Daƙiƙa:Masallacin Jamkaran
Wannan labarin yana magana ne kan Masallacin Jamkaran, don haka idan ana so a duba ƙauyen Jamkaran sai a koma zuwa shigar Jamkaran (Ƙauye).
| Kafawa | Ƙarni na huɗu na Hijirar (bisa ra'ayin Muhaddis Nuri). |
|---|---|
| Mai amfani | Masallaci |
| Wuri | Qom |
| Sauran sunaye | Masallacin Sahibuz Zaman●Masjide Ƙadamga |
| Salon | Na Iran da Musulunci |
| Sabunta gini | A daurori daban-daban |
| Shafin yanar gizo | پایگاه مسجد جمکران |
Masallacin Jamkaran wani masallaci ne da ake dangantawa da Imam Mahadi (A.F), Imam na goma sha biyu a wajen Shi'a, wanda aka ce an gina shi a ƙarni na huɗu na hijira a gefen birnin Qom. Bisa rahoton Mirza Husaini Nuri, malamin hadisi a ƙarni na goma sha uku na hijira, an gina wannan masallaci ne da umarnin Imam Mahadi (A.F) ta hannun wani malami daga Qom mai suna Abul Hassan. Muhaddis Nuri ya ruwaito wani labari da ya ce Hassan Bin Musla Jamkarani ya gana da Imam Mahadi (A.F), kuma Imam ɗin ya umarce shi da a gina Masallacin Jamkaran. Mirza Husaini Nuri ya bayyana cewa wannan abin ya faru a shekara ta 373 ko 393H, kuma ya danganta ruwayar zuwa littafin Mu'unisul Hazin na Shaik Saduƙ.
Sai dai wasu masu bincike sun nuna shakku kan danganta wannan masallaci ga Imam Mahadi (A.F), suna kawo hujjoji kamar rashin ambaton wannan littafi a cikin littattafan ilimin rijal na Shi'a, da kuma rashin samuwar wannan labari a sauran rubuce-rubucen Shaik Saduƙ.
A wannan masallaci ana gudanar da bukukuwa da ibadu daban-daban kamar bikin rabin Sha'aban, Du'a'u Tawassul da Du'a'u Nudba. Mutane daga sassa daban-daban na Iran da ma sauran ƙasashe suna zuwa Masallacin Jamkaran.
An yi gyare-gyare da sabuntawa ga masallacin a lokuta daban-daban. Tsohon rubutu mafi daɗewa da aka samu yana nuna gyara a shekara ta 1167H. Har zuwa kafin juyin juya halin Iran na 1979M, masallacin ƙarami ne, amma daga baya ya faɗaɗa sosai. Rukunin Masjid Jamkaran ya haɗa da fili na waje, babban farfajiya, ɗakunan sallah, masjide maƙam da gine-ginen gudanarwa.
Akwai ibadu na musamman da aka ruwaito ga wannan masallaci, kamar raka'o'i biyu na sallar gaisuwar masallaci da kuma raka'o'i biyu na sallar Imam Zaman. Muhaddis Nuri ya danganta waɗannan ibadu ga Imam Mahadi (A.F), kuma Shaik Abbas Ƙummi ya kawo su daga gare shi a cikin Mafatih al-Jinan.
