Sayyid Ibrahim Ra'isi

Daga wikishia

Sayyid Ibrahim ra’isi al-sadati, (Larabci:السيد إبراهيم رئيس الساداتي) (1339-1403. h. shamsi) wanda aka sani da Sayyid Ibrahim ra’isi, malamin addini na shi’a kuma mutum na takwas cikin jerin shugabannin jamhuriyar muslunci ta Iran, ya yi karatun addini a hauzar ilimi ta ƙum da mashad haka nan ya yi karatu a jami’ar shahid muɗahhari da take a tehran. Ra’isi ya kasance memba a majalisar malaman addini ƴan gwagwarmaya. Ya kasance yana ɗaukar nauyin jan ragama ɓangarori da muƙamai daban-daban cikin jamhuriyar muslunci ta Iran, daga jumlarsu akwai: shugabancin hukumar shari’a, jagorancin ma’aikatar bakiɗayan kotukan ƙasa, shugabancin hukumar bincike cikin bakiɗayan ƙasa, shugabancin kotun malamai da ɗaliban addini, memba a majalisar fayyace maslahar gwamnati da kuma wakilci a majalisar kwararrun jagoranci, haka nan kuma ya shugabancin haramin Imam Ali ɗan Musa Al-Rida (a.s) har tsawon shekaru uku. Ranar 30 ga watan Urdibeheshti shekara 1403 h. shamsi. wanda ya yi daidai da 19 ga watan Mayu 2024 miladiya Sayyid Ibrahim ya amsa kiran ubangiji bayan hatsarin da ya faru da shi yana cikin jirgin sama mai sauka ungulu.

Tarihin Rayuwa da Karatu

An haifi Sayyid Ibrahim ra’isi a ranar 23 ga watan Azar shekara ta 1339 h. shamsi. a garin mashad a yankin naugan, salsalar nasabarsa tana danganewa zuwa ga Zaidu ɗan Ali, ya fara karatun hauza a mashad a makarantar hauzar nawab, sannan ya cigaba da karatu a shekarar 1354 a hauzar ƙum, ya yi almiranta a hannun manya-manyan malamai misalin Yadullahi Duzdani, Sayyid Ali Muhaƙƙiƙ Damad, Ali Akbar Mishkini, Ahmed Baheshti, Murtada Muɗahhari da Husaini Nuri Hamdani.[1]‌‌ haka nan kuma ya shiga darajin karijul fiƙihu na Sayyid Muhammad Hassan mar’ashi, Sayyid Mahmud Hashimi shaharudi, Agha Mujtaba taharani, Ayatullahi Khamna’i da sauran manyan malamai..[2]

Ya kasance ɗalibi a makaranta Madraseh Ali Shahid Muɗahhari ind aya karanci fiƙihu da huƙuƙ.[3] a shekarar 1362 h. shamsi, ya auri Jamila ɗiyar babban limamin garin mashad Sayyid Ahmad Alamul Huda.[4]

Tarihin Gwagwarmaya Tun Kafin Samun Nasarar Juyin Juya Hali A Iran

Kamar yanda aka naƙalto, haƙiƙa Sayyid Ibrahim ra’isi shekaru gabanin kafa jamhuriyar muslunci a Iran, ya kasance yana ayyukan gwagwarmaya lamarin da yakai ga jami’an leƙen asirin fadar sarki shah suka kama shi[5]‌‌ haka nan kuma ya kasance tare da rakiyar ba’arin ɗalibai yana zuwa ziyartar malaman addini da gwamnatin shah ta kora ta kai su wurare masu nisa daga inda suke, daga jumnlarsu akwai zuwa ganin Ayatullahi Khamna’i wanda aka kora zuwa garin Iranshahar ra’isi ya je wannan gari don ziyartarsa,[6] bayan yaɗa wani rubutu na cin fuska kan Imam Khomaini a cikin jaridar Iɗɗila’at a 17 ga watan day shekara ta 1356, ra’isi ya shiga taron nuna rashin amincewa kan wannan cin fuska, wanda aka fara shi daga makarantar Ayatullahi Burujurdi (Madraseh Khan).[7] haka kuma a watan Bahman shekara 1357 h. shamsi. ya halarci taron malamai cikin nuna rashin amincewa da rufe filin sauka da tahsin jirage don hana saukar jirgin da ya ɗauko Imam Khomaini don dawo da shi Iran.[8]

