Shirazi, Sayyid Muhammad, Tabyin al-Qur'an, Beirut, Darul Ulum, bugu na biyu, 1423H.
- Khorramshahi, Qavam al-Din, "Musa (AS)", Encyclopedia of the Quran and Quran Studies, Tehran, Dostan, 1998.
- «در کوه طور»،Rijistar, ranar ziyara: 14 ga Yuni, 1401.
- «ده فرمان چگونه ساخته شد؟»، Cibiyar Sinima, ranar ziyara: Disamba 3, 1401.
- Raghib Isfahani, Hussein bin Muhammad, Al-Mufradat fi Gharib al-Quran, Damascus, Dar al-Qalam, bugu na farko, 1412H.
- Rawandi, Qutb al-Din, Qasas al-Anbiya, Mashhad, Astan Quds Razavi, 1368H.
- رمضان ماهی، سمیه، «تحلیل مجسمه موسی ساخته میکلانژ»، سایت تبیان، تاریخ بازدید:۳آذر ۱۴۰۰ش.
- «روایت تاریخی_فرهنگی انیمیشن شاهزاده مصر»، Kamfanin Dillancin Labarai na IMNA, ranar ziyara: Disamba 3, 1401.
- Rahbarian, Mohammad Reza, "Musa", Daneshnameh Muasir Kur'ane Kareem: Seyyed Salman Safavi, Qom, Cibiyar Nazarin Iran ta London, 2018.
- Zuhaili, Wahba bin Mustafa, Tafsir al-Munir fi al-Aqeedah wa al-Shari'ah wa al-Manhaj, Beirut, Damascus, Darul Fikr al-Masjid, bugu na biyu, 1418H.
- Zuhaili, Wahba bin Mustafa, Tafsir Wasit, Damascus, Darul Fikr, bugun farko, 1422H.
- Zamakhshari, Mahmoud bin Abdullah, Al-Kashf, Riyadh, Maktaba al-Ubaikan, bugu na biyu, 1418H.
- Saqi, Abul-Fadl, Tarjame Farsi Taurat, Tehran, Bincike kan Dokoki da Addinai, 2019.
- Sobhani, Ja'afar, Mafahim Qur'an, Qom, Gidauniyar Imam al-Sadiq (a.s.), bugu na 3, 1421 AH.
- Saadi Shirazi, Musleh bin Abdullah, «غزلیات، غزل ۳۸۹»،Shafin Ganjur, ranar ziyara: 31 ga Disamba 1401.
Soleimani, Hossein, "Ahkame 613 Ganeh Taurat", Haft Asman, No. 18, Summer 2003.
- Soleimani, Hossein, "Jarayime Dar Huque Kifari Yahud", Haft Asman, No. 16, Winter 2002.
- Seyyed Murtaza, Alam al-Huda, Tanziyyah al-Anbiya, Qum, Al-Sharif al-Radi, Beta.
- Shabar, Sayyid Abdullah, Tafsir Al-Quran al-Karim, Beirut, Darul Balagha na Bugawa da Bugawa, Bugu na Farko, 1412 Hijira.
- Shabestari, Abdul-Hossein, Aalam al-Quran, Qom, Bostan Kitab, 2008.
- Shalabi, Ahmad, Muqaranatul Adaynil Yahudiyya, Alkahira, Al-Nahda Egypt Library, Bugu na Goma, 1992.
- Sheikh Saduq, Muhammad bn Ali bn Babuyyah, Ayoun Akhbar al-Rida (AS), Beirut, Al-Alami Publishing Foundation, Bugu na Farko, 1404H.
- Sheikh Saduq, Muhammad bin Ali bin Babawayh, Kamal al-Din Wa Tamam al-Ni'ima, Tehran, Islamiyyah, bugu na biyu, 1395H.
- Sheikh Tusi, Muhammad ibn Hassan, Al-Tibiyan fi Tafsir al-Quran, gabatarwar Sheikh Agha Buzurg Tehrani, bincike na Ahmad Qusayr Ameli, Beirut, Dara Hayya al-Turat al-Araby.
- Talghani, Mahmoud, Partoyi az Qur’an, Tehran, Sahami Publication, 1362.
- Tabarsi, Fadl ibn Hassan, Majma’ al-Bayan fi Tafsir al-Quran, gabatarwar Muhammad Javad Balaghi, Tehran, Nasser Khosrow, bugu na uku, 1372.
- Tabari, Muhammad ibn Jarir, Jame’ al-Bayan fi Tafsir al-Quran, Beirut, Dar al-Mar’afa’, bugun farko, 1412H.
- Turahi, Fakhr al-Din ibn Muhammad, Majma’ al-Baharain, Tehran, Mortazavi Publication, 1375.
- Tayyib, Abdul Hussein, Atib al-Bayan fi Tafsir al-Quran, Tehran, Islam Publication, 1378.
- Fadl al-Miqdad, Abdullah ibn Miqdad, Luwa’me’ Alilahiya fi al-Mabahith al-Kalaamiyyah, Qom, Daftar Tablik al-Islami, 1380.
- Fakhr Razi, Muhammad bn Omar, Tafsir al-Kabir, Beirut, Darul Kutb al-Ilmiyah, 1420H.
- Fakhr Razi, Muhammad bn Omar, Ismat al-Anbiya, Beirut, Darul Kutb al-Ilmiyah, 1409H.
- Farahi Haravi, Moin al-Din, Qasase Musa (AS): Tafsir Irfani Bar Paye Qur'an Majid, wanda Mohsen Kiani da Ahmad Beheshti Shirazi, Kamfanin Buga Ilimi da Al’adu na Tehran suka yi, 1393 bayan hijira.
- Fadlallah, Sayyid Muhammad Hussein, Tafsir min Wahayi al-Quran, Beirut, Darul-Mulak na Bugawa da Bugawa, bugu na biyu, 1419H.
- Fayz Kashani, Malam Hasan, Tafsir al-Safi, wanda A’alami, Hussein, al-Sadr Publishing, Tehran ya yi bincike, bugu na biyu, 1415 AH.
- Qara'ti، «مثنوی موسی و شبان مولوی کاملا ضد قرآنی است», Shafin Khabaronline. Ranar ziyara: 23 Disamba 2011.