Wuri Da Suna
Masallacin Jamkaran shi ne masallaci da ake dangantawa da Imam Mahadi (A.F),[1] wanda yake a gefen birnin Qom kuma yana da nisan kusan kilomita 8 daga haramin Sayyida Ma'asuma (A.S).[2] An yi wa wannan masallaci suna ne saboda kusancinsa da ƙauyen Jamkaran, shi ya sa aka fi saninsa da wannan suna.[3]
A da can wannan masallaci ana kiran sa da Masjide Ƙadamga (masallacin wurin takun sawu), saboda wani dutse mai marmara da ake ɗauka a matsayin wurin da Imam na goma sha biyu na Shi'a ya taka sawu.[4]Ana kiran sa da Masjid Ƙadamga a baya.[5] Haka kuma, saboda dangantarsa da Imam Zaman (A.S),[6] ana kiran shi da Masjide Sahibiz Zaman.[7]
Dangantawa Da Imam Mahadi (A.F)
Bisa ruwayar Mirza Husaini Nuri (ya rasu: 1320H), ɗaya daga cikin malamai masu ruwayar hadisi na Shi'a, an ce Masallacin Jamkaran an gina shi ne a ƙarni na huɗu na hijira da umarnin Imam Mahadi (A.F), kuma wani malami daga Qom mai suna Sayyid Abul Hassan ne ya gina shi.[8]
Muhaddis Nuri ya ruwaito daga Hassan Bin Musla Jamkarani cewa ya ce a daren Talata, 17 ga watan Ramadan, shekara ta 393H, ya haɗu da Imam Zaman (A.F) a wurin da daga baya aka gina Masallacin Jamkaran. Imam ɗin ya ba shi umarni biyu: na farko, a nemi Hassan Bin Muslim ya daina noma wannan ƙasa saboda ƙasa ce mai daraja, wacce ya haɗa da gonarsa ba bisa ƙa'ida ba. Na biyu, a gaya wa Sayyid Abul Hassan (ɗaya daga cikin malaman Qom) ya yi amfani da kuɗin da Hassan Bin Muslim ya samu daga noman shekarun baya wajen gina masallaci a wannan wuri.[9]
Bisa wannan ruwaya, bayan wannan lamari Sayyid Abul Hasan ya gina masallaci mai rufi na itace a wurin da aka riga aka iyakance ta hannun Imam Zaman (A.F).[10][Tsokaci 1]
Majiyoyin Labarin
An ruwaito labarin gina Masallacin Jamkaran a cikin littattafan Muhaddis Nuri kamar Kalimate Ɗayyiba,[11] Najmus Saƙib,[12] Mustadrakul Wasa'il,[13] da Jannatul Ma'awa.[14] Muhaddis Nuri ya danganta wannan labari zuwa littafin Tarikhe Qom, kuma ya rubuta cewa Tarikhe Qom ya naƙalto shi daga littafin Mu'unisul Hazin Fi Ma'arifatil Haƙƙi Wa Al-Yaƙin na Shaik Saduƙ.[15]
Haka kuma Muhaddis Nuri a cikin Mustadrakul Wasa'il, ya ce ya ga wannan labari a cikin ƙarin bayani (hashiya) na littafin Naƙdir Rijal da aka rubuta da hannun Muhammad Ali Bihbahani (ya rasu: 1216H), wanda kuma ya danganta shi zuwa Mu'unisul Hazin.[16]
Shakku Kan Labarin
Muhaddis Nuri (ya rasu: 1320H) ya kawo cewa shekarar gina masallacin a wasu littattafansa ita ce 393H,[17] a wasu kuma 373H.[18] Nasirush Sharia, marubucin Tarikhe Qom, ya kawo tsammanin cewa wannan lamari ya faru kusan shekaru 100 kafin hakan, a shekara ta 293H.[19] Muhaddis Nuri ma ya ambaci wannan shekara a cikin hashiya na Naƙdur Rijal.[20]
Wasu masu bincike sun yi shakku kan ingancin danganta Masallacin Jamkaran da Imam Zaman (A.F). Ali Duwani ya nuna cewa rashin ambaton littafin Mu'unisul Hazin a cikin littattafan rijal, rashin samuwar wannan labari a cikin bugu biyar na Tarikhe Qom, da kuma rashin ambaton Shaik Saduƙ a wasu rubuce-rubucensa, suna daga cikin hujjojin da ke sa a yi shakku kan wannan ruwaya.[21]
