Daƙiƙa:Masallacin Jamkaran
Wannan labarin yana magana ne kan Masallacin Jamkaran, don haka idan ana so a duba ƙauyen Jamkaran sai a koma zuwa shigar Jamkaran (Ƙauye).
| Kafawa | Ƙarni na huɗu na Hijirar (bisa ra'ayin Muhaddis Nuri). |
|---|---|
| Mai amfani | Masallaci |
| Wuri | Qom |
| Sauran sunaye | Masallacin Sahibuz Zaman●Masjide Ƙadamga |
| Salon | Na Iran da Musulunci |
| Sabunta gini | A daurori daban-daban |
| Shafin yanar gizo | پایگاه مسجد جمکران |
Masallacin Jamkaran wani masallaci ne da ake dangantawa da Imam Mahadi (A.F), Imam na goma sha biyu a wajen Shi'a, wanda aka ce an gina shi a karni na huɗu na Hijirar Qamariyya a gefen birnin Qum. Bisa rahoton Mirza Husaini Nuri, malamin hadisi a ƙarni na goma sha uku na Hijira, an gina wannan masallaci ne da umarnin Imam Mahdi (A.F) ta hannun wani malami daga Qum mai suna Abul Hassan. Muhaddis Nuri ya ruwaito wani labari da ya ce Hassan Bin Musla Jamkarani ya gana da Imam Mahdi (A.F), kuma Imam ɗin ya umarce shi da a gina Masallacin Jamkaran. Mirza Husaini Nuri ya bayyana cewa wannan abin ya faru a shekara ta 373 ko 393 Hijira, kuma ya danganta ruwayar zuwa littafin Mu'unis al-hazin na Shaik Saduƙ.
Sai dai wasu masu bincike sun nuna shakku kan danganta wannan masallaci ga Imam Mahadi (A.F), suna kawo hujjoji kamar rashin ambaton wannan littafi a cikin littattafan ilimin rijal na Shi'a, da kuma rashin samuwar wannan labari a sauran rubuce-rubucen Shaik Saduƙ.
A wannan masallaci ana gudanar da bukukuwa da ibadu daban-daban kamar bikin rabin Sha'aban, addu'ar tawassuli da addu'ar Nudba. Mutane daga sassa daban-daban na Iran da ma sauran ƙasashe suna zuwa Masallacin Jamkaran, musamman a dararen Laraba. Wasu malamai sun danganta ziyartar masallacin a dararen Laraba da umarnin Imam Mahadi ga Hassan Bin Musla, kuma kasancewar malamai irin su Muhammad Taƙiyyu Bafƙi a dararen Laraba ya taimaka wajen ƙarfafa wannan al'ada.
An yi gyare-gyare da sabuntawa ga masallacin a lokuta daban-daban. Tsohuwar rubutu mafi daɗewa da aka samu yana nuna gyara a shekara ta 1167 Hijira. Har zuwa kafin juyin juya halin Iran na 1979, masallacin ƙarami ne, amma bayan haka ya faɗaɗa sosai. Rukunin Masjid Jamkaran ya haɗa da fili na waje, babban farfajiya, dakunan salla, masallacin maƙam da gine-ginen gudanarwa.
Akwai ibadu na musamman da aka ruwaito ga wannan masallaci, kamar raka'o'i biyu na sallar gaisuwa ga masallaci da kuma raka'o'i biyu na sallar Imam Zaman. Muhaddis Nuri ya danganta waɗannan ibadu ga Imam Mahdi (a.s.), kuma Shaik Abbas Ƙummi ya kawo su daga gare shi a cikin Mafatih al-Jinan.