Shugabancin Haramin Imam Rida (A.S)

Ibrahim Raisi daga cikin mayaka Iran a yakin Iran da Iraƙi.[9]

A shekarar 1394 bayan mutuwar Abbas wa’iz ɗabasi, ƙarƙashin umarnin jagoran juyin juya halin muslunci na Iran Sayyid Ali Khamna’i an naɗa ra’isi muƙamin kula da haramin Imam Rida (a.s)[10] har zuwa watan farwardinb shekara ta 1398 ya cigaba da zama a wannan muƙami[11] lokacin shugabancinsa ya samar tarin hidimomi ga wannan wuri mai tsarki, daga jumlarsu akwai samar da unguwannin maziyarta da suke kusa da haramin, tare da hidima samar musu da makwanci da abin ci da sauran hidimomi,[12] haka nan kuma samar da tsarin ɗaukar nauyin masu son zuwa ziyara garin mashad, tare da fifita raunana cikinsu, samar da miƙatin Rida (Wurin ne da aka tane da shi don hutawar maziyarta) kan hanyoyin da suke tuƙewa ga garin mashad, haka nan tsarin mahidimta matasa shima yana cikin sauran cigaba da ya kawo a wannan harami.[13]Ayatullahi Khamna’i cikin hukuncin umarnin naɗa ra’isi kan muƙamin kula da haramin Iman Rida (a.s) da kulawa da al’amuran maziyarta, hidima ga maƙota musamman ma raunanan haramin Imam Rida (a.s) yaɗa ilimin kur’ani da mazhabar Ahlul-baiti (a.s) a duk duniya, samar da tsarin da zai taimakawa talakawan da suke cikin sassan ƙasar Iran amfana waƙafofin wannan harami mai tsarki, Kuma ya tsara harkokin tattalin arziki da sabis na wannan harami mai tsarki.

Ayyukan Siyasa

Ibrahim ra’isi bayan nasarar juyin juya halin muslunci a ƙasar Iran, tun yana ɗan shekara 20 da haihuwa ya fara kutsawa cikin ayyukan hidima ga al’umma, ya fara aiki a ma’aikatar shari’a da muƙamin majistare na yankin karaj, Na dan wani lokaci, ya kula da ofishin masu gabatar da ƙara na Hamadan..‌[14] sauran muƙaman da ya jagoranta za su iya kasancewa kamar haka:

  • Mai gabatar da kara na Tehran daga 1368 zuwa 1373.[15]
  • Shugaban Hukumar Bincike ta ƙasa ta 1373 zuwa 1383[16]
  • Shugaban Hukumar Bincike ta ƙasa ta 1373 zuwa 1383.[17]
  • Wakilin al'ummar Khorasan ta Kudu a majalisar kwararrun jagoranci tun 2005.[18]
  • Babban mai gabatar da ƙara na ƙasardaga 1393 zuwa 1394[19]
  • Memba a majalisar fayyace maslahar hukuma daga shekara 1396.
  • Shugaban Hukumar Shari'a ta Iran daga 1397 zuwa 1400.[20]
  • Shugaban ƙasar Iran tun 1400.[21]
  • Kasancewa memba a majalisar malamai ƴan gwagwarmaya a shekara 1376 bisa shawarar Ayatullahi Mahadawi Keni..[22]

Taimakawa Palasɗinu da ƴan Gwagwarmaya

Sayyid Ibrahim Raisi yana rike da kur'ani tare da karanta ayoyinsa a wajen zama na 78 na Majalisar ɗinkin Duniya.[23]