Ayyukan Ibada Na Masallacin Jamkaran
An ambaci salloli biyu masu raka'a biyu-biyu na musamman ga Masjid Jamkaran: sallar gaisuwar masallaci da kuma sallar Imam Zaman.[22]
- Sallah ta farko, wato sallar gaisuwar masallaci, ana karanta Suratul Fatiha sau ɗaya da Suratul Iklasi sau bakwai a kowace raka'a. Haka kuma ana maimaita zikirin ruku'u da sujjada sau bakwai-bakwai.[23]
- Sallah ta biyu kuwa ana yin ta da niyyar sallar Imam Zaman. A kowace raka'a, ana maimaita ayar Iyyaka na'abudu wa iyyaka nasta'in sau ɗari,[24] sannan a ci gaba da karanta sauran Suratul Fatiha tare da Suratul Ikhlasi sau ɗaya. Bayan haka, ana maimaita zikirin ruku'u da sujjada sau bakwai-bakwai. Bayan an yi sallama, ana karanta La Ilaha Illallah sau ɗaya, sannan a yi Tasbihin Sayyida Zahra (S). Daga nan mai sallah zai yi sujjada ya aika salati sau ɗari ga Annabi (S.A.W).[25]
Muhaddis Nuri ya danganta waɗannan ayyukan ibada ga Imam Zaman (A.S), kuma ya ruwaito daga gare shi cewa: Mutane su riƙa ƙaunar wannan wuri kuma su girmama shi. Kamar yadda ya rubuta, duk wanda ya yi waɗannan raka'o'i huɗu a Masallacin Jamkaran, kamar ya yi sallah ne a cikin Ka'aba.[26]
Shaik Abbas Ƙummi ya kawo waɗannan ayyukan ibada a cikin Mafatihul Jinan, yana naƙalto su daga malaminsa Muhaddis Nuri.[27]
Ali Duwani, masanin tarihi da bincike, saboda shakkun da ya nuna game da danganta Masjid Jamkaran da Imam Mahadi (A.F), ya kuma nuna shakku game da danganta waɗannan ayyukan ibada gare shi.[28]
Tarihi Da Sauye-sauye

Tarihi da sauye-sauye Bisa wani labari da Mirza Husaini Nuri ya ruwaito, ginin Masallacin Jamkaran yana komawa ne zuwa ƙarni na huɗu na hijira.[29] Sayyid Husaini Mudarassi Ɗabaɗaba'i ya yi hasashen cewa Masallacin Jamkaran shi ne dai Masallacin Khaɗɗab Asadi da aka ambata a cikin Tarikhe Qom, wadda aka ce an gina ta a ƙauyen Jamkaran a farkon ƙarni na biyu na hijira.[30][Tsokaci 2] Sai dai wasu masu bincike sun yi imanin cewa Masallacin Jamkaran ba shi ne wannan masallaci ba, kuma bisa ruwayar Muhaddis Nuri suna ganin an gina shi ne a ƙarni na huɗu na hijira.[31]
Duk da haka, babu cikakkun bayanai game da Masallacin Jamkaran a cikin tsofaffin majiyoyin tarihi. Abin da aka samu kawai shi ne a littafin Khulasatut Tawarikh, inda a yayin bayanin abubuwan da suka faru a shekara ta 98H, an ambaci cewa Mir Ghiyasud-Din Muhammad Mirmiran, lokacin da yake sauka a ƙauyen Lanjarud na Qom, wani lokaci yana yin itikafi a wani wuri a Jamkaran da ake kira Maƙame Imam Zaman.[32]
A cewar Ali Asgar Faƙihi, masanin tarihin zamani, abin da ake nufi da wannan maƙam shi ne Masallacin Jamkaran.[33]
Faɗaɗa Ginin A Jamhuriyar Musulunci

Bayan Juyin Juya Halin Musulunci na Iran a shekara ta 1357Sh (1979M), Majalisar Gudanarwar Hauzar Ilmi ta Qom ta gabatar da membobin kwamitin amintattu na Masallacin Jamkaran, sannan Hukumar Waƙfai da Harkokin jin ƙai ta ɗauki nauyin sa ido kan harkokin wannan masallaci.[34] Daga wannan lokaci ne aikin faɗaɗa masallacin ya samu sauri.
