Jump to content

Tattakin Arba'in (Najeriya)

Daga wikishia
Tattakin Arba'in (Najeriya)
Lokacin da aka shirya20 Safar
Wurin da aka shiryaNajeriya
Faɗin ƙasaNajeriya
Wuridai da TakeLabbaika Ya Husain (A.S) da Labbaika Ya Mahdi (A.F)
Mu'assasa da ƙarƙashintaHarkar Muslunci Najeriya


Tattakin arba'in a Najeriya, (Larabci: المسيرة الأربعينية في نيجيريا) yana cikin ayyukan addini a wurin Shi'a a Najeriya da suke yi kwanakin ƙarshe na arba'in na Husaini (20 Safar) wannan tattaki yana kasancewa a yankuna daban-daban n Arewacin Najeriya zuwa garin Zariya. Wannan tattaki yana daga cikin mafi girman manya-manyan tarurruka na duniyar Muslunci bayan tattaki da ake yi zuwa Karbala, Ana cewa dubunnan ɗaruruwan ƴanshi'ar Najeriya ne suke shiga wannan tattaki. A lokuta da dama gwamnatin Najeriya ta afkawa masu yin tattaki lamarin da ya jawo asarar rayuka da jikkata wasu adadi.

Waɗanda Suka Kasa Zuwa Arba'in Na Karbala

Tattakin arba'in a Najeriya yana daga cikin manyan taron jama'a a duniyar Muslunci, bayan taron tattakin arba'in a Iraƙ.[1] Bisa rahotanni, dubunnan ɗaruruwan mutane ne suke halartar wannan taro[2] na makokin Imam Husaini (A.S) daga yankuna daban-daban na Najeriya, inda suke doguwar tafiya tsakanin kilomita 80-160 suna tattaki da ƙafafunsu[3] zuwa Husainiyyar Baƙiyatullahi Zariya[4] An ce wannan tattaki yana da tasiri matuƙa cikin janyo mutane zuwa shi'anci.[5] Najeriya ita ce ƙasa mafi yawan adadin jama'a a Afrika, kuma ita ce ta uku a yawan jama'a a cikin ƙasashen Musulmi a duniya.[6] An bada rahota cewa Ahlus-Sunna[7] da Kiristoci su ma suna shiga wannan tattaki a Najeriya.[8]

Labbaika Ya Imam Mahadi (A.F) Labbaika Ya Husaini (A.S) suna daga cikin taken da ƴanshi'ar Najeriya suke rerawa a lokacin wannan tattaki.[9]

Kashe-kashen Masu Tattakin Arba'in A Najeriya

Bisa rahotanni, gwamnatin Najeriya duk shekara tana afkawa masu makokin ranar arba'in na lumana tare da amfani da harsashi mai rai a kansu.[10]

A shekarar 2015 gwamnatin Najeriya bayan kashe ɗaruruwan ƴanshi'a a Najeriya ta ruguje Husainiyyar Baƙiyyatullahi a garin Zariya ta kuma kama Shaikh Zakzaky shugaban ƴan shi'ar Najeriya[11] tare kuma da kashe masa ƴaƴa.[12]

A shekarar 2016m, sakamakon buɗewa wuta da sojojin Najeriya suka yi ka ƴanshi'a masu tattaki a garin Kano, an kashe kusan mutane 100 da suka haɗa da mata da ƙananan yara..[13]

A lokacin tattakin arba'in na shekarar 2018m, wasu jama'a daga ƴanshi'a a Najeriya cikin nuna fushinsu kan ci gaba da tsare Shaik Zakzaky, sun shirya jerin gwano tare da neman gaggauta sakin Shaikh Zakzaky. Sojojin Najeriya sun kai hari kan masu muzahara, bisa madogaran labarai an ce an shahadantar mutum 40 daga masu muzahara.[14]

A ranar 10 Satumba 2024m, a garin Abuja babban birnin tarayyar Najeriya ƴansandan sun kai hari kan masu tattaki tare da shahadantar wasu adadi da jikkata wasu adadi da kama wasu adadi.[15]

kamfanin dillancin labarai na Abna, a taron arba'in na 2024 jami'an tsaron Najeriya sun tilastawa mata na Shi'a cire hijabi, wand ahaka ya fusata `yanshi'a suka yi jerin gwano a titunan garuruwa daban-daban don nuna rashin amincewa da wannan mataki.[16]

Haka nan a shekarar 2013m, Boko Haram sun ɗana bom cikin masu tattaki, bayan fashewa kusan mutane 30 suka yi shahada tare da jikkata gomomi.[17]