Sayyid Ibrahim ra’isi yana cikin fuskokin fitattun ƴan gwagwarmaya, a farkon fara shugabancin ƙasar Iran tare da abokanen rakiya ya yi tafiya zuwa ƙasar Siriya, a babban birnin Damashƙa ya gana da jagororin gwagwarmayar kwato ƴancin palasɗinu da ma Hizbullahi lubnan. Shi ne farkon shugaban ƙasar Iran da tun bayan yaƙin cikin gida na Siriya ya yi tafiya zuwa wannan ƙasa. A rahotan kamfanin dillancin labarai na irna, ra’isi tsawon kwanaki 165 da fara ofireshin ɗin ɗufanul al-aƙsa da kuma harin isra’ika ta kai a gazza, ya dauki matakai sama da 100 don tallafawa Gaza da kungiyoyin gwagwarmayar Falasɗinu..[24] Har ila yau, a zauren Majalisar Dinkin Duniya karo na 78, ya kebe wani bangare na jawabin nasa kan batun mamayar Palastinu da mamayar da gwamnatin yahudawan sahyoniya ta yi wa wasu sassan Lebanon da Siriya.[25]

Shin ba lokaci ba ne da za a kawo ƙarshen shekaru 75 na mamayar kasar Palasɗinu da zaluncin wannan al'ummar da ake zalunta da kisan mata da ƙananan yara da haƙƙoƙin al'ummar Palasɗinu?[26]

Kowarwa da Kuma Rubuce-rubucensa

Ibrahim ra’isi a zamanin da yake shugabancin haramin Imam Rida (a.s) a mashad ya kasance yana bada darasin bahasil karijul fiƙihu, haka kuma ya koyar da litattafan fiƙihu, ƙawa’idul fiƙihil ƙada’i da fiƙihul iƙtisad a hauzozin ilimi na tehran da jami’o’i daban-daban misalin jami’ar Imam Sadiƙ (a.s) da jami’ar shahid beheshti.[27] Sayyid Ibrahim ya walllafa taƙriri cikin darasin ƙawa’idul fiƙihi (mujalladi uku da ya ƙunshi shari’a, tattalin arziƙi da ibada) da kuma bahasin gado wanda bashi da magaji, ta’arudul asli da zahir cikin fiƙihu da doka.[28]haka nan an wallafa litattafai daban-daban cikin batutuwan haƙƙoƙi, tattalin arziƙi, fiƙihu, adalcin zamantakewa da tsarin rayuwa.[29]

Mutuwa Sakamakon Hatsarin Jirgi

Ranar 30 ga watan Urdibeheshti shekara 1403, Sayyid Ibrahim ra’isi ya yi tafiya cikin jirgi mai saukar ungulu zuwa yankin azerbaijan sharƙi domin kai shi bikin buɗe ɗaya daga cikin ayyukan raya ƙasa, cikin kan hanyarsa ta dawowa a daidai yankin da yake tsakanin garuruwan warzaƙan da julfa ya fuskanci ibtila’in hatsarin jirgi, cikin wannan jirgi mai saukar ungulu akwai Husaini Abdullahiyan ministan harkokin wajen ƙasar Iran, da kuma Sayyid Ali Ale Hashim wakilin waliyul faƙihi a garin Azerbaijan sharƙi..[30] bayan yaɗuwar labarin wannan hatsari, gungu-gungun jama’ar ƙasar Iran sun taru a wuraren ibada misalin haramin Imam Rida (a.s),[31] haramin Sayyada Ma’asuma (a.s),[32] haramin Shah Cerag domin yi musu addu’a da Allah ya kuɓutar da su.[33] washegari 31 ga watan Urdibehesti aka gano ɓaraguzan wannan jirgi da suke ciki, bayan nan kafofin yaɗa labarin ƙasar Iran suka sanar da cewa shugaban Iran tare da waɗanda suke tare sun rasa rayukansu sakamakon wannan hatsari.[34]

cikin al’adar jamhuriyar muslunci ta Iran, mutanen da suke rasa rayukansu a lokacin sauke wazifar da take wuyansu ana ƙirga su cikin shahidai, da wannan dalili ne aka kira Sayyid ra’isi da waɗanda suke kasance tare da sunan shahidai.

