Istidraj

Daga wikishia


Istidraj Bada lokaci ko ɗaga ƙafa, sunna ce daga cikin sunonin Allah, haka yana nufin Allah baya gaggauta azaba ga maƙaryata, a a yana ɗaga musu ƙafa tare da b asu dama, amma su ba sa anfani da damarsu domin su koma zuwa ga Allah, sai suke yaudarar kansu da kyautatawar Allah da nimar shi, sai suke manta niman gafarar Allah, kuma suka ci gaba da saɓawa Allah, to waɗannan daga ƙarshe azabar su za ta yi muni da yawa.

Ya zo a cikin wasu hadisai cewa duk wanda baya godewa Allah kan nimar da Allah ya yi masa, kuma ya cigaba da saɓon Allah to irin wannan mutumin yana daga cikin mutanan da Allah yake ɗaga musu ƙafa domin su hankalta, amma su kuma ba sa faɗaka. malam Murtada muɗahhari ya ce, Allah baya ɗagawa mutum ƙafa akan ni'imar shi sai dai idan ya yi anfani da ita a hanyar da bata shari'a ba.

Ma'anar Ɗaga Ƙafa

Imam Sadiƙ (A.S)


العبد يذنب الذنب فيُملَى له وتُجدَّد له عندها النعم، فتُلهيه عن الاستغفار من الذنوب فهو مستدرَج مِن حيث لا يعلَم.
Imam Sadiƙ (A.S) ya ce, bawa yana aikata saɓo, sai Allah ya ɗaga mishi ƙafa kuma yana ƙara mishi ni'ima, amma sai wannan ni'imar ta shagaltar da shi daga barin istigfari, to shi yana daga cikin waɗanda Allah yake ɗagawa ƙafa amma yadda bai sani ba.



[1]



Shi istidraji ɗaga ƙafa ko bada dama kalma ce wacce aka ciro ta daga cikin kur'ani mai girama, na farko aya ta 182 a cikin suratul A'araf, karo na biyu kuma aya ta 44 a cikin suratul ƙalam.[2] shi ɗaga ƙafa ko bada dama a cikin yara larabci yana nufin kusantar wani abu ko guri kaɗa-kaɗan[3] amma a gurin kwararru yana nufin ɗaya daga cikin sunnoni na Allah, kuma yana nufin Allah zai azabtar da azzalumai da masu saɓo masu keta haddin Allah da gangan, amma fa da sannu-sannu zai azabtar da su. kuma duk lokacin da suka so su yi zalinci da girman kai, Allah zai ƙara musu ni'ima, domin su kara girman kai da shagalta kan cewar Allah zai azabtar da su, kuma a ƙarshe Allah zai musu azaba mai tsanani.[4]

Ayoyin da suke bada dama ga mai zunubi

Akwai ayoyi da yawa da suka yi magana kan Istidraji kai tsaye ko saɓanin haka,[5] wato ɗaga ƙafa da bada dama wasu ayoyi ya zo da kalmar Imhal wato jinkirtawa ko bada dama, kamar aya ta 17 a cikin suratut ɗariƙ:"فَمَهِّلِ الْكافِرينَ أَمْهِلْهُمْ رُوَيْداً ka bawa kafirai dama wace za ta zo kaɗan-kaɗan a wasu daga cikin ayoyin kuma da kalmar Imla'a da aya ta 178 a cikin suratu Ali-Imran:

وَلاَ يَحْسَبَنَّ الَّذِينَ كَفَرُوا أَنَّمَا نُمْلِي لَهُمْ خَيْرٌ لِأَنْفُسِهِمْ إِنَّمَا نُمْلِي لَهُمْ لِيَزْدَادُوا إِثْماً وَلَهُمْ عَذَابٌ مُهِينٌ

kada waɗanda suka kafurce su yi tinanin muna basu dama,wato mana ɗaga musu ƙafa, su yi tinanin hakan alheri ne gare su, a a ba haka bane, kawai mu muna basu dama ne domin su kara laifi ne da kuma zunubi, kuma a gobe ƙiyama za su sha azaba mai ƙasƙantarwa.[6]

Sunnar Jinkirta Azaba Ta Ƙunshi Al'ummu Daban-daban

Wasu masu binciken kur'ani sun ce sunnar jinkirta azaba ba abu bane da ya keɓantu ga mutane ɗaiɗaiko ba, a'a abu ne da yashafi al'ummu daban-daban,sun faɗa hakan bisa dogaro kan aya ta 48 a cikin suratul Haj,

وَكَأَيِّنْ مِنْ قَرْيَةٍ أَمْلَيْتُ لَها وَهِيَ ظالِمَةٌ ثُمَّ أَخَذْتُها وَإِلَيَّ الْمَصيرُ

Kuma babu wata alƙarya da Na yi jinkiri gare ta, alhali kuwa tana zalunci, sa'an nan na kama ta, kuma zuwa gare ni makoma take.[7]

Alamomin Jinkirta Azaba

Haƙiƙa yazo cikin ruwayoyi da maganar wasu malamai wasu daga cikin alamomin jinkirta azaba ga su kamar haka;