Wuri Da Suna
Masallacin Jamkaran shi ne masallaci da ake dangantawa da Imam Mahdi (A.F),[1] wanda yake a gefen birnin Qum kuma yana da nisan kusan kilomita 8 daga haramin Sayyida Ma'asuma (A.S).[2] An yi wa wannan masallaci suna ne saboda kusancinsa da ƙauyen Jamkaran, shi ya sa aka fi saninsa da wannan suna.[3]
A da, wannan masallaci ana kiran sa da Masjide Ƙadamga (masallacin wurin taka sawu), saboda wata dutse mai marmara da ake ɗauka a matsayin wurin da Imam na goma sha biyu na Shi'a ya taka sawu.[4]Ana kiran sa da Masjid Ƙadamga a baya.[5] Haka kuma, saboda dangantarsa da Imam Zaman (A.S),[6] ana kiran shi da Masjid Sahib al-Zaman.[7]
Dangantawa Da Imam Mahadi (A.F)
Bisa ruwayar Mirza Husaini Nuri (ya rasu: 1320 H), ɗaya daga cikin malamai masu riwayar hadisi na Shi'a, an ce Masallacin Jamkaran an gina shi ne a karni na huɗu na Hijira da umarnin Imam Mahadi (A.F), kuma wani malami daga Qum mai suna Sayyid Abul Hassan ne ya gina shi.[8]
Muhaddis Nuri ya ruwaito daga Hassan Bin Musa Jamkarani cewa ya ce a daren Talata, 17 ga watan Ramadan, shekara ta 393 Q, ya haɗu da Imam Zaman (A.F) a wurin da daga baya aka gina Masallacin Jamkaran. Imam ɗin ya ba shi umarni biyu: na farko, a nemi Hassan Bin Muslim ya daina noma wannan ƙasa saboda ƙasa ce mai daraja, wacce ya haɗa da gonarsa ba bisa ƙa'ida ba. Na biyu, a gaya wa Sayyid Abul Hassan (ɗaya daga cikin malaman Qum) ya yi amfani da kuɗin da Hassan Bin Muslim ya samu daga noman shekarun baya wajen gina masallaci a wannan wuri.[9]
Bisa wannan ruwaya, bayan wannan lamari Sayyid Abu al-Hasan ya gina masallaci mai rufi na itace a wurin da aka riga aka iyakance ta hannun Imam Zaman (A.F).[10][Tsokaci 1]
Majiyoyin Labarin
An ruwaito labarin gina Masallacin Jamkaran a cikin littattafan Muhaddis Nuri kamar Kalimat Tayyiba,[11] Najme Saƙib,[12] Mustadrakul Wasa'il,[13] da Jannatul Ma'awa.[14] Muhaddith Nuri ya danganta wannan labari zuwa littafin Tarikhe Qum, kuma ya rubuta cewa Tarikh Qum ya nakalto shi daga littafin Mu'unisul Hazin Fi Ma'arifatilHaƙƙi Wa Al-Yaƙin na Sheikh Saduƙ.[15]
Haka kuma Muhaddith Nuri a cikin Mustadrak al-Wasa'il ya ce ya ga wannan labari a cikin ƙarin bayani (hashiya) na littafin Naƙdir Rijal da aka rubuta da hannun Muhammad Ali Bahbahani (ya rasu: 1216 Q), wanda kuma ya danganta shi zuwa Muns al-hazin.[16]
Shakku Kan Labarin
Muhaddis Nuri (ya rasu: 1320 Q) ya kawo cewa shekarar gina masallacin a wasu littattafansa ita ce 393 Q,[17] a wasu kuma 373 Q.[18] Nasir al-Shariah, marubucin Tarikh Qum, ya yi yiwuwar cewa wannan lamari ya faru kusan shekaru 100 kafin hakan, a shekara ta 293 Q.[19] Muhaddith Nuri ma ya ambaci wannan shekara a cikin hashiya na Naƙdir Rijal.[20]
Wasu masu bincike sun yi shakku kan ingancin danganta Masallacin Jamkaran ga Imam Zaman (A.S). Ali Dawani ya nuna cewa rashin ambaton littafin Mu'unisul Hazin a cikin littattafan rijal, rashin samuwar wannan labari a cikin bugu biyar na Tarikh Qum, da kuma rashin ambaton Shaikh Saduƙ a wasu ayyukansa, suna daga cikin hujjojin da ke sa a yi shakku kan wannan ruwaya.[21]
Ayyukan Ibada Na Masallacin Jamkaran
An ambaci salloli biyu masu raka'a biyu-biyu na musamman ga Masjid Jamkaran: sallar gaisuwar masallaci da kuma sallar Imam Zaman (A.S).[22]
- Salla ta farko, wato sallar gaisuwar masallaci, ana karanta Suratul Fatiha sau ɗaya da Suratul Iklasi (Qul Huwa Allahu Ahad) sau bakwai a kowace raka'a. Haka kuma ana maimaita zikirin ruku'u da sujada sau bakwai-bakwai.[23]
- Salla ta biyu kuwa ana yin ta da niyyar sallar Imam Zaman (A.F). A kowace raka'a, ana maimaita ayar Iyyaka na'abudu wa iyyaka nasta'in sau ɗari,[24] sannan a ci gaba da karanta sauran Suratul Fatiha tare da Suratul Ikhlasi sau ɗaya. Bayan haka, ana maimaita zikirin ruku'u da sujada sau bakwai-bakwai. Bayan an yi sallama, ana karanta La Ilaha Illallah sau ɗaya, sannan a yi Tasbihin Sayyida Zahra (S). Daga nan mai salla zai yi sujada ya aika salati sau ɗari ga Annabi (S.A.W).[25]
Muhaddis Nuri ya danganta waɗannan ayyukan ibada ga Imam Zaman (A.S), kuma ya ruwaito daga gare shi cewa: Mutane su riƙa ƙaunar wannan wuri kuma su girmama shi. Kamar yadda ya rubuta, duk wanda ya yi waɗannan raka'o'i huɗu a Masallacin Jamkaran, kamar ya yi salla ne a cikin Ka'aba.[26]
Shaik Abbas Ƙummi ya kawo waɗannan ayyukan ibada a cikin Mafatihul Jinan, yana naƙalto su daga malaminsa Muhaddis Nuri.[27]