Ku Duba

Bayanin kula

  1. Kurdi, Shi'ayane Nijriye (Fursatha, Tahdidha, Babarha)," shafi. 123.
  2. Hosseini,Qatle Am Bi Saro Sida Shi'ayane Nijeriya Arbaeen 97,” shafi. 64; Kurdi, Shi'ayane Nijriye (Fursatha, Tahdidha, Babarha)," shafi. 123.
  3. «برگزاری باشکوه‌ترین مراسم اربعین»، Hukumar Labarai ta Jamhuriyar Musulunci.
  4. «پیاده روی اربعین در نیجریه»، "Hukumar Labarai ta Ƙasa da Ƙasa mai Hotuna – Iran Press".
  5. Shojaei Fard,Negahi beh Zindagi Sheikh Ibrahim Zakzaky, Rahbare Shi’ayane a Nijeriye, Ibrahimi Ba Qudrat Yek Ummat, shafi. 40
  6. Ghaibi Hajipour da Namdar, "Tasirat Wa Baztab Inqilabe Islami Iran Dar Nijeriye," shafi na. 72
  7. «اربعین در نیجریه»، Kamfanin Dillancin Labarai na Mizan.
  8. Ghaibi Hajipour da Namdar, "Tasirat Wa Baztab Inqilabe Islami Iran Dar Nijeriye," shafi na. 81
  9. Kurdi, Shi'ayane Nijriye (Fursatha, Tahdidha, Babarha)," shafi. 123.
  10. «اربعین خونین ابوجا»، روزنامه خراسان.
  11. «توطئه سعودی‌ها و صیهونیست‌ها برای سرکوب شعیان نیجریه»، Kamfanin Dillancin Labarai na Mizan؛ «افشاگری شیخ زکزاکی از نقش انگلیس در کشتار شیعیان نیجریه» Shafin Kihan
  12. «اربعین خونین ابوجا»، Jaridar Khorasan; Pishvaei, "Maganar Watan: Launin Parisian, Beiruti, da Jinin Najeriya," shafi. 7;«افشاگری شیخ زکزاکی از نقش انگلیس در کشتار شیعیان نیجریه» Shafin Kihan
  13. «شیعیان نیجریه»، Shafin Diflomasiya ta Iran.
  14. «شیعیان نیجریه»، Shafin Diflomasiya ta Iran.
  15. «شیعیان نیجریه»، Shafin Diflomasiya ta Iran
  16. «تظاهرات شیعیان نیجریه علیه سرکوب عزاداران اربعین حسینی»، Kamfanin dillancin labarai na Abna.
  17. «شیعیان نیجریه»، Shafin Diflomasiya ta Iran.

Nassoshi

  • "Haɗin kai tsakanin Saudiyya da Sahayoniya don murƙushe Shi'a a Nijeriya", Kamfanin Dillancin Labarai na Mizan, kwanan wata: 31 ga Oktoba, 2018, ranar da aka duba (ko aka ziyarci shafin): 4 ga Satumba, 2024M.
  • Arba'in a Nijeriya», Kamfanin Dillancin Labarai na Mizan, ranar da aka wallafa labarin: 4 ga Disamba, 2015, ranar da aka duba (ko aka ziyarci shafin): 4 ga Satumba, 2024M.
  • Fallasa da Sheikh Zakzaky ya yi game da rawar da Ingila ke takawa wajen kisan kiyashin da ake yi a Nijeriya», shafin jaridar Kayhan, kwanan watan wallafawa: 23 ga Satumba, 2022, ranar da aka duba (ziyara): 6 ga Satumba, 2024M.
  • Ganawar Sheikh Zakzaky da wasu daga cikin masu halartar Arba'in», Kamfanin Dillancin Labarai na Hawza (Hawza News), kwanan watan wallafawa: 13 ga Agusta, 2024, ranar da aka duba (ziyara): 7 ga Satumba, 2024M.
  • Hosseini, Mehdi, "Kisan kiyashin da aka yi wa 'yan Shi'a a Nijeriya a lokacin Arba'in 97 (2018) a ɓoye," a cikin mujallar Pasdar-e-Islam, lamba 441-442, Nuwamba da Disamba 2019M.
  • Kurdi, Hamid Reza, "Shi'an Nijeriya (Damammaki, Barazana, da Kalubale)," a cikin mujallar Payam (Saƙo), lamba 116, lokacin hunturu (Winter), 2015M.
  • Nijeriya: Ƙasa ta Uku mafi yawan Musulmai: Shi'an Nijeriya», a cikin mujallar Dars-ha-ye az Maktab-e-Islam, lamba 661, Yuni 2016M.
  • Ghaibi Hajipour, Nazanin da Mahdieh Namdar, "Tasirin Juyin Juya Halin Musulunci na Iran da Martaninsa a Nijeriya," a cikin mujallar Nameh-e-Jame'a, lamba 119, lokacin kaka (Fall), shekarar 2016M.
  • Gudanar da Mafi Girman Bikin Arba'in," Kamfanin Dillancin Labaran Jamhuriyar Musulunci (IRNA), kwanan wata: 5 ga Disamba, 2015M.
  • Pishvaei, Mehdi, "Maganar Wata (Sukhane Mah): Launin Jinin Mazaje, Baƙin Ciki a Nijeriya", a cikin mujallar Dars-ha-ye az Maktab-e-Islam, lamba 657, Fabrairu 2016M.
  • Shojaifard, Mohammad Hassan, "Dubawa rayuwar Sheikh Ibraheem Zakzaky, Jagoran 'Yan Shi'ar Nijeriya; Ibrahim mai ikon al'umma guda," a cikin mujallar Pasdar-e-Islam, lamba 455 da 456, Janairu da Fabrairu 2020M.
  • Tafiya a Ƙafa don Arba'in a Nijeriya", Kamfanin Bidiyo na Ƙasashen Duniya na Iran Press, kwanan wata: 8 ga Oktoba, 2022, ranar da aka duba (ko aka ziyarci shafin): 29 ga Satumba, 2024M.
  • Zanga-zangar 'yan Shi'ar Nijeriya kan murƙushe masu makokin Arba'in na Imam Husaini (AS),» Kamfanin Dillancin Labarai na ABNA, kwanan watan wallafawa: 23 ga Agusta, 2024, ranar da aka duba (ziyara): 1 ga Satumba, 2024.