Bayan haka, an ware hekta 40 na ƙasa domin Masallacin Jamkaran, inda hekta 5.5 daga cikinsu aka keɓe don haraba da babban filin masallacin.[35]
Har ila yau, a shekara ta 1382Sh, an amince da wani sabon tsari na bunƙasa harabar Masallacin Jamkaran, wanda ya tanadi kusan hekta 250 na ƙasa ga wannan cibiya. Daga cikin wannan fili, kusan murabba'in mita 30,000 an ware su ga Masjide Maƙam da ɗakunan sallah, yayin da sauran filayen suka kasance na haraba, gine-ginen gudanarwa da kuma wuraren hidima. A cikin wannan shiri, an sake gina dukkan gine-ginen masallacin, ban da Masjide Maƙam.[36]
Ana gudanar da Masjid Jamkaran ta hannun sassa daban-daban, kamar: Sashen bukukuwa da wa'azi, hulɗa da jama'a, ɗakin karatu, sashen wallafe-wallafe, sashen rajistar karamai, da sashen karɓar nazirce-nazirce da kyaututtuka.
A halin yanzu, Sayyid Ali Akbar Ojaƙnejad ne ke riƙe da muƙamin mai kula da Masallacin Jamkaran.[37] Kafin shi kuwa, Muhammad Husaini Rahimiyan da Abul Ƙasim Wafi ne suka riƙe wannan muƙami..[38]
Gine-gine da Tsarin Gini
Ƙungiyar Masallacin Jamkaran ta ƙunshi sassa daban-daban kamar Masjide Maƙam, ɗakunan sallah, babban filin masallaci, da kuma gine-ginen gudanarwa da na hukumomi.

Masjide Maƙam
Babban ginin ɗakin sallah na Masallacin Jamkaran ana kiransa Masjide Maƙam, wanda ke da faɗin kusan murabba'in mita 1100. Ƙofar shigarsa tana haɗe da ɗakin sallah ta hanyoyin shiga uku, kuma a gefen wannan ƙofa akwai manara biyu masu tsayin kusan mita 60.
Wannan ɗakin sallah yana da ginshiƙai takwas, inda ƙubbar masallacin ke zaune a kan su ta hanyar tsarin ƙarfe. A cikin ƙasan ƙubbar an saka tagogi 23 waɗanda ke ba da haske ga cikin ɗakin sallah.
Fuskar waje ta ƙubbar an lulluɓe ta da tayal masu launin shuɗi-firuzai, sannan an ƙawata ta da rubuce-rubucen tahlil da kuma zane-zanen ado da ke ɗauke da kalmar Ya Mahadi adrikni. Cikin ƙubbar kuma an yi ado da tayal masu zane-zane na muraƙƙa tare da haɗa su da tubali.
Haka kuma ginshiƙai, mihrabi, ƙofar shiga ɗakin sallah, da manarori biyu da ke gefensa an ƙawata su da tayal na ado da kuma zane-zanen muƙarnas.[39]
Babban Filin Masallaci
Masallacin Jamkaran yana da ƙofofi shida, inda ƙofar arewa maso gabas ke kaiwa kai-tsaye zuwa babban ɗakin sallah na masallaci.[40] A kewayen filin masallacin an gina manarori, kuma bisa bayanin jami'an masallacin, ana shirin kai adadinsu zuwa 14.[41]
Ɗakunan Sallah (Shabistan)
- Shabistan na yamma da gabas: A gefen Masjide Maƙam akwai ɗakunan sallah biyu, kowanne yana da faɗin kusan murabba'in mita 4000, kuma an gina su a matakai biyu (bene biyu). Cikin waɗannan ɗakuna an yi ado da madubai, kuma kowanne yana da ƙubbobi biyu masu daidaito.[42]
Rijiyar Neman Buƙata (Rijiyar Arize)

A wajen harabar masallaci, a bayan ginin Masjide Maƙam, akwai wani rijiya da ake kira Chahe Arize (rijiyar wasiƙa/buƙata).[43]
Wasu daga cikin Shi'a suna da imani da tsarkinta, kuma suna jefa rubuce-rubuce ko wasiƙu zuwa ga Imam Zaman a cikinta.[44] Sai dai wasu masu bincike sun bayyana cewa babu wata hujja ko takardar sahihanci game da wannan rijiya, kuma babu wani daga cikin maraji'an taƙlidi (manyan malamai) da ya tabbatar mata da wata daraja ta musamman.[45]
Ayatullahi Khamna'i, jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran,[46] da Ayatullahi Makarim Shirazi,[47] sun bayyana rashin goyon bayansu ga jefa wasiƙu cikin wannan rijiya.