Ali Dawani, masanin tarihi da bincike, saboda shakkun da ya nuna game da danganta Masjid Jamkaran ga Imam Mahadi (A.F), ya kuma nuna shakku game da danganta waɗannan ayyukan ibada gare shi.[28]
Ziyartar Masallacin Jamkaran A Dararen Laraba

Ali Asgar Faƙihi, marubucin Tarikh-e Jame Qum a shekara ta 1350 SH,[29] ya bayyana Masjid Jamkaran a matsayin ɗaya daga cikin manyan masallatai masu yawan jama'a a Iran a wancan lokaci, inda mutane daga birane daban-daban ke halarta a dararen Laraba.[30]
Wasu masu bincike sun jaddada cewa dagewa kan ziyartar Masallacin Jamkaran a dararen Laraba ya dace da ruwayar Hassan Bin Musla Jamkarani,[31] domin ganawarsa da Imam Zaman (A.F) ta faru ne a daren Talata a wurin masallacin,[32] kuma Imam ya umurce shi da cewa daren gobe (darar Laraba) a je a kawo wata akuya daga garken dabbobi a yanka a wurin, sannan a rarraba naman ga marasa lafiya.[33]
Marubucin Tarikhe Jsme Qum ya danganta bunƙasar Masallacin Jamkaran da kulawar Muhammad Taƙiyyu Yazdi Bafƙi, wanda ya kasance yana tafiya da wasu ɗalibai da ƙafa zuwa masallacin a yammacin Talata, yana yin sallar magriba da isha'i a wurin, sannan ya kwana yana ibada har zuwa safiya.[34] A cewar Nasir al-Shariah, tun da farko ma ana samun mutane daga Qum da ke yin ibada a wannan masallaci a dararen Jumma'a.[35]
Masjid Jamkaran kuma wurin gudanar da wasu bukukuwa na addini ne kamar bikin rabin Sha'aban.[36] Haka kuma ana gudanar da addu'o'i kamar Du'a'u Kumail da Du'a'u Nudba a dararen Juma'a, da Du'a'u Tawassul a dararen Laraba, inda mutane daga wurare daban-daban ke halarta.[37] An ruwaito cewa yawan masu ziyara na shekara-shekara na iya kaiwa kusan miliyan 15.[38]
Tarihi Da Sauye-sauye

Tarihi da sauye-sauye Bisa wani labari da Mirza Husaini Nuri ya ruwaito, ginin Masallacin Jamkaran yana komawa ne zuwa karni na huɗu na Hijirar hijira.[39] Sayyid Husaini Mudarassi Ɗabaɗaba'i ya yi hasashen cewa Masallacin Jamkaran shi ne dai Masallacin Khattab Asadi da aka ambata a cikin Tarikh Qum, wadda aka ce an gina ta a ƙauyen Jamkaran a farkon ƙarni na biyu na Hijira.[40][Tsokaci 2] Sai dai wasu masu bincike sun yi imanin cewa Masallacin Jamkaran ba ita ce wannan masallaci ba, kuma bisa ruwayar Muhaddis Nuri suna ganin an gina ta ne a ƙarni na huɗu na Hijira.[41]
Duk da haka, babu cikakkun bayanai game da Masallacin Jamkaran a cikin tsofaffin majiyoyin tarihi. Abin da aka samu kawai shi ne a littafin Khulasatut Tawarikh, inda a yayin bayanin abubuwan da suka faru a shekara ta 986 Q, an ambaci cewa Mir Ghiyasud-Din Muhammad Mirmiran, lokacin da yake sauka a ƙauyen Lanjarud na Qum, wani lokaci yana yin itikafi a wani wuri a Jamkaran da ake kira Maƙame Imam Zaman.[42]
A cewar Ali Asgar Faƙihi, masanin tarihin zamani, abin da ake nufi da wannan maƙam shi ne Masallacin Jamkaran.[43]
Gyaran Masallacin
An yi wa Masallacin Jamkaran gyare-gyare da sake gina wasu sassansa a lokuta daban-daban. Bisa wani rubutun allo mai ɗauke da shekarar 1167 Q, Mirza Ali Akbar Jamkarani ya gyara masallacin a wannan shekara. Haka kuma, wannan katiba ta nuna cewa a lokacin ginin ya ƙunshi masallaci mai girman mita 17 × 5, wanda yake a kudancin wani fili mai girman mita 17 × 13.[Tsokaci 3][44]
Daga baya, Ali Ƙuli Jamkarani ya fara gina wani ɓangare na filin masallacin, amma aikin bai kammala ba har sai da Ali Asgar Khan Atabak ya gyara shi a farkon mulkin Muzaffarud-Din Shah Ƙajar (1232–1285 SH).[45]
Muhammad Taƙiyyu Bafƙi (ya rasu a 1325 SH), ɗaya daga cikin malaman Qum, shi ma ya gudanar da wasu gyare-gyare a masallacin.[46] Haka kuma wani mutum mai suna Sayyid Muhammad Aghazadeh ya gyara wasu sassa na masallacin a shekara ta 1332 SH, kuma ya gina wani babban zaure a kudancin filin masallacin.[47]
A ɓangaren kudu maso gabashin masallacin akwai wata hasumiyar azan (minaret) ta tubali mai tsayin mita 17, wadda bisa ga wani rubutun katiba aka gina ta a shekara ta 1318 SH.[48]
Faɗaɗa Ginin A Jamhuriyar Musulunci

Bayan Juyin Juya Halin Musulunci na Iran a shekara ta 1357 SH (1979 M), Majalisar Gudanarwar Hauzar Ilmi ta Qum ta gabatar da mambobin kwamitin amintattu (hay'at-e umana) na Masallacin Jamkaran, sannan Hukumar Waƙfi da Harkokin Alkhairi ta ɗauki nauyin sa ido kan harkokin wannan masallaci.[49] Daga wannan lokaci ne aikin faɗaɗa masallacin ya samu sauri.