  • Gafalta Kan Yin Istigfari

Kulaini ya rawaito daga Imam Sadiƙ (A.S) cewa haƙiƙa idan Allah ya so bawan shi da alheri zai sa shi ya yi wani zunubi wato laifi sai kuma Allah ya yi mishi wata ni'ima, kuma ya sa shi ya tina neman gafara, idan kuma Allah ya so bawa da sharri sabo da abin da ya zaɓa da kan shi ya yi, sai ya yi wani zunubi laifi, sai Allah ya yi mishi wata ni'ima domin ya mantar da shi neman gafarar Allah kuma zai cigaba da saɓo alhalin yana cikin ni'imar Allah. Kamar yadda wata magana ta Imam Sadiƙ (a.s) ta yi dai-dai da maganar Allah madaukaki, faɗar Allah; da sannu za mu jinkirta musu azaba ta fuskacin da basu sani ba.[8] wato Allah zai jinkirta musu azaba a yayin da suke saɓo a lokacin da suke cikin ni'ima.

  • Rashin godiyar Allah

Ya zo a wani hadisin daga Imam Sadiƙ (a.s) cewa; ni'ima idan ba'a gode mata ba, to lalle mutumin da yake haka to ya jira azabar Allah, sai wanda ya rawaito ruwayar ya ce, na faɗawa Aba Abdillah na roki Allah Madaukakin Sarki Ya ba ni dukiya, kuma ya ba ni, kuma na roki Allah ya ba ni ɗa, ya ba ni ɗa, na ce ya bani gida. Ya ba ni gida ya azurta ni, sai na ji tsoron kada wannan ya zama yaudara, sai ya ce: “Na rantse da Allah, matukar kana godiya, to a'a ba zai zama istidraji ba.”[9]

  • Samun Damar Yin Wani Abu Da Saɓawa Abin Da Aka Saba da Shi

Fakhrur Razi daya daga cikin malaman tafsiri na ahlus-sunna da malamin tauhidi a karni na shida ya yi imani da cewa samun damar da mutane masu aikata saɓo suke yi na yin wani abu ya saɓawa wa al'ada yaudara ne.[10]

  • Anfani Da Ni'ma Cikin Hanya Ta Haramun

Murtada Motahhari ya ce: Istidraji baya haduwa tare da ni'ima sai idan ma'abcoin ni'ima ya yi amfani da ita a hanyar haramun, ko kuma ya yi almubazzaranci ko ruduwa da ita.[11]

Bayanin kula

  1. Kulaini,AL-kafi,j 2 shafiu na 4252
  2. Makarem Al-Shirazi, Al-Amsal, juzu'i na 5, shafi na 311..
  3. Tabatabai, Al-Mizan, juzu'i na 8, shafi na 346.
  4. Makarem Al-Shirazi, Al-Amsal, juzu'i na 5, shafi na 313..
  5. Mamouri, "Barasi Sunnat Istidraj dar Kur'an wa mirasi tafsiri", shafi na 105.
  6. Tabatabai, Al-Mizan, juzu'i na 4, shafi na 79.
  7. Mamouri, “Barasi sunnat Istidarj dar Kur'an wa miras tafsiri” shafi na 115.
  8. Kulaini Kafi, juzu'i na 2, shafi na 452.
  9. Kulaini Kafi, juzu'i na 2, shafi na 97.
  10. Al-Razi, Mafiatihul al-Ghaib, juzu'i na 21, shafi na 431.
  11. Motahari,Majmu Asare, juzu'i na 27, shafi na 626.

Nassoshi

  • Al-Tabatabai, Mohammad Hossein, "Al-Mizan in Tafsir al-Qur'an", Beirut - Lebanon, mawallafi: Est
  • Al-Razi, Muhammad bin Omar, "Mufatih al-Gheeb", Beirut - Lebanon, mawallafi: Dar Ihya al-Tarat al-Arabi, juzu'i na 3, 1420H.
  • Al-Kulaini, Muhammad bin Yaqoob, "Al-Kafi", al-Haqq: Ali Akbar al-Ghafari, Tehran - Iran, mawallafi: Dar al-Kutub al-Islamiyya, juzu'i na 4, 1407H.
  • Motahari, Morteza, ""Majmu Asare", Tehran - Iran, Mawallafi: Sadra, Mujalladi na 14, 1390.
  • Ma'amouri, Ali, "Barasi Sunnat Istidaraje dar Kur'an wa mirase tafsiri", "Alkur'ani da Hadisi", No. 1, 1386.
  • Marafa, Mohammad Hadi, "Al-Tamhid fi Ulum Al-Qur'an", Qom - Iran, Al-Nasher: Est.
  • Makaram Al-Shirazi, Nasser, "Al-Amsal fi Tafsir Kitab Allah al-Manzil", fassarar Muhammad Ali Azarshab, Qum - Iran, mawallafi: Madrasah Al-Imam Ali bin Abi Talib , juzu'i na 1. 1421 AH.