Daƙiƙa:Suratul Zariyat
:Domin ganin kammalallen nassin wannan shafi. ku duba: Nassin: Suratul Zariyat.
Ƙaf Zariyat Ɗur | |
| Lambar Sura | 51 |
|---|---|
| Juzu'i | 26 da 27 |
| Adadin Ayoyi | 60 |
| Adadin Kalmomi | 360 |
| Adadin Haruffa | 1546 |
| Makkiya/Madaniyya | Makkiya |
Suratul Zariyat (Larabci: سورة الذاريات) Sura ta 51 cikin Juzi'i na 26 da 27 cikin ƙur'ani mai girma, sura ce da aka saukar a Makka, kuma sunanta an ciro shi ne daga aya ta farko, wannan sura tana magana ne kan ranar Alƙiyama, da kaɗaita Allah da magana kan baƙon Ibrahim (A.S) daga cikin mala'iku, da ƙissar Musa (A.S) tana magana kan al'ummomin da suka ƙi yarda da annabawansu, kuma tana umartar Annabi (S.A.W) da ya yi haƙuri idan ya sami kanshi a cikin wahala.
Daga cikin shahararrun ayoyinta akwai wannan ayar: Kuma ban halicci mutum da aljanu ba sai don su bauta mini Akwai ruwayoyi da yawa da suka zo kan falalar karanta wannan sura, daga cikin abin da aka rawaito daga Annabi (S.A.W) cewa duk wanda ya karanta suratul Zariyat, to Allah zai bashi lada guda goma gwargwadon yawan iskar da ts kaɗa da gudana a duniya.
Sunanta Da Ayoyinta
An sawa wannan sura wannan suna Zariyat, saboda farawa cikin ayar farko da wannan kalma faɗar Allah, (وَالذَّارِيَاتِ ذَرْوًا)[1] Azzariyat tana nufin iskar da take ɗibar ƙasa da wasu abubuwa yayin da ta kaɗa, hakan yana nufin iskar da take rarrabawa da watsar da ƙasa da abubuwa.[2] Ayoyinta 60 ne kalmominta 360 haruffanta 1546, ana la'akarinta a matsayin Mufassalat surar da take gajera amma da ayoyi da yawa.[3]
Jerantuwa Ta Sauka
Suratul Zariyat tana cikin surorin Makka[4] ne kuma a jerin sauka ita ce sura ta 67 da ga sauka gurin Annabi (S.A.W), amma yanzu lambarta a cikin ƙur'ani ita ce ta 51, cikin juzu'i na 26 da 27.[5]
Ma'anar Kalmominta
Mafi muhimmancin ma'anonin kalmomin surar Kalmar (الذَّارِيَاتِ ذَرْوًا) ma'ana iskar da take ɗaukar turɓaya ta yi watsi da ita guri daban-daban. Kalmar (الْحَامِلاتِ وِقْرًا) ma'ana gajimare ko gizagizai waɗanda suke ɗauke da ruwa. Kalmar (الْجَارِيَاتِ يُسْرًا) tana nufin jiragen ruwa waɗanda suke tafiya cikin ruwa da sauƙi Kalmar (الْمُقَسِّمَاتِ أَمْرًا) ma'ana Mala'iku waɗanda suke raba al'amarin ibada ko iskar da take rarraba ruwan sama. Kalmar (ذَاتِ الْحُبُكِ) wannan kalma jam'i ce ta habika, ai abin nufi duk abin da ka iya da kyau. Kalmar (الْخَرَّاصُونَ) Alkarras yana nufin kazzab, Maƙaryaci. Kalmar (مُسَوَّمَةً) tana nufin ma'abociyar alama. Kalmar (الْيَمِّ) tana nufin kogi Kalmar (ذَنُوبِ) Idan aka yiwa harafin Zal wasali, tana da ma'anar wani yanki daga azaba.[6]
Abin da Yake Cikin Surar