Tasiri da Martani

Mutuwar Raisi ta yi tasiri da martani daban-daban. Haramin Imam Rida (a.s) ya soke shirye-shiryen da ya shirya na Maulidin Imam Rida (a.s.). Har ila yau, an maye gurbin koren tutar haramin da bakar tuta, A cikin sakon ta'aziyyar nasa, Ayatullah Khamenei ya kira Raisi malamin mujahidi da rasuwarsa a matsayin shahada tare da ayyana zaman makoki na kwanaki biyar a kasar Iran.[35] Masana harkokin siyasa da na addini da suka hada da Ayatullah Sistani daga mahukuntan birnin Najaf da kuma shugabannin qasashe daban-daban sun bayyana alhininsu kan rasuwar shugaban na Iran. Haka kuma a Lebanon da Siriya na tsawon kwanaki uku[36] da qasar pakistan[37] Kuma kasar Iraqi ta ayyana ranar jama'a ranar makoki.

Bayanin kula

  1. نجفی، روایت انتخابات دوازدهم، ص۱۸۶-۱۸۸ به نقل از «روایت حجت‌الاسلام رئیسی از دوران مبارزه علیه رژیم پهلوی/ شکل‌گیری هسته‌های مبارزاتی طلاب در قم / ماجرای دیدار با آیت‌الله خامنه‌ای در ایرانشهر»، مرکز اسناد انقلاب اسلامی.
  2. «زندگینامه: سید ابراهیم رئیسی»، خبرگزاری همشهری.
  3. «سوابق و زندگینامه حجت الاسلام و المسلمین رئیسی»، خبرگزاری صداوسیما.
  4. «زندگینامه: سید ابراهیم رئیسی»، خبرگزاری همشهری.
  5. نجفی، روایت انتخابات دوازدهم، ص۱۸۶-۱۸۸ به نقل از «روایت حجت‌الاسلام رئیسی از دوران مبارزه علیه رژیم پهلوی/ شکل‌گیری هسته‌های مبارزاتی طلاب در قم / ماجرای دیدار با آیت‌الله خامنه‌ای در ایرانشهر»، مرکز اسناد انقلاب اسلامی.
  6. نجفی، روایت انتخابات دوازدهم، ص۱۸۶-۱۸۸ به نقل از «روایت حجت‌الاسلام رئیسی از دوران مبارزه علیه رژیم پهلوی/ شکل‌گیری هسته‌های مبارزاتی طلاب در قم / ماجرای دیدار با آیت‌الله خامنه‌ای در ایرانشهر»، مرکز اسناد انقلاب اسلامی.
  7. «شرح زندگی سید ابراهیم رئیسی »، پایگاه اطلاع‌رسانی سید ابراهیم رئیسی.
  8. نجفی، روایت انتخابات دوازدهم، ص۱۸۶-۱۸۸ به نقل از «روایت حجت‌الاسلام رئیسی از دوران مبارزه علیه رژیم پهلوی/ شکل‌گیری هسته‌های مبارزاتی طلاب در قم / ماجرای دیدار با آیت‌الله خامنه‌ای در ایرانشهر»، مرکز اسناد انقلاب اسلامی.
  9. «روایت حجت‌الاسلام رئیسی از دوران مبارزه علیه رژیم پهلوی/ شکل‌گیری هسته‌های مبارزاتی طلاب در قم / ماجرای دیدار با آیت‌الله خامنه‌ای در ایرانشهر»، مرکز اسناد انقلاب اسلامی.
  10. «انتصاب حجت‌الاسلام رئیسی به تولیت آستان قدس رضوی»، دفتر حفظ و نشر آثار حضرت آیت‌الله العظمی خامنه‌ای.
  11. نگاه کنید به: «انتصاب حجت‌الاسلام رئیسی به تولیت آستان قدس رضوی»، دفتر حفظ و نشر آثار حضرت آیت‌الله العظمی خامنه‌ای.