Bayan haka, an ware hekta 40 na ƙasa domin Masallacin Jamkaran, inda hekta 5.5 daga cikinsu aka keɓe don haraba da babban filin masallacin (sahn).[50]
Har ila yau, a shekara ta 1382 SH an amince da wani sabon tsari na bunƙasa harabar Masallacin Jamkaran, wanda ya tanadi kusan hekta 250 na ƙasa ga wannan cibiya. Daga cikin wannan fili, kusan murabba'in mita 30,000 an ware su ga Masjide Maƙam da ɗakunan sallah, yayin da sauran filayen suka kasance na haraba, gine-ginen gudanarwa da kuma wuraren hidima. A cikin wannan shiri, an sake gina dukkan gine-ginen masallacin, ban da Masjide Maƙam.[51]
Ana gudanar da Masjid Jamkaran ta hannun sassa daban-daban, kamar: Sashen bukukuwa da wa'azi, hulɗa da jama'a, ɗakin karatu, sashen wallafe-wallafe, sashen rajistar karamai, da sashen karɓar nazirce-nazirce da kyaututtuka.
A halin yanzu, Sayyid Ali Akbar Ojaƙnejad ne ke riƙe da muƙamin mai kula da Masallacin Jamkaran.[52] Kafin shi kuwa, Muhammad Husaini Rahimiyan da Abul Ƙasim Wafi ne suka riƙe wannan muƙami..[53]
Gine-gine da Tsarin Gini
Ƙungiyar Masallacin Jamkaran ta ƙunshi sassa daban-daban kamar Masjide Maƙam, ɗakunan sallah, babban filin masallaci, da kuma gine-ginen gudanarwa da na hukumomi.

Masjide Maƙam
Babban ginin ɗakin salla na Masallacin Jamkaran ana kiransa Masjide Maƙam, wanda ke da faɗin kusan murabba'in mita 1100. Ƙofar shigarsa tana haɗe da ɗakin sallah ta hanyoyin shiga uku, kuma a gefen wannan ƙofa akwai manara biyu masu tsayin kusan mita 60.
Wannan ɗakin sallah yana da ginshiƙai takwas, inda ƙubbar masallacin ke zaune a kan su ta hanyar tsarin ƙarfe. A cikin ƙasan ƙubbar an saka tagogi 23 waɗanda ke ba da haske ga cikin ɗakin sallah.
Fuskar waje ta ƙubbar an lulluɓe ta da tayal masu launin shuɗi-firuzai, sannan an ƙawata ta da rubuce-rubucen tahlil da kuma zane-zanen ado da ke ɗauke da kalmar Ya Mahdi adrikni. Cikin kubbar kuma an yi ado da tayal masu zane-zane na muraƙƙa tare da haɗa su da tubali.
