Daƙiƙa:Yaumul Hasra
Ranar Baƙin Ciki (Yawmul Hasrah) ɗaya ce daga cikin sunayen ranar tashin alƙiyama,[1] kuma tana nufin ranar baƙin ciki, nadama da yanke ƙauna.[2] Wannan sunan ya zo a cikin aya ta 39 na surat Maryam.
Malaman tafsiri sun yi imanin cewa dalilin sanyawa ranar tashin alƙiyama suna "Ranar Baƙin Ciki" shi ne, domin a wannan rana, bayan bayyana sakamakon ayyukansu, mutane za su gane kura-kurai da sakacinsu a rayuwar duniya.[3] Rasa damar yin ayyukan alheri da samun ladar Allah suma suna daga cikin abubuwan da ke jawo baƙin ciki da nadama.[4] A cewar Fadlu Bin Hassan Ɗabrisi a cikin Majma'ul Bayan, baƙin ciki a ranar alƙiyama ba ya taɓa masu zunubi kaɗai, a'a, masu ayyukan alheri ma suna jin baƙin ciki domin rashin yin ayyukan alheri da yawa da za su iya yi.[5]
A cikin Alƙur'ani, an ambaci abubuwa da yawa a matsayin dalilan baƙin ciki a ranar alƙiyama, kamar: girman kai, izgili,[6] kashe dukiya a hanyar saɓawa addini,[7] ƙaryata tashin kiyama ko sakaci game da ita,[8] da barin imani da ayyukan ƙwarai.[9] Haka kuma, a cikin wasu hadisai, an ambaci abubuwa kamar: halartar majalisun da ba a ambaton Allah ko Ahlul-Baiti (A.S) a cikinsu ba,[10] samun dukiya ba tare da bin umarnin Allah ba,[11] yabon adalci ba tare da aiki da shi ba,[12] da fifita muradun duniya na wasu a kan farin ciki na lahira,[13] samun dukiya ba tare da bin umarnin Allah ba, a matsayin abubuwan da ke jawo nadama da baƙin ciki a ranar kiyama.
Bayanin kula
- ↑ Makarim Shirazi, Tafsir Namuna, juzu’i na 13, shafi na 86.
- ↑ Raghib Isfahani, Mufradat, ƙarƙashin kalmar "Hasrah".
- ↑ Shaik Ɗusi, At-Tibyan, Dar Ihya’ at-Turath al-Arabi, juzu’i na 7, shafi na 127; Allama Tabataba’i, Al-Mizan, juzu’i na 14, shafi na 51.
- ↑ Kashani, Manhaj as-Sadiqin, juzu’i na 5, shafi na 408.
- ↑ Ɗabrisi, Majma’ al-Bayan fi Tafsir al-Qur’an, juzu’i na 6, shafi na 795.
- ↑ Bani Hashimi KhomAini, Risalat Tawdhih al-Masa’il Maraji, juzu’i na 1, shafi na 584.
- ↑ Suratul Anfal, aya ta 36.
- ↑ Suratul An'am, ayoyi na 29 zuwa 31; Suratul Anbiya, aya ta 97.
- ↑ Suratul An'am, aya ta 27; Suratul Ahzab, aya ta 66.
- ↑ Majlisi, Bihar al-Anwar, juzu’i na 75, shafi na 468.
- ↑ HuwaIzi, Nur ath-Thaqalayn, juzu’i na 1, shafi na 152.
- ↑ Faizul Kashani, At-Tafsir as-Safi, juzu’i na 1, shafi na 430.
- ↑ Majlisi, Bihar al-Anwar, juzu’i na 27, shafi na 186.
Nassoshi
- Huwaizi, Abdul Ali Bin Juma, Tafsir Nur ath-Thaqalayn, Qum, Matba’at al-Ilmiyya, 1963M.
- Ragib Isfahani, Husain Bin Muhammad, Mufradat Alfaz al-Qur’an, Beirut, Dar ash-Shamiyya, 1992M.
- Shaik Ɗusi, Muhammad Bin Hassan, At-Tibyan fi Tafsir al-Qur’an, bincike: Ahmad Ƙasir Amili, Beirut, Dar Ihya at-Turath al-Arabi, babu shekara.
- Ɗabaɗaba’i, Sayyid Muhammad Husaini, Al-Mizan fi Tafsir al-Qur’an, Beirut, Cibiyar al-A’lami lil-Matbu’at, 1970M.
- Tabarsi, Fadlu Bin Hassan, Majma’ al-Bayan fi Tafsir al-Qur’an, Beirut, Dar al-Ma’rifa, 1986M.
- Faiz Kashani, Muhsin, At-Tafsir as-Safi, Qum, Cibiyar al-Hadi, 1995M.
- Kashani, Mulla Fathullah, Manhaj as-Sadiqin fi Ilzam al-Mukhalifin, Tehran, Shagon syar da litattafan Musulunci, 1957M.
- Majlisi, Muhammad Baqir, Bihar al-Anwar al-Jami’a li Durar Akhbar al-A’immah al-Athar, Beirut, Dar Ihya at-Turath al-Arabi, bugu na biyu, 1983M.
- Makarim Shirazi, Nasir, Tafsir Namuna, Tehran, Dar al-Kutub al-Islamiyya, 1995M.