  12. «نگاهی به عملكرد سه ساله حجت الاسلام رئیسی در آستان قدس رضوی»، خبرگزاری ایرنا.
  13. نگاه کنید به: «نگاهی به عملكرد سه ساله حجت الاسلام رئیسی در آستان قدس رضوی»، خبرگزاری ایرنا.
  14. «شرح زندگی سید ابراهیم رئیسی »، پایگاه اطلاع‌رسانی سید ابراهیم رئیسی.
  15. «"Zindaginameh: Seyed Ebrahim Raisi", Kamfanin Dillancin Labarai na Hamshahri.
  16. "Zindaginameh: Seyed Ebrahim Raisi", Kamfanin Dillancin Labarai na Hamshahri.
  17. "Zindaginameh: Seyed Ebrahim Raisi", Kamfanin Dillancin Labarai na Hamshahri.
  18. "Zindaginameh: Seyed Ebrahim Raisi", Kamfanin Dillancin Labarai na Hamshahri.
  19. "Zindaginameh: Seyed Ebrahim Raisi", Kamfanin Dillancin Labarai na Hamshahri.
  20. "Zindaginameh: Seyed Ebrahim Raisi", Kamfanin Dillancin Labarai na Hamshahri.
  21. "Zindaginameh: Seyed Ebrahim Raisi", Kamfanin Dillancin Labarai na Hamshahri.
  22. «شرح زندگی سید ابراهیم رئیسی »، پایگاه اطلاع‌رسانی سید ابراهیم رئیسی.
  23. «متن کامل سخنرانی رئیسی در سازمان ملل»، انصاف‌نیوز.
  24. «بیش از۱۰۰موضع‌گیری درحمایت از غزه/ رئیسی چگونه دست مدعیان حقوق بشر را روکرد»، خبرگزاری ایرنا.
  25. «متن کامل سخنرانی رئیسی در سازمان ملل»، انصاف‌نیوز.
  26. «متن کامل سخنرانی رئیسی در سازمان ملل»، انصاف‌نیوز.
  27. "ZSindagi nameh: Seyed Ebrahim Raisi", Kamfanin Dillancin Labarai na Hamshahri.
  28. «سوابق و زندگینامه حجت الاسلام و المسلمین رئیسی»، خبرگزاری صداوسیما.
  29. "Zindagi nameh: Seyed Ebrahim Raisi", Kamfanin Dillancin Labarai na Hamshahri..
  30. «بالگرد حامل رئیس جمهور دچار سانحه شد/با ۲ نفر از سرنشینان بالگرد رئیس‌جمهور ارتباط برقرار شد»، خبرگزاری ایسنا.
  31. "Addu'ar maziyartan haramin Motahar Razavi ga lafiyar shugaban kasa da abokan tafiyarsa", kamfanin dillancin labarai na Mehr.
  32. "Yin Addu'a a Haramin Hazrat Masoumeh (A.S) domin samun lafiyar Raisi da abokan tafiyarsa", Kamfanin Dillancin Labarai na Elekht.
  33. "Addu'ar maziyarta na Shahcharagh don samun lafiyar shugaban kasa da abokansa", kamfanin dillancin labarai na Mehr.
  34. آیت‌الله رئیسی و هیئت همراه به ملکوت اعلی پیوستند، خبرگزاری تسنیم.
  35. «پیام تسلیت رهبر انقلاب اسلامی و اعلام عزای عمومی در پی درگذشت شهادت‌گونه رئیس‌جمهور و همراهان گرامی ایشان»، دفتر حفظ و نشر آثار حضرت آیت‌الله العظمی خامنه‌ای.
  36. «۳ روز عزای عمومی در سوریه اعلام شد»، خبرگزاری مهر.
  37. «ایرانی صدر کے انتقال پر پاکستان میں قومی پرچم سرنگوں»، jang.com.

Nassoshi