Maganar Da Annabi Isa Ya yi Yana Jariri
Magana da Annabi Isa Ya yi Yana Jariri (Larabci: تكلم النبي عيسى في المهد) Magana ta mu'ujiza Annabi Isa (A.S) ya yi lokacin da yake jariri a shimfiɗar haihuwa domin kawar da tuhumar aikata alfasha daga mahaifiyarsa Sayyida Maryam (S), da kuma shelanta muƙamin annabtarsa a gaban malaman yahudawa.[1] Cikin ayoyi guda uku daga kur'ani aya ta 46 suratul alu imran, aya ta 110 suratul ma'ida da aya ta 29 suratul maryam an yi ishara kan buɗa bakin Annabi Isa tun yana kan zanin haihuwa.[2] A cewar marubutan tafsirul al-amsal, mutane biyu daga masu dandaƙe bincike daga malaman tafsiri sun tafi kan cewa abin nufi daga kalmar “mahdi” shi ne shimfiɗa ko wani lokaci da galibi jariri yake kasance cikin kulawar mahaifiyarsa.[3] Kishiyar wannan magana, Muhammad Hadi Marifat cikin littafin At-Tamhid ya yi amanna cewa bayan shuɗewar wasu adadin shekaru bayan ta haihu ne ta dawo cikin gari, sannan ma'anar "Mahdi" shekarun yarintarsa.[4] Haka nan Sayyid Ahmad Khani Hindi, Malamin tafsirin kur'ani, ya yi amnanna maganar da Annabi Isa ya yi ta kasance a farko-farkon yarintarsa bawai lokacin da yake jariri ba.[5]
Abul Fatuh Razi, malamin tafsiri da hadisi ɗanshi'a a ƙarni na shida ƙamari, tare da jingina da wani hadisi daga Annabin muslunci, ya tafi kan cewa Annabi Isa ya kasance ɗaya daga cikin mutum biyar da suka yi magana a lokacin da suke jarirai.[6] Jafar Subhani da Ibrahim Amini daga malaman shi'a, game da maganar da Annabi Isa ya yi sun fitar da cewa hakan dalili ne kan yiwuwar samun hankali da tantancewa ta wajibi ga imamanci a shekarun yarinta.[7]
bisa Abin da ya zo cikin aya ta 30 suratul maryam, Isa cikin wannan magana da ya yi ya kirayi kansa da bawan Allah, Annabin Allah da aka bashi littafi da kuma kasancewarsa mai alabrka. haka nan ya yi bayani shi bai kasance mai takurawa ba, kuma Allah ya umarce shi da kiyaye sallah da bada zakka da biyayya ga babarsa, bisa abin da ayoyin kur'ani suka kawo, hakika wannan magana ya yi sallama uku ga kansa, aminci kaina ranar da aka haifeni, ranar da zan mutu da kuma ranar da za a tashe ni a raye a wata duniya.[8]
Ba'arin malaman tafsiri sun tafi kan cewa maganar da Annabi Isa ya yi mu'ujiza ce tasa, wasu kuma suna ganin matsayin karama ce ta Sayyida Maryam.[9] Muhammad Hadi Marifat, malamin tafsiri a shi'a, ya tafi kan cewa asalin maganar tasa ba ta da alaƙa da ko wace irin mu'ujiza, saboda a imanin malamin Annabi Isa ya yi magana ne bayan girmnsa kuma dama yawanci yara suna fara magana ne a wannan lokaci, a cewar Hadi Marifat nau'in maganarsa ta kasance ne da wani ma'auni da hankali na musamman wanda cikinsa ya tabbatar da cewa mahaifiyarsa ta haife shi ta hanyar mu'ujiza kuma ta kasance tsarkakakkiya daga duk wata tuhumar aikata alfasha.[10]
Fakhrur Razi, malamin tafsiri da hadisi Ahlus-sunna a ƙarni na shida, a cikin littafin Tafsirul Al-Kabir ya yi amanna cewa wannan waƙi'a tsantsar abin al'ajabi ne. Ya yi amanna da cewa akwai bambanci tsakanin mu'ujizar da take faruwa daga Annabi da kuma faruwar wani abin al'ajabi da ya same shi, ya yi amanna da cewa al'amura misalin haihuwar Annabi Isa ba tare da uba ba da maganar da ya yi a shimfiɗar jariri tana da bambanci da mu'ujizozi misalin raya matattu da ya yi a zamaninsa.[11]
Bayanin Kula
- ↑ Sadeghi Tehrani, "Sharhe Sakhnan Issa Masih Dur Ghawarah," na Muhammad Sadeghi Tehran.