Haka kuma an ruwaito cewa a cikin mihrabin masallaci akwai wata ƙaramar rijiya, inda wasu masu ziyara ke ɗaukar ƙasa don neman albarka. A cikin mihrabi kuma akwai wani dutse da aka sassaka da siffar sawun ƙafa, a matsayin alamar cewa masallacin gidan sawun ƙafa ne. Sai dai a shekarar 1350H, bisa umarnin Faizul Ƙummi (ya rasu 1370H), an lalata shi saboda kasancewa alama ta bidi'a.[48]
A cewar wasu rahotannin kafafen labarai, wannan rijiya an rufe ta a watan Nuwamba na shekara ta 1399Sh.[49]
Batutuwa Masu Alaƙa
Bayanin kula
- ↑ Nuri, Jannatul Ma'awa, shafi na 54–58; Nuri, Najmus Saƙib, juzu'i na 2, shafi na 454–458; Nuri, Kalimate Ɗayyiba, shafi na 682–686.
- ↑ Khan Muhammadi, «Chahe Arizeye Jamkaran; az khorafeh ta Waƙe'iyat,» shafi na 162.
- ↑ Arab, «Masjide Jamkaran,» shafi na 747.
- ↑ Nasirush Sharia, Tarikhe Qom, shafi na 233.
- ↑ Faize Ƙummi, Ganjineye Asare Qom, juzu'i na 2, shafi na 667, daga: Arab, «Masjide Jamkaran,» shafi na 747.
- ↑ Arab, «Masjide Jamkaran,» shafi na 747.
- ↑ Mudarrasi Ɗabaɗaba'i, Turbate Pakan, juzu'i na 2, shafi na 164.
- ↑ Nuri, Jannatul Ma'awa, shafi na 54–58.
- ↑ Nuri, Jannatul Ma'awa, shafi na 54–58.
- ↑ Nuri, Jannatul Ma'awa, shafi na 54–58; Nuri, Najmus Saƙib, juzu'i na 2, shafi na 454–458; Nuri, Kalimate Ɗayyiba, shafi na 682–686.
- ↑ Nuri, Kalimate Ɗayyiba, shafi na 682–686.
- ↑ Nuri, Najmus Saƙib, juzu'i na 2, shafi na 454–458.
- ↑ Nuri, Mustadrakul Wasa'il, juzu'i na 3, shafi na 447..
- ↑ Nuri, Jannatul Ma'awa, shafi na 54–58
- ↑ Nuri, Jannatul Ma'awa, shafi na 54.
- ↑ Nuri, Mustadrakul Wasa'il, juzu'i na 3, shafi na 432 da 447.
- ↑ Nuri, Jannatul Ma'awa, shafi na 54–58 da 383–388; Nuri, Kalimate Ɗayyiba, shafi na 682–686.
- ↑ Nuri, Mustadrakul Wasa'il, juzu'i na 3, shafi na 447; Nuri, Najmus Saƙib, juzu'i na 2, shafi na 458.
- ↑ Nasirush Shari'a, Tarikhe Qom, shafi na 239.