Abubuwan da ke cikin surar sun taƙaita zuwa sassa da dama: 1. Tana magana kan ranar Alƙiyama 2. Wannan sura tana magana kan kaɗaita Allah, ayoyin kuma suna magana kan tsari wajan samar da halittu. 3. Tana magana kan baƙon Ibrahim daga cikin mala'iku da umarnin da aka ba su na ruguza garuruwan mutanen Annabi Luɗ (A.S) 4. Tana bayyana ƙissar Musa (A.S) da wasu alumma, kamar mutanen Adawa da mutanen Samud da mutanen Nuhu . 5. Tana magana kan fuskantar wasu al'umma da suka kangarewa annabawansu kuma tana umartar Annabi (S.A.W) da ya yi haƙuri kuma ya jajirce wajan fuskantar matsaloli da wahala.[7]
Shahararrun Ayoyinta
Faɗar Allah: Kuma ban halicci mutum da aljani ba sai don su bauta mini.[8] A cikin ƙur'ani akwai magana iri-iri kan al'amarin halittar ɗan'adam da hadafin halittarshi[9] abin da ayar take nufi a nan shi ne cewa Allah bai halicci mutum da Aljan ba face dan su bauta mishi, saboda haka dalilin yin halittar mutum shi ne domin ya sami lada, wanda lada ba zai samu ba har sai mutum ya bautawa Allah, hakan ta sa kamar Allah ya halicci ɗan'adam ne domin ya bauta mishi[10] bautar Allah tana nufin ƴancin ɗan'adam daga bautar wani Allah, kamar bautar kuɗi ko matsayi da duk wani son zuciya da adalci[11] hadisi ya zo daga Imam Sadiƙ (A.S) kan wannan aya, cewar Allah ya halicce su ne domin ya ba su umarni ya kuma hane su da ɗora musu wani nauyi, amma fa ba ya haliccesu ba ne domin tilas su bauta mishi ba, a a zai jarrabe su da ba su umarni da hana su, domin ya ga wane ne zai bi shi kuma wane ne zai saɓa mishi.[12]
Falaloli Da Hususiyoyi
Akwai falaloli da yawa da suka zo kan karanta wannan sura daga cikinsu akwai:
- An rawaito daga Annabi (S.A.W) duk wanda ya karanta suratul Zariyati, Allah zai ba shi lada goma gwargwadon iskar da ta kaɗa da gudana a duniya.[13]
- An rawaito daga Imam Sadiƙ (A.S) cewa duk wanda ya karanta wannan sura da rana ko dare, to Allah zai gyara abin da yake buƙata na rayuwa, ya bashi arziƙi mai yawa kuma zai haskaka kabarinshi da wata fitila mai haskawa har zuwa ranar Alƙiyama.[14]
An rawaito abubuwan da suka keɓanta da wannan sura da yawa:
- Ya zo daga Manzon Allah (S.A.W) cewa duk wanda ya rubuta wannan sura, ya wanke ya sha, to cuwan cikinshi zai gushe, idan kuma aka rubuta ta aka bawa mai ciki mai tsananin naƙuda, to za ta haihu da sauri.[15]
Bayanin kula
- ↑ Al‑Musawi, Al‑Wadih fi at‑Tafsir, Juzu’i na 15, Shafi na 146
- ↑ Al‑Alusi, Ruhul Ma’ani, Juzu’i na 27, Shafi na 5
- ↑ Al‑Khurmushahi, Mawsu’atul Qur’an wal‑Buhuth, Juzu’i na 2, Shafi na 1252
- ↑ At‑Tusi, Tafsiru at‑Tibyan, Juzu’i na 10, Shafi na 614; Ar‑Razi, At‑Tafsiru al‑Kabir, Juzu’i na 28, Shafi na 167
- ↑ Ma’arifa, At‑Tamheed fi Ulumil Qur’an, Juzu’i na 2, Shafi na 169
- ↑ Al‑Musawi, Al‑Wadih fi at‑Tafsir, Juzu’i na 15, Shafuka na 147–178
- ↑ Makarim Shirazi, Tafsiru al‑Amthal, Juzu’i na 17, Shafi na 44
- ↑ Suratul Dhariyat: aya ta 56.