Haka kuma ginshiƙai, mihrabi, ƙofar shiga ɗakin sallah, da manarori biyu da ke gefensa an ƙawata su da tayal na ado da kuma zane-zanen muƙarnas.[54]
Babban Filin Masallaci
Masallacin Jamkaran yana da ƙofofi shida, inda ƙofar arewa maso gabas ke kaiwa kai-tsaye zuwa babban ɗakin sallah na masallaci.[55] A kewayen filin masallacin an gina minare-minare, kuma bisa bayanin jami'an masallacin, ana shirin kai adadinsu zuwa 14..[56]
Ɗakunan Sallah (Shabistan)
- Shabistan na yamma da gabas: A gefen Masjide Maƙam akwai ɗakunan sallah biyu, kowanne yana da faɗin kusan murabba'in mita 4000, kuma an gina su a matakai biyu (bene biyu). Cikin waɗannan ɗakuna an yi ado da madubai, kuma kowanne yana da ƙubbobi biyu masu daidaito.[57]
Rijiyar Neman Buƙata

A wajen harabar masallaci, a bayan ginin Masjide Maƙam, akwai wani rijiya da ake kira Chahe Arize (rijiyar wasiƙa/buƙata).[58]
Wasu daga cikin Shi'a suna da imani da tsarkinta, kuma suna jefa rubuce-rubuce ko wasiƙu zuwa ga Imam Zaman a cikinta.[59] Sai dai wasu masu bincike sun bayyana cewa babu wata hujja ko takardar sahihanci game da wannan rijiya, kuma babu wani daga cikin manyan malamai (maraji'ai) da ya tabbatar mata da wata daraja ta musamman.[60]
Ayatullahi Khamina'i, jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran,[61] da Ayatullah Makarim Shirazi,[62] sun bayyana rashin goyon bayansu ga jefa wasiƙu cikin wannan rijiya.
Haka kuma an ruwaito cewa a cikin mihrabin masallaci akwai wata ƙaramar rijiya, inda wasu masu ziyara ke ɗaukar ƙasa don neman albarka. A cikin mihrabi kuma akwai wani dutse da aka sassaka da siffar sawun ƙafa, a matsayin alamar cewa masallacin gidan sawun ƙafa ne. Sai dai a shekarar 1350 Q, bisa umarnin Faizul Ƙummi (ya rasu 1370 Q), an lalata shi a matsayin bidi'a.[63]
A cewar wasu rahotannin kafafen labarai, wannan rijiya an rufe ta a watan Nuwamba na shekara ta 1399 SH.[64]
Batutuwa Masu Alaƙa
Bayanin kula
- ↑ Nuri, Jannat al-Ma'wa, shafi na 54–58; Nuri, Najm al-Thaqib, juzu'i na 2, shafi na 454–458; Nuri, Kalimat Tayyiba, shafi na 682–686.
- ↑ Khan-Muhammadi, Cah-e Arize-ye Jamkaran; az khorafeh ta vaqeiyat, shafi na 162.
- ↑ Arab, Masjid Jamkaran, shafi na 747.
- ↑ Nasir al-Shariah, Tarikh Qum, shafi na 233.
- ↑ Fayḍ Qummi, Ganjina-ye athar-e Qum, juzu'i na 2, shafi na 667, daga: Arab, Masjid Jamkaran, shafi na 747.
- ↑ Arab, Masjid Jamkaran, shafi na 747.
- ↑ Madrasi Tabataba'i, Turbat-e Pakan, juzu'i na 2, shafi na 164.
- ↑ Nuri, Jannat al-Ma'wa, shafi na 54–58.
- ↑ Nuri, Jannat al-Ma'wa, shafi na 54–58.
- ↑ Nuri, Jannat al-Ma'wa, shafi na 54–58; Nuri, --~~~~Najm al-Thaqib, juzu'i na 2, shafi na 454–458; Nuri, Kalimat Tayyiba, shafi na 682–686.
- ↑ Nuri, Kalimat Tayyiba, shafi na 682–686.
- ↑ Nuri, Najm al-Thaqib, 1384 Q, juzu'i na 2, shafi na 454–458.
- ↑ Nuri, Mustadrak al-Wasa'il, 1408 Q, juzu'i na 3, shafi na 447..
- ↑ Nuri, Jannat al-Ma'wa, shafi na 54–58
- ↑ Nuri, Jannat al-Ma'wa, shafi na 54.
- ↑ Nuri, Mustadrak al-Wasa'il, juzu'i na 3, shafi na 432 da 447.
- ↑ Nuri, Jannat al-Ma'wa, shafi na 54–58 da 383–388; Nuri, Kalimat Tayyiba, 1380 SH, shafi na 682–686.
- ↑ Nuri, Mustadrak al-Wasa'il, juzu'i na 3, shafi na 447; Nuri, Najm al-Thaqib, juzu'i na 2, shafi na 458.
- ↑ Nasir al-Shari'ah, Tarikhe Qum, shafi na 239.
- ↑ Nuri, Najm al-Thaqib, juzu'i na 2, shafi na 458.
- ↑ Nasir al-Shariah, Tarikh Qum, shafi na 29–30.
- ↑ Nuri, Jannat al-Ma'wa, shafi na 56; Nuri, Kalimat Tayyiba, shafi na 684.
- ↑ Qummi, Kulliyyat Mafatih al-Jinan', Namaz-e Masjid Jamkaran", shafi na 427–429.
- ↑ Surat al-hamd, aya ta 5.
- ↑ Nuri, Jannat al-Ma'wa, shafi na 55–56; Nuri, Najm al-Thaqib, juzu'i na 2, shafi na 456; Qummi, Kulliyyat Mafatih al-Jinan, Namaz-e Masjid Jamkaran, shafi na 427–429.