- ↑ Nuri, Najmus Saƙib, juzu'i na 2, shafi na 458.
- ↑ Nasirush Sharia, Tarikhe Qom, shafi na 29–30.
- ↑ Nuri, Jannatul Ma'awa, shafi na 56; Nuri, Kalimate Ɗayyiba, shafi na 684.
- ↑ Ƙummi, Kulliyyate Mafatihil Jinan, Sallar Masallacin Jamkaran, shafi na 427–429.
- ↑ Suratul Hamd, aya ta 5.
- ↑ Nuri, Jannatul Ma'awa, shafi na 55–56; Nuri, Najmus Saƙib, juzu'i na 2, shafi na 456; Ƙummi, Kulliyyate Mafatihil Jinan, Sallar Masallacin Jamkara, shafi na 427–429.
- ↑ Nuri, Jannatul Ma'awa, shafi na 56; Nuri, Kalimate Ɗayyiba, shafi na 684; Ƙummi, Kulliyyate Mafatihil Jinan, Sallar Masallacin Jamkara, shafi na 429.
- ↑ Ƙummi, Kulliyyate Mafatihil Jinan, Sallar Masallacin Jamkaran, shafi na 427–429.
- ↑ Nasirush Sharia, Tarikhe Qom, shafi na 30.
- ↑ Nuri, Jannatul Ma'awa, shafi na 54–58; Nuri, Jannatul Ma'awa, juzu'i na 2, shafi na 454–458; Nuri, Kalimate Ɗayyiba, shafi na 682–686.
- ↑ Modarassi Ɗabaɗaba'i, Turbate Pakan, juzu'i na 2, shafi na 163–164.
- ↑ Faƙihi, Tarikhe Mazhabiye Qom, shafi na 272.
- ↑ Munshi Ƙummi, Khulasatut Tawarikh, juzu'i na 2, shafi na 1019, daga: Daneshnameh-ye Jahane Islam, shafin Masallacin Jamkaran, shafi na 747.
- ↑ Faƙihi, «Qom Dar Masire Tarikh,» shafi na 171, daga: Daneshnameh-ye Jahane Islam, shafin Masallacin Jamkaran, shafi na 747.
- ↑ Zandiyye, «Masjide Jamkaran,» shafi na 80, daga: Daneshnameh-ye Jahane Islam, shafin Masallacin Jamkaran, shafi na 748.
- ↑ Zandiyye, «Masjide Jamkaran,» shafi na 78, daga: Daneshnameh-ye Jahane Islam, shafin Masallacin Jamkaran, shafi na 749.
- ↑ Arab, «Masjide Jamkaran,» juzu'i na 10, shafi na 749.
- ↑ «انتصاب حجتالاسلام اجاقنژاد به تولیت مسجد مقدس جمکران»، Ofishin Hifze Wa Nashre Asare Hazrate Ayatullahi al-Uzma Khamna'i.
- ↑ «تولیت مسجد مقدس جمکران»، shafin yanar gizo na Masjide Muƙaddase Jamkaran.
- ↑ Arab, «Masjide Jamkaran,» juzu'i na 10, shafi na 749.
- ↑ «معماری مسجد مقدس جمکران؛ دومین مقصد گردشگری مذهبی در قم»، Shafin yanar gizo na Rahnamaye Sare Man.
- ↑ «توسعه مسجد جمکران نیازمند ۱۷۰ میلیارد تومان اعتبار است»، Shafin yanar gizo na Masjide Muƙaddase Jamkaran.
- ↑ Arab, «Masjide Jamkaran,» juzu'i na 10, shafi na 749.
- ↑ Khan Muhammadi «Chahe Arizeye Jamkaran; az khorafeh ta Waƙe'iyat,» shafi na 162.
- ↑ Khan Muhammadi, «Chahe Arizeye Jamkaran; az khorafeh ta Waƙe'iyat,» shafi na 163.
