Wasiƙar Ayatullah Khamene'i zuwa ga Ɗaliban Jami'a Masu Goyan Bayan Palasɗinawa

Daga wikishia
Wannan labarin, ko ɓangarensa, ya ƙunshi wani lamari na yanzu.

Bayanai na iya canzawa da sauri cikin lokaci. Rahotanni na farko na iya zama kuskure kuma sabbin abubuwan sabuntawa ga wannan labarin ƙila ba za su nuna duk abin da ke faruwa game da wannan ƙasida ba. Da fatan za a inganta wannan ƙasida.

Wasiƙar Ayatullah Khamena'i zuwa ga ɗaliban jami'a a amurka masu goyan bayan palasɗinawa, saƙon haɗin kai da nuna jin ƙai na jagoran jamhuriyar muslunci ta Iran Ayatullahi Sayyid Ali Khamene'i tare da masu goyan bayan palasɗin a amurka da suke nuna rashin amincewarsu kan hare-haren da haramtacciyar ƙasar isra'ila take kaiwa kan zirin gaza tun bayan ofireshin ɗin Tufanul Al-Aksa waɗannan ɗalibai sun shirya jerin gwano a jami'o'in amurka. Ayatullahi khamene'i cikin wannan wasiƙaya kira yi matasan da suke nuna goyan bayansu ga palasɗin matsayin wani ɓangare daga gwagwarmayar neman ƴanci sa ɓanin gwamnatocinsu, sun fara fito na fito mai daraja kan haramtacciyar ƙasar isra'ila sun tsaya kan hanya ta daidai a cikin tarihi, haka kuma ya yi ishara kan rawar da ƙasar birtaniya ta taka cikin samar gwamnatin sahayoniya. haka nan ya gabtar da amurka da ingila a matsayin mafi girman masu goyan bayan sahayoniya, Kuma ya jaddada haƙƙin Falasdinawa na kare kansu, Ayatullahi khamene'i cikin wannan wasiƙa ya lissafa tsayuwa ƙyam cikin hanyar gaskiya matsayin darasi da kur'ani ya koyar da dukkanin musulmi da ƴan Adam. haka nan ya tunatar da cewa gwamnatin jamhuriyar muslunci ta Iran ya faɗaɗa fagen gwagwarmaya tare da ƙarfafa shi. . a ƙarshen wasiƙar ya yi wasiyya ga matasan da yake aika wannan saƙo gare su da cewa su nemi sanin kur'ani؛[1] don haka aka ce Ayatullahi khamene'i a cikin wannan wasiƙa kamar dai sauran wasiƙu guda biyu ya buƙaci waɗannan matasa domin fahimtar addinin muslunci, su koma zuwa ga litattafan muslunci na asali, ka da su tasirantu da maganganu da fassarorin gabashi da yammacin duniya da makarantunsu daban-daban.[2]

Buga wannan wasiƙar ya haifar da martani daban-daban kuma kafofin watsa labaru na duniya sun nuna hakan.[3] ba'arin kamfanonin labarai sun labarta cewa mutane miliyan goma sha biyar suka bibiyi shafin dandanlin kafar sada zumunci a shgafin dfa ake danganta shi ga Ayatullahi khamene'i game da batun wasiƙar da ya fitar zuwa ga matasan ɗaliban jami'a na amurka a ranar 31 ga watan mayu shekara ta 2024.[4]

wannan wasiƙa a ranar 25 ga watan mayu 2024 bayan fitowarta[5] daidai lokacin da jerin gwanon nuna rashin amincewa da kisan ƙare dangi da isra'ila take zartarwa kan mutanen zirin gaza ya fuskanci yunƙurin tarwatsasu daga ƴan sandan amurka.[6] An fara zanga-zangar lumana ta dalibai na goyon bayan Gaza a ranar 17 ga Afrilu, 2024 daga jami'o'in Amurka kuma a hankali ya bazu zuwa jami'o'i a wasu ƙasashen yammacin Turai.[7] yunƙurin ƴan sanda na tarwatsa waɗannan matasa a amurka da wasu ƙasashen yammacin turan ya fuskanci martani daban-daban a duniya.[8]

Ina rubuta wannan wasiƙar zuwa ga matasan da farkakken lamirinsu ya motsar su don kare yara da matan Gaza da ake zalunta.