- ↑ Alqur'ani mai girma. ↑
- ↑ Makarem Shirazi, Tafsir Namuna, 1371 AH, juzu'i na 13, shafi na 52; Mansouri da Shorgashti, “Parssi Didgah Hai Tafsir, Mufassirun darbaraye Ayat takallum Hazrat Isa, (A.S), dar Mahd”, shafi na 209-210.
- ↑ Mansouri da Shorgashti, “Parse didGahaye Tafsir, Mufassirun Ayat Takallum Hazrat Isa, (A.S), Dar Mahd” shafi na 210.
- ↑ Kazemi, “Naqdi Bar Andisheh Hai Sayyid Ahmadkhan Hindi Pyramun Ijaz,” shafi na 138.
- ↑ Razi, Rawd al-jinan wa Ruh al-jinan fi Tafsir Qur’an, 1408 AH, juzu’i na 13, shafi na 78.
- ↑ Sobhani, “Imamate dar kodaki?”, shafi na 46; Amini, “Aya Kodake panje sale Imam mishawad?”, Ibrahim Amini Ittila rasani.
- ↑ Makarem Shirazi, Tarjameh qur'an, 1373, shafi na 307.
- ↑ Fakhr Razi, al-Tafseer al-Kabir, 1420 AH, juzu'i na 21, shafi na 534.
- ↑ Mansouri da Shorgashti, “Parssi Didgah Hai Tafsir, Mufassirun darbaraye Ayat takallum Hazrat Isa, (A.S), dar Mahd”, shafi na 212
- ↑ Fakhr Razi, al-Tafsir al-Kabir, 1420 AH, juzu'i na 23, shafi na 280.
Nassoshi
- Alqur'ani mai girma.
- امینی، ابراهیم، «آیا کودک پنج ساله امام میشود؟»، Shafin bayanai na Ibrahim Amini, kwanan ziyara: 29 Yuni 1403
- Razi, Abul Fattouh, Ruz al-Jinnan da Ruh al-jinan a cikin Tafsirin Qur'an, Mashhad, Astan Quds Razavi, bugun farko, 1408H.
- Jafar Subhani «امامت در کودکی؟»،Mujallar "Darussa daga Maktabar Islama", lamba 640, Satumba 1393 SH.
- «شرح سخنان عیسی مسیح در گهواره»، Shafin bayanai na Muhammad Sadiqi Tehrani, kwanan ziyara: 29 Yuni 1403 SH.
- Fakhr Razi, Muhammad bin Omar, al-Tafsir al-Kabir, Lebanon, Dar Ihya Al-Tarat al-Arabi, bugu na uku, 1420H.
Kazimi Shahab، «نقدی بر اندیشههای سید احمدخان هندی پیرامون اعجاز»، Jaraidar Fasali ta Bayyinaat", lamba 26, shekara ta 7, 1379 SH
- Makarem Shirazi, Nasser, Tarjameh qur'an, Qum, Ofishin Tarihi da Ilimin Ilimin Musulunci, bugu na biyu, 1373.
- Makarem Shirazi, Nasser, Tafsir Namuna, Tehran, Dar Al-Kutub Al-Islamiyyah, Shaab Dahm, 1371H.
- Mansuri, Muhammad Hadi, da Hamida Shurgasht «بررسی دیدگاههای تفسیری مفسران درباره آیات تکلم حضرت عیسی علیهالسلام در مهد»، Mujallar fasali-falasi ta Nazarin Tafsiri", lamba 44, hunturu 1399 SH