- ↑ Khan Muhammadi, «Chahe Arizeye Jamkaran; az khorafeh ta Waƙe'iyat,» shafi na 175.
- ↑ Masih Dar Shabe Ƙadr, shafi na 431.
- ↑ «چاه عریضه در مسجد جمکران»، Shafin watsa bayanai na Ayatullah Makarim Shirazi.
- ↑ Faize Ƙummi, Ganjineye Asare Qom, juzu'i na 2, shafi na 668, an naƙalto daga: Daneshnameh-ye Jahane Islam, shafin Masallacin Jamkaran, shafi na 748.
- ↑ «چاه مسجد جمکران موقتا بسته شد»، Kamfanin Dillancin Labarai na Taƙrib,«چاه مسجد جمکران بسته و تخریب شد»، Shafin yanar gizo Shi'are Sal.
Tsokaci
- ↑ Bisa ruwayar Muhaddith Nuri, Hassan Bin Musla Jamkarani ya ce a wannan tattaunawa da Imam Zamana (a.s.), ya roƙi Imam ya sanya masa wata alama domin mutane su gaskata maganarsa. Imam ya amsa da cewa: Ka je ka aiwatar da wannan umarni, kuma za mu sanya muku wasu alamu. Haka kuma Imam ya ce akwai wata akuya a garken Jafar Kashani da za a yanka a wannan wuri, a rarraba naman ga marasa lafiya, kuma duk wanda ya ci daga naman zai warke da izinin Allah. Haka nan, Abu al-Hasan ya ga a mafarki cewa wani ya gaya masa cewa Hasan ibn Muthla daga Jamkaran zai zo wajensa, don haka ya tabbatar da shi kuma ya dogara da maganarsa. Lokacin da suka je tare zuwa Jamkaran, sun gamu da garken Jafar Kashani, sai wata akuya ta ruga zuwa gare su. Jafar ya rantse cewa wannan akuya ba ta cikin garkensa kuma bai taɓa ganinta ba. (Muhaddis Nuri, Jannatul Ma'awa, shafi na 54–58; Najmus Saƙib, juzu'i na 2, shafi na 454–458; Kalimate Ɗayyiba, shafi na 682–686.)
- ↑ Bisa rahoton littafin Tarikhe Qom, masallaci na farko da aka gina a Qom shi ne masallacin ƙauyen Jamkaran, wanda Khattab Asadi ya gina kafin hijirar Ash'ariyawa daga Kufa zuwa wannan birni, a farkon karni na biyu na Hijira (Qommi, Tarikhe Qom, shafi na 38).
Nassoshi
- Faƙihi, Ali-Asghar, «Qom Dar Masire Tarikh,» (Qom a cikin tafarkin tarihi), a cikin mujallar Nameh-ye Qom, lamba 7 da 8, kaka da hunturu 1378Sh/1999M.
- Faƙihi, Ali-Asgar, Tarikhe Mazhabiye Qom, sashi na farko daga littafin Tarikhe Jame Qom, Qom, Za'er, 1386Sh.
- Kwamitin wallafa na Cibiyar Farhange Honari Imani Jihadi, Masih Dar Shabe Ƙadr, Tehran, Cibiyar Jihadi Sahba, 1393Sh.
- Mudarrasi Ɗabaɗaba'i, Sayyid Husain, Turbate Pakan, : athar wa Banahaye Ƙadime Hadde Kununiye Dare al-Mu'minin Qom, Mehr, 1335Sh.
- Munshi Ƙummi, Ahmad, Khulasatut Tawarikh, Tehran, bugun Ihsan ishraqi, 1359–1363Sh.
- Nasirush Sharia, Muhammad Husaini, gyara: Ali Duwani, Tarikhe Qom, Tehran, Rahnamun, 1383Sh.
- Nuri, Husaini Bin Muhammad Taƙi, Mustadrakul Wasa'il wa Mustanbaɗ al-Masa'il, Qom, Cibiyar Alul-Bait, 148H.