- ↑ Nuri, Jannat al-Ma'wa, 1427 Q, shafi na 56; Nuri, Kalimat Tayyiba, shafi na 684; Qummi, Kulliyyat Mafatih al-Jinan, Namaz-e Masjid Jamkaran, shafi na 429.
- ↑ Qummi, Kulliyyat Mafatih al-Jinan, Namaze Masjid Jamkaran, shafi na 427–429.
- ↑ Nasir al-Shariah, Tarikh Qum, shafi na 30.
- ↑ Faqihi, Tarikh-e Mazhabi-ye Qum, shafi na 7–10.
- ↑ Faqihi, Tarikh-e Mazhabi-ye Qum, shafi na 273.
- ↑ Nuri, Jannat al-Ma'wa, shafi na 54–58.
- ↑ Riḍwani, Mawud-shinasi wa Pasokh be Shubuhat, shafi na 486.
- ↑ Riḍwani, Mawud-shinasi wa Pasokh be Shubuhat, shafi na 486.
- ↑ Faqihi, Tarikh-e Mazhabi-ye Qum, shafi na 273–274.
- ↑ Nasir al-Shariah, Tarikh Qum, shafi na 233.
- ↑ «اعلام برنامههای ویژه نیمه شعبان در مسجد مقدس جمکران»،Kungiyar 'Yan Jarida Matasa
- ↑ Khan-Muhammadi, Cah-e Arize-ye Jamkaran az khorafe ta vaqeiyat, shafi na 162.
- ↑ Wiz eh-nameh-ye Jamkaran, shafi na 7–11, daga: Daneshnameh-ye Jahan-e Eslam, madkhal Masjid Jamkaran, shafi na 748.
- ↑ Nuri, Jannat al-Ma'wa, 1427 Q, shafi na 54–58; Nuri, Najm al-Thaqib, 1384 Q, juzu'i na 2, shafi na 454–458; Nuri, Kalimat Tayyiba, shafi na 682–686.
- ↑ Mudarassi Tabataba'i, Turbat-e Pakan, juzu'i na 2, shafi na 163–164.
- ↑ Faqihi, Tarikh-e Mazhabi-ye Qum, shafi na 272.
- ↑ Munshi Qummi, Khulasat al-Tawarikh, juzu'i na 2, shafi na 1019, daga: Daneshnameh-ye Jahan-e Eslam, madkhal Masjid Jamkaran, shafi na 747.
- ↑ Faqihi, Qum dar Masir-e Tarikh, shafi na 171, daga: Daneshnameh-ye Jahan-e Eslam, madkhal Masjid Jamkaran, shafi na 747.
- ↑ Madrasi Tabataba'i, Turbat-e Pakan, juzu'i na 2, shafi na 164.
- ↑ Nasir al-Shariah, Tarikh Qum, shafi na 233.
- ↑ Kuchakzadeh, Tarikhcheh-ye Qum wa Masajid-e Tarikhi-ye an, shafi na 246, daga: Daneshnameh-ye Jahan-e Eslam, madkhal Masjid Jamkaran, shafi na 748.
- ↑ Fayḍ Qummi, Ganjina-ye athar-e Qum, 1349–juzu'i na 2, shafi na 668 da 671, daga: Daneshnameh-ye Jahan-e Eslam, madkhal Masjid Jamkaran, shafi na 748.
- ↑ Fayḍ Qummi, Ganjina-ye athar-e Qum, juzu'i na 2, shafi na 670–672, daga: Daneshnameh-ye Jahan-e Eslam, madkhal Masjid Jamkaran, shafi na 748.
- ↑ Zandiyyeh, Masjid Jamkaran, shafi na 80, daga: Daneshnameh-ye Jahan-e Eslam, madkhal Masjid Jamkaran, shafi na 748.
- ↑ Zandiyyeh, Masjid Jamkaran, shafi na 78, daga: Daneshnameh-ye Jahan-e Eslam, madkhal Masjid Jamkaran, shafi na 749.
- ↑ Arab, Masjid Jamkaran, juzu'i na 10, shafi na 749.
- ↑ «انتصاب حجتالاسلام اجاقنژاد به تولیت مسجد مقدس جمکران»،Ofishin Kiyaye da Wallafa Ayyukan Mai Girma Ayatullah al-Uzma Khamna'i ..
- ↑ «تولیت مسجد مقدس جمکران»، Masallacin mai tsarki na Jamkaran
- ↑ Arab, Masjid Jamkaran, juzu'i na 10, shafi na 749.
- ↑ «معماری مسجد مقدس جمکران؛ دومین مقصد گردشگری مذهبی در قم»، Shafin jagorar tafiya.
