Jump to content

Daƙiƙa:Ƙauracewa Kur'ani

Daga wikishia
Wannan maƙala tana magana ne kan Ƙauracewa Kur'ani. Domin fahimtar aya mai alaƙa da wannan suna, a duba aya ta 30 a cikin Suratul Furƙan.

Ƙauracewa Kur'ani ra'ayi ne da aka samo daga aya ta 30 a Suratul Furƙan, inda Annabi (S.A.W) ya kai ƙorafi ga Allah game da yadda mutane suka yi watsi da Kur'ani. Wannan ma'ana ta samu ƙarfafa a cikin ruwayoyin Shi'a, inda take nufin barin Kur'ani a fannoni daban-daban, kamar rashin fahimta daidai, sakaci da aiki da shi, da kuma takaita amfani da shi kawai ga karatu ba tare da zurfafa fahimta ba.

Masu tafsiri sun bayyana ma'anonin wannan kalma ta hanyoyi daban-daban; daga barin Kur'ani a aikace zuwa raba shi da Ahlul-Baiti da suke asalin masu bayani da fassara shi. Imam Khomaini ya jaddada bangaren siyasa da zamantakewa na Kur'ani, yana ganin cewa ƙaurace masa yana nufin watsi da waɗannan koyarwar, kuma yana ɗaukar hakan a matsayin ɗaya daga cikin manyan dalilan matsalolin duniyar Musulmi.

Ƙauracewar Kur'ani tana bayyana a fannoni kamar karanta shi, sauraro, haddacewa, tunani a kansa, tafsiri, da kuma aiki da shi. Haka kuma amfani da shi kawai don al'ada ko fassara shi bisa ra'ayi na kai ma ana ɗaukarsa daga cikin wannan matsala.

Daga cikin dalilan ƙauracewar Kur'ani akwai raba shi da Ahlul-Baiti, rinjayar fahimta ta zahiri, dakatar da ijtihadi, da yaɗa ra'ayin raba addini da siyasa.

Sakamakonsa kuwa ya haɗa da rarrabuwar ƙungiyoyi, koma-baya, yaɗuwar camfe-camfe, talauci, mulkin zalunci, da nisantar ruhaniya. Wasu daga cikin manyan malamai kamar Allama Ɗabaɗaba'i, Imam Khomaini, da Sayyid Jamalud-Din Asad Abadi sun yi ƙoƙari wajen magance wannan matsala.

Ma'anar Kalma Da Matsayinta

Ƙauracewa Kur'ani kalma ce da aka samo daga aya ta 30 a Suratul Furƙan, inda Annabi Muhammad (S.A.W) ya yi ƙorafi ga Allah game da rashin kula da al'ummarsa ga Kur'ani.[1] Haka kuma a ruwayoyin Shi'a an yi gargaɗi game da barin Kur'ani a gefe; misali Sayyid Radi a Nahjul Balaga[2] da Kulaini a Al-Kafi[3] sun kawo ruwayoyi daga Imaman Shi'a kan wannan batu.

Ƙauracewa Kur'ani a ma'ana gaba ɗaya tana nufin rashin fahimtar muhimmancinsa da matsayinsa, watsi da koyarwarsa, rashin kulawa da shi saboda gafala, da kuma takaita amfani da shi ga al'amuran biki ko na zahiri kawai.[4] Sayyid Muhammad Ali Ayazi ya bayyana ta a matsayin rashin sanin Kur'ani da kuma fitar da shi daga tsakiyar rayuwar ɗan adam.[5]

Masu bincike sun kawo ra'ayoyi daban-daban kan ma'anar wannan kalma a cikin aya ta 30 a Suratul Furqan:

  • Ma'anar ƙauracewa kai tsaye: tana haifar da rashin ji, juya baya da barin Kur'ani a zahiri,[6] ko rashin yin imani da shi.[7]
  • Ma'anar riƙe shi a gefe (tare da karantawa kawai): bisa kalmar ittakhazu, ma'anar ita ce mutane suna karanta Kur'ani amma ba sa fahimta daidai, ba sa aiki da shi, kuma suna kauce wa mahimman koyarwarsa, don haka a zahiri sun yi watsi da shi duk da suna da alaƙa da shi.[8] A wannan ra'ayi, Hassan Musɗafawi a At-Tahƙiƙ fi Kalimatil Ƙur'an ya bayyana cewa ƙauracewa Kur'ani na iya kasancewa tare da alaƙar zahiri amma ba tare da aiki da shi ba.[9]
  • Raba Kur'ani da Ahlul-Baiti: bisa ruwayoyi kamar Hadisin Saƙlaini da kuma wasu ra'ayoyi tarihi kamar Hasbuna Kitabullahi, da halifa na biyu ya furta wanda ya haifar da fahimta mara kyau ga Kur'ani.[10]