Ya ku matasa dalibai da ke Amurka! Wannan shi ne sakon mu na tausayawa da kuma goyon bayanmu gare ku. Yanzu kuna tsaye a bangaren daidai na tarihi - wanda ke gudana a halin yanzu. Yanzu kun kafa wani bangare na gwagwarmaya, kuma a ƙaraashin yin matsin lamba ga zaluncin gwamnatinku - wacce ke ba da kariya ga gwamnatin sahyoniya ta mamaya da rashin tausayi - kun fara yin gwagwarmaya mai daraja.

Babban fagen gwagwarmaya da ke a wuri mai nisa ya kasance yana fito na fito a tsawon shekaru tare da hangen nesa da jin ku na yanzu. Manufar wannan gwagwarmaya ita ce dakatar da irin zaluncin da wata Cibiyar ta'addanci da rashin tausayi da ake kira "Sahyoniyawa" ta ke yi wa al'ummar Palasɗinu tun shekaru da suka gabata tare da jefa su cikin mawuyacin hali da azabtarwa bayan mamaye ƙasarsu. Kisan gillar da gwamnatin wariyar launin fata ta Sahayoniya ta ke yi a yau ci gaba ne na muguwar halayyar da suke yi ne a cikin shekarun da suka gabata.

Falasɗinu ƙasa ce mai cin gashin kanta mai al'umma da ta kƙnshi Musulmai, Kirista da Yahudawa, kuma tana da dogon tarihi. Bayan yakin duniya, 'yan jari-hujjar cibiyar Sahayoniya tare da taimakon gwamnatin Burtaniya, sannu a hankali sun shigo da dubban 'yan ta'adda sannu a hankali cikin wannan ƙasa; Suka mamaye biranenta da ƙauyukanta; Dubun dubatar mutane ne aka kashe ko aka kore su zuwa ƙasashe makwabta; Sun kwace gidaje, kasuwanni, da gonaki daga hannunsu, suka kafa gwamnati mai suna Isra’ila a cikinƙkasar Falasɗinu da suka kwace.

Babban mai goyan bayan wannan gwamnatin kwace, bayan taimakon farko na Birtaniya, ita ce gwamnatin Amurka, wadda ta ci gaba da goyon bayanta a siyasance da tattalin arziki da makamai ga wannan gwamnatin, har ma cikin sakaci da bazai yiwu a yafe ba ta bude mata hanyar kera makaman kare dangi da makaman nukiliya ta taimaka masa ta wannan hanya.

Tun daga rana ta farko gwamnatin sahyoniyawan ta yi amfani da manufar "ƙarfin ƙarfe" a kan al'ummar Palasɗinu da ba su da kariya, tare da yin watsi da duk wata kima, ta dan Adam da ta addini, a kowacce rana tana ƙara aikata zalunci da ta'addanci da danniya.

Gwamnatin Amurka da kawayenta ba su ma nuna adawa da wannan gwamnatin ta'addanci da zalunci da ke cigaba ba. Har yau, wasu kalaman gwamnatin Amurka dangane da munanan laifuka a Gaza sun fi a munafunce fiye da na gaske.

“Fagen gwagwagwarmaya” ya taso ne daga cikin wannan yanayi mai duhu da rashin tabbas wanda kuma da kafa gwamnatin “Jamhuriyar Musulunci” a Iran ta faɗaɗa ta tare da ba shi karfin gwiwa.

Shugabannin yahudawan sahyoniyanci na ƙasa da ƙasa, wanda ya zamo galibin kamfanonin yada labarai a Amurka da Turai nasu ne ko kuma suna ƙarƙashin tasirin kuɗaɗensu da cin hancinsu, sun gabatar da wannan gwagwarmaya ta mutuntaka da jajircewa a matsayin ta'addanci! Shin al'ummar da ta kare kanta a cikin ƙasarta daga laifukan sahyoniyawa 'yan mamaya 'yan ta'adda ne? Sannan shin taimakon ƴan Adamtaka da ake baiwa wannan al'umma da ƙarfafa makamanta ana iya ɗaukarsa a matsayin ta'addanci? Shugabannin mulkin mallaka na duniya ba sa jin tausayin ra'ayoyin ɗan adam. Suna goyon baya ga azzalumar gwamnatin ta'addanci ta Isra'ila, kuma suna kiran gwagwarmayar Palasɗinawa da ke kare 'yancinta, tsaro da 'yancin kai, a matsayin "'yan ta'adda"!