- Nuri, Husaini, Jannatul Ma'awa fi Zikr man faza bi-liƙa' al-hujja, gyara: Cibiyar Ad-Dirasatul Takhassusiyya Fil Imam Mahadi (A.S), Qom, Cibiyar al-Sayyida al-Ma'asuma, 1427H.
- Nuri, Husaini, Kalimate Ɗayyiba, gyara: Muhammad Malaki, Qom, Mawallafar Parhizkar, 1380Sh.
- Nuri, Husaini, Najmus Saƙib fi Ahwal al-Imam al-Gha'ib, Qom, Masjid Jamkaran, 1384H.
- Ƙummi, Hassan Bin Muhammad, Tarikhe Qom, fassarar Hassan Bin Ali Ƙummi, Tehran, bugun Jalal al-Din Tehrani, 1361Sh.
- Ƙummi, Shaik Abbas, Kulliyyate Mafatihil Jinan, gyara:Husaini Ostad Wali, fassara: Musawi Damgani, Qom, Wallafe-wallafen sadiƙe, 1376Sh.
- «توسعه مسجد جمکران نیازمند ۱۷۰ میلیارد تومان اعتبار است»، (Ci gaban Masallacin Jamkaran yana buƙatar kasafin kuɗi na toman biliyan 170), Shafin Masjid Jamkaran, an wallafa: 4 Mayu 2011, an duba: 4 Satumba 2018M.
- «تولیت مسجد مقدس جمکران»، (Jagorancin/mai kula da Masjid Jamkaran mai tsarki), Shafin Masjid Jamkaran, an duba: 4 Satumba 2018M.
- «چاه عریضه در مسجد جمکران»، (Rijiya ta wasiƙa a Masjid Jamkaran), Shafin bayanai na Ofishin Ayatullah Makarim Shirazi, an duba: 4 Satumba 2018M.
- «معماری مسجد مقدس جمکران؛ دومین مقصد گردشگری مذهبی در قم»، (Tsarin gine-ginen Masjid-e Muqaddas-e Jamkaran; wuri na biyu na yawon buɗe ido na addini a Qom.), A shafin Rahnamaye Safre Man, an wallafa: 18 Maris 2017, an duba: 4 Satumba 2018M.
- «چاه مسجد جمکران موقتا بسته شد»، (An rufe rijiya ta Masallacin Jamkaran na ɗan lokaci.), Shafin yanar gizo na Rooze No, an wallafa: 3 Nuwamba 2020, an duba: 16 Nuwamba 2020M.
- «چاه مسجد جمکران بسته و تخریب شد»، (An rufe kuma an lalata rijiya ta Masjid Jamkaran.), Shafin yanar gizo na Shi'are Sal, an wallafa: 3 Nuwamba 2020, an duba: 16 Nuwamba 2020M.
- Arab, Kazim. «مدخل مسجد جمکران در دانشنامه جهان اسلام»، (Shigar Masjid Jamkaran a cikin Kundin Ilimin Duniya na Musulunci), Tehran, 2006M.
- Khan Muhammadi da Anwari, Karim da Muhammadreza. «چاه عریضه جمکران از خرافه تا واقعیت»، (Rijiya ta wasiƙa ta Jamkaran: daga camfi zuwa gaskiya), Nazarin Shi'a, fitowa ta 37, 2013M.
- «انتصاب حجتالاسلام اجاقنژاد به تولیت مسجد مقدس جمکران»، (Nadawa/naɗin Hujjatul-Islam Ojaƙnejad a matsayin mai kula na Masallacin Jamkaran Mai tsarki), Ofishin Hifze Wa Nashre Asare Hazrate Ayatullahi al-Uzma Khamna'i. an wallafa: 11 Oktoba 2023, an duba: 30 Oktoba 2023M.
- Zandiyye, Hassan, «Masjide Jamkaran» (Masallacin Jamkaran) a cikin mujallar Masjid, shafi na 25, Maris da Afrilu 1996M.