- ↑ Makarim Shirazi, Tafsiru al‑Amthal, Juzu’i na 17, Shafi na 86
- ↑ At‑Tabrasi, Majma’ul Bayan, Juzu’i na 9, Shafi na 398
- ↑ Mughniya, Tafsiru al‑Kashif, Juzu’i na 7, Shafi na 158
- ↑ Al‑Huwaizi, Nuruth Thaqalayn, Juzu’i na 7, Shafi na 147
- ↑ Az‑Zamakhshari, Tafsiru al‑Kashshaf, Juzu’i na 4, Shafi na 1555. Na juya lafuzzan cikin rubutun Hausa, amma na bar su da tsarin asali. Kana so in tattara duk waɗannan bayanan da kake kawo min a jerin tebur domin ya fi sauƙin karantawa da kwatanta wurin bugawa, juzu’i da shafuka?
- ↑ At‑Tabrasi, Jawami’ul Jami’, Juzu’i na 3, Shafi na 425
- ↑ Al‑Bahrani, Tafsiru al‑Burhan, Juzu’i na 9, Shafi na 122
Sadarwa Ta Waje
Nassoshi
- Alusi, Mahmudu ɗan Abdullahi, Ruhul Ma’ani fi Tafsiril Qur’ani al‑Azim was‑Sab’il Mathani, Bayrut – Lebanon, Dar Ihya’ut Turathil Arabi, Bugu na 1, 1421 H.
- Al‑Kur’ani Mai Tsarki
- Bahrani, Hashimu ɗan Sulaiman, Al‑Burhan fi Tafsiril Qur’an, Bayrut – Lebanon, Dar Ihya’ut Turathil Arabi, Bugu na 1, 1429 H.
- Huwaizi, Abdu Ali ɗan Jum’a, Tafsiru Nurith Thaqalayn, Bayrut – Lebanon, Mu’assasat at‑Tarikh al‑Arabi, Bugu na 1, ba a sa shekara ba.
- Khurmu‑shahi, Baha’uddin, Mawsu’atul Qur’an wad‑Dirasat al‑Qur’aniyya, Iran – Tehran, Mu’assasat al‑Asdiqa’, 1377 Sh.
- Makarim Shirazi, Nasiru, Al‑Amthal fi Tafsiri Kitabillahil Munazzal, Bayrut – Lebanon, Mu’assasat al‑Amira, Bugu na 2, 1430 H.
- Ma’arifa, Muhammadu Hadi, At‑Tamheed fi Ulumil Qur’an, Qum – Iran, Dhawi al‑Qurba, Bugu na 1, 1428 H.
- Mughniya, Muhammadu Jawad, Tafsiru al‑Kashif, Bayrut – Lebanon, Darul Anwar, Bugu na 4, ba a sa shekara ba.
- Musawi, Abbasu ɗan Ali, Al‑Wadih fi at‑Tafsir, Bayrut – Lebanon, Markazul Ghadir, Bugu na 1, 1433 H.
- Razi, Muhammadu ɗan Umar, At‑Tafsiru al‑Kabir, Bayrut – Lebanon, Darul Kutub al‑Ilmiyya, Bugu na 4, 1434 H.
- Tabrasi, Al‑Fadlu ɗan al‑Hasan, Majma’ul Bayan, Tehran – Iran, Darul Uswa, Bugu na 1, 1426 H.
- Tabrasi, Al‑Fadlu ɗan al‑Hasan, Tafsiru Jawami’ul Jami’, Qum – Iran, Mu’assasat an‑Nashr al‑Islami ta Jami’ar Mudarrisin, Bugu na 2, 1430 H.
- Tusi, Muhammadu ɗan al‑Hasan, At‑Tibyan fi Tafsiril Qur’an, Qum – Iran, Mu’assasat an‑Nashr al‑Islami, Bugu na 1, 1431 H.
- Zamakhshari, Mahmudu ɗan Umar, Al‑Kashshaf, Bayrut – Lebanon, Dar Sadir, Bugu na 1, 1431 H.