- ↑ «توسعه مسجد جمکران نیازمند ۱۷۰ میلیارد تومان اعتبار است»،Shafin yanar gizo na Masjid Jamkaran mai tsarki.
- ↑ Arab, Masjid Jamkaran, juzu'i na 10, shafi na 749.
- ↑ Khan-Muhammadi,Chah-e Arize-ye Jamkaran az khorafe ta vaqeiyat, shafi na 162.
- ↑ Khan-Muhammadi, Chah-e Arize-ye Jamkaran az khorafe ta vaqeiyat, shafi na 163.
- ↑ Khan-Muhammadi, Chah-e Arize-ye Jamkaran az khorafe ta vaqeiyat, shafi na 175.
- ↑ Masih dar Shab-e Qadr, shafi na 431.
- ↑ «چاه عریضه در مسجد جمکران»،Shafin watsa bayanai na Ayatullah Makarem Shirazi
- ↑ Fayḍ Qummi, Ganjina-ye athar-e Qum, juzu'i na 2, shafi na 668, daga: Daneshnameh-ye Jahan-e Eslam, madkhal Masjid Jamkaran, shafi na 748.
- ↑ «چاه مسجد جمکران موقتا بسته شد»، Kamfanin Dillancin Labarai na Taqrib«چاه مسجد جمکران بسته و تخریب شد»، Shafin yanar gizo Taken Shekara
Tsokaci
- ↑ Bisa ruwayar Muhaddith Nuri, Hasan ibn Muthla Jamkarani ya ce a wannan tattaunawa da Imam Zamana (a.s.), ya roƙi Imam ya sanya masa wata alama domin mutane su gaskata maganarsa. Imam ya amsa da cewa: Ka je ka aiwatar da wannan umarni, kuma za mu sanya muku wasu alamu. Haka kuma Imam ya ce akwai wata akuya a garken Jafar Kashani da za a yanka a wannan wuri, a rarraba naman ga marasa lafiya, kuma duk wanda ya ci daga naman zai warke da izinin Allah. Haka nan, Abu al-Hasan ya ga a mafarki cewa wani ya gaya masa cewa Hasan ibn Muthla daga Jamkaran zai zo wajensa, don haka ya tabbatar da shi kuma ya dogara da maganarsa. Lokacin da suka je tare zuwa Jamkaran, sun gamu da garken Jafar Kashani, sai wata akuya ta ruga zuwa gare su. Jafar ya rantse cewa wannan akuya ba ta cikin garkensa kuma bai taɓa ganinta ba. (Muhaddis Nuri, Jannat al-Ma'wa, 1427 Q, shafi na 54–58; Najm al-Thaqib, juzu'i na 2, shafi na 454–458; Kalimat Tayyiba, shafi na 682–686.)
- ↑ Bisa rahoton littafin Tarikh Qum, masallaci na farko da aka gina a Qum shi ne masallacin ƙauyen Jamkaran, wanda Khattab Asadi ya gina kafin hijirar Ash'ariyawa daga Kufa zuwa wannan birni, a farkon karni na biyu na Hijira (Qummi, Tarikh Qum, 1361 Q, shafi na 38).
- ↑ Nasir al-Shariah ya ambaci shekarar gyaran masallacin da kuma shekarar rubutun katibar da 1158 Q, ba 1167 Q ba (Tarikh Qum, 1383 SH, shafi na 233).
Nassoshi
- Faqihi, Ali-Asghar, Qum dar Masir-e Tarikh, a cikin mujallar Nameh-ye Qum, lamba 7 da 8, kaka da hunturu 1378 SH.
- Faqihi, Ali-Asghar, Tarikh-e Mazhabi-ye Qum; sashi na farko daga littafin Tarikh-e Jame Qum, Qum, Za'er, 1386 SH.
- Kuchakzadeh, Muhammad-Reża, Tarikhcheh-ye Qum wa Masajid-e Tarikhi-ye an, Qum, 1380 SH.
- Kwamitin wallafa na Cibiyar Al'adu da Fasaha ta iman Jihadi, Masih dar Shab-e Qadr, Tehran, Mu'assasa Jihadi sahba, 1393 SH.
- Madrasi Tabataba'i, Sayyid Husayn, Turbat-e Pakan: athar wa Banaha-ye Qadim-eHadd-e Kununi-ye Gidan al-Mu'minin Qum, Mehr, 1335 SH.
- Mir Azimi, Sayyid Jafar, Masjid-e Muqaddas-e Jamkaran: Tajalli-gah-e sahib al-Zaman, Qum, Mawallafar Masjid-e Muqaddas-e Jamkaran, 1378 SH.
- Munshi Qummi, Ahmad, Khulasat al-Tawarikh, Tehran, bugun Ihsan Eshraqi, 1359–1363 SH.
- Nasir al-Shariah, Muhammad Husaini, gyara: Ali Dawani, Tarikh Qum, Tehran, Rahnamun, 1383 SH.