Ina so in tabbatar muku cewa a yau al'amura sun canza. Wata makoma tana jiran yankin da ke da muhimmanci na yammacin Asiya. Lamiri da yawa a duniya suna kara farkawa kuma gaskiya tana bayyana. Kuma fagen gwagwarmaya ya yi ƙarfi kuma zai ƙara yin ƙarfi sosai. Tarihi kuma yana cikin canzawa. Baya ga ku, ɗaliban jami'o'i da dama a Amurka, jami'o'i da jama'ar wasu ƙasashe ma sun tashi tsaye. Suna masu goyon baya da tallafawa malaman jami'a gare ku dalibai wani abu ne mai mahimmanci kuma mai tasiri. Wannan zai iya zama ɗan kwantar da hankali idan akai la’akari da tsananin matakan ƴan sandan da gwamnati ke yi da kuma matsin lamba da suke yi. Ina kuma tausaya muku matasa kuma ina girmama matsayinku.

Koyarwar Alkur'ani gare mu Musulmi da dukkan mutanen duniya shi ne tsayawa kan tafarkin gaskiya فَاستَقِم کَما اُمِرت” (Suratul Hud, bangare na aya ta 112) kuma koyarwar Alkurani dangane da alaƙoƙin da su ke tsakanin mutane ita ce: “kada ku yi zalunci kuma kada ku bari a zalince ku”: (لا تَظلِمونَ وَ لا تُظلَمون) (Suratul Baƙarah, aya ta 279) fagen gwagwarmaya da bin waɗannan umarni da ɗaruruwan makamantansu ta ke ci gaba kuma zata samu kaiwa ga nasara; Da yardar Allah

Ina Mai Shawarartarku Da Ku San Alkur'ani.

Sayyid Ali Khamenei

25/5/2024.[9]

Bayanin kula

  1. «نامه حضرت آیت‌الله خامنه‌ای به دانشجویان حامی مردم فلسطین در دانشگاه‌های ایالات متحده آمریکا»، وبگاه دفتر حفظ و نشر آثار حضرت آیت‌الله العظمی خامنه‌ای.
  2. بیابان‌نورد سروستانی، «فرصت درک بدون پیش‌داوری از اسلام مهیاست»، روزنامه فرهیختگان.
  3. «بازتاب نامه رهبر انقلاب به دانشجویان آمریکا در فضای بین‌المللی»، خبرگزاری مهر.
  4. «بازدید ۱۵ میلیونی توییت حساب کاربری رهبر انقلاب»، مشرق‌نیوز.
  5. «نامه حضرت آیت‌الله خامنه‌ای به دانشجویان حامی مردم فلسطین در دانشگاه‌های ایالات متحده آمریکا»، وبگاه دفتر حفظ و نشر آثار حضرت آیت‌الله العظمی خامنه‌ای.
  6. Dubi Azhari, "Shekaste Marepich sukut dar dele Amrika", Jaridar Farhikhtegan.
  7. «بازتاب نامه رهبر انقلاب به دانشجویان آمریکا در شبکه تی‌آرتی ترکیه»، خبرگزاری مهر.
  8. برای نمونه نگاه کنید به «واکنش سازمان ملل به بازداشت دانشجویان حامی فلسطین در دانشگاه‌های آمریکا»، خبرگزاری ایرنا.
  9. «نامه حضرت آیت‌الله خامنه‌ای به دانشجویان حامی مردم فلسطین در دانشگاه‌های ایالات متحده آمریکا»، وبگاه دفتر حفظ و نشر آثار حضرت آیت‌الله العظمی خامنه‌ای.

Nassoshi