- Nuri, Husaini ibn Muhammad Taqi, Mustadrak al-Wasa'il wa MustanbaT al-Masa'il, Qum, Cibiyar Al al-Bayt, 148 Q.
- Nuri, Husaini, Jannat al-Ma'wa fi dhikr man faza bi-liqa' al-hujja, gyara: Cibiyar Nazarce-nazarce na Musamman kan Imam Mahdi (A.S), Qum, Cibiyar al-Sayyida al-Masuma, 1427 Q.
- Nuri, Husaini, Kalimat Tayyiba, gyara: Muhammad Malaki, Qum, Mawallafar Parhizkar, 1380 SH.
- Nuri, Husayn, Najm al-Thaqib fi Ahwal al-Imam al-Gha'ib, Qum, Masjid Jamkaran, 1384 Q.
- Qummi, Hasan ibn Muhammad, Tarikh Qum, fassarar Hassan ibn Ali Qummi, Tehran, bugun Jalal al-Din Tehrani, 1361 SH.
- Qummi, Shaik Abbas, Kulliyyat Mafatih al-Jinan, gyara:Husaini Ostad Vali, fassara: Musavi Damghani, Qum, Wallafe-wallafen sadiƙe, 1376 SH.
- Wizeh-nameh-ye Jamkaran, Qum, Masjid-e Muqaddas-e Jamkaran, 1384 SH.
- «مراسم این هفته مسجد مقدس جمکران»، (Shirye-shiryen wannan mako a Masjid-e Muqaddas-e Jamkaran.), Shafin Masjid Jamkaran, an wallafa: 2 Satumba 2018 M, an duba: 4 Satumba 2018 M.
- «توسعه مسجد جمکران نیازمند ۱۷۰ میلیارد تومان اعتبار است»،(Ci gaban Masjid Jamkaran yana buƙatar kasafin kuɗi na 170 biliyan toman.), Shafin Masjid Jamkaran, an wallafa: 4 Mayu 2011 M, an duba: 4 Satumba 2018 M.
- «تولیت مسجد مقدس جمکران»، (Jagorancin/mai kula da Masjid Jamkaran mai tsarki), Shafin Masjid Jamkaran, an duba: 4 Satumba 2018 M.
- «چاه عریضه در مسجد جمکران»، (Rijiya ta wasiƙa a Masjid Jamkaran), Shafin watsa bayanai na Ofishin Ayatullah Makarem Shirazi, an duba: 4 Satumba 2018 M (Miladiyya).
- «معماری مسجد مقدس جمکران؛ دومین مقصد گردشگری مذهبی در قم»، (Tsarin gine-ginen Masjid-e Muqaddas-e Jamkaran; wuri na biyu na yawon buɗe ido na addini a Qum.), A shafin Rahnama-ye Safar-e Man, an wallafa: 18 Maris 2017 M, an duba: 4 Satumba 2018 M.
- «چاه مسجد جمکران موقتا بسته شد»،(An rufe rijiya ta Masallacin Jamkaran na ɗan lokaci.), Shafin yanar gizo na Rooz-e No, an wallafa: 3 Nuwamba 2020 M, an duba: 16 Nuwamba 2020 M..
- «چاه مسجد جمکران بسته و تخریب شد»، (An rufe kuma an lalata rijiya ta Masjid Jamkaran.), Shafin yanar gizo na Shiar-e Sal, an wallafa: 3 Nuwamba 2020 M, an duba: 16 Nuwamba 2020 M.
- «اعلام برنامه های ویژه نیمه شعبان در مسجد مقدس جمکران»، (Sanar da shirye-shirye na musamman na Nisf Shaban a Masjid-e Muqaddas-e Jamkaran.), Shafin Kungiyar 'Yan Jarida Matasa (YJC), an wallafa: 22 Afrilu 2018 M, an duba: 4 Satumba 2018 M.
- Arab, Kazim. «مدخل مسجد جمکران در دانشنامه جهان اسلام»، (Shigar Masjid Jamkaran a cikin Kundin Ilimin Duniya na Musulunci), Tehran, 2006 M.
- Khanmuhammadi da Anvari, Karim da Muhammadreza. «چاه عریضه جمکران از خرافه تا واقعیت»،(Rijiya ta wasiƙa ta Jamkaran: daga camfi zuwa gaskiya), Nazarin Shi'a, fitowa ta 37,2013 Miladiyya
- «انتصاب حجتالاسلام اجاقنژاد به تولیت مسجد مقدس جمکران»، (Nadawa/naɗin Hujjatul-Islam Ojaqnejad a matsayin mai kula (tawliyya) na Masjid-e Muqaddas-e Jamkaran.), Ofishin Kiyaye da Wallafa Ayyukan Ayatullah al-Uzma Khamna'i , an wallafa: 11 Oktoba 2023 M, an duba: 30 Oktoba 2023 M.