Imam Khomaini, daga cikin manyan maraji'an taƙlidi na shi'a, ya ɗauki fassarar siyasa da zamantakewa, yana cewa Kur'ani ya fi mayar da hankali kan tsarin rayuwa da siyasa fiye da ibada kawai.[11] Saboda haka, ƙauracewa Kur'ani a ganinsa yana nufin watsi da waɗannan dokoki na zamantakewa da siyasa, tare da takaita Kur'ani ga ibada kawai. Ya kuma danganta matsalolin al'ummar Musulmi da rashin aiki da waɗannan koyarwar Kur'ani.[12]

Ƙauracewar Kur'ani (Sasanni)

Masu binciken Kur'ani sun yi nazari kan ƙauracewar Kur'ani ta fannoni da salo daban-daban, kuma sun bayyana alamominsa a wurare da dama kamar: karantawa, sauraro, haddacewa, tunani mai zurfi (tadabbur), tafsiri, da kuma aiki da Kur'ani a rayuwa.[13]

A ra'ayin Ayatullah Makarim Shirazi, daga cikin masu tafsiri na Shi'a, ƙauracewar Kur'ani tana haɗa da: Amfani da Kur'ani kawai don ado ko al'ada (kamar amfani da ayoyi a ado na masallatai), amfani da shi don neman warkarwa ba tare da fahimtar sa ba, fifita tunanin Yammacin Turai a kan koyarwar Kur'ani, da kuma fassara Kur'ani bisa ra'ayin kai ba tare da hujja ba.[14]

Wasu masu tafsiri kuma sun bayyana cewa rashin kulawa da karatu, sauraro, haddacewa, tunani, da kuma rashin aiki da umarnin Kur'ani suna daga cikin alamomin ƙauracewa Kur'ani.[15]

Imam Khomaini ya bayyana cewa ƙauracewar Kur'ani tana nufin yin sakaci da koyarwar asali ta Kur'ani da rashin aiki da su.[16] A ganinsa, mayar da hankali kawai ga bangarorin zahiri kamar tajwidi, ilimin lafazi da adabi, ko batutuwan mu'ujiza, ba ya wadatarwa wajen kawar da ƙauracewar Kur'ani.[17]

Abubuwan Da Ke Haifar Da Ƙauracewar Kur'ani

An ambaci dalilai da abubuwa da dama da ke haifar da ƙauracewar Kur'ani, daga cikinsu akwai: ƙoƙarin raba Kur'ani da Ahlul-Baiti (A.S) waɗanda su ne masu bayani na asali,[18] shagala da fassarorin zahiri kawai, amfani da tafsiri na ra'ayi, ƙin amfani da hankali, dakatar da ijtihadi da yaɗuwar aƙidar Akhbariyya, son duniya da wasu Musulmi suka shiga, nuna Kur'ani a matsayin marar amfani, da kuma adawa da koyarwar siyasa da zamantakewar Kur'ani.[19]

Imam Khomaini ya bayyana cewa daga cikin manyan dalilai akwai takaita fahimtar Kur'ani ga wasu ƙwararru kawai da hana jama'a yin tunani a kansa da hujjar tsoron tafsiri bisa ra'ayi.[20] Haka kuma ya nuna cewa yaɗa ra'ayin raba addini da siyasa na daga manyan abubuwan da suka haifar da wannan matsala, domin ana rage Kur'ani zuwa ibada kawai, ana ɓoye bangarensa na siyasa da zamantakewa, don kiyaye ikon manyan ƙasashe a ƙasashen Musulmi.[21]

Masanin tarihi Rasul Jafariyan ya yi imani cewa tun zamanin Safawiyyawa, fahimtar Shi'a ta karkata sosai zuwa hadisi da tafsirin ruwaya, abin da ya jawo nesa daga Kur'ani.[22]

Haka kuma an ce rinjayen akidar Akhbariyyawa, mabiya Sufanci, da manufofin gwamnatoci su ma sun taka rawa. A wasu lokuta, gwamnatocin da ke da ra'ayoyin akida daban-daban ba sa son ganin Kur'ani yana fitowa fili a cikin rayuwar jama'a, saboda suna ganin hakan na iya zama barazana ga ikon su, don haka suke ƙoƙarin rage tasirin Kur'ani a al'umma.[23]

Sakamako

An bayyana cewa ƙauracewar Kur'ani a cikin al'ummar Musulmi tana haifar da mummunan sakamako da illoli da dama, daga ciki akwai:

  • Yaɗuwar bangaranci da rarrabuwar kai tsakanin mutane[24]
  • Yawaitar Islami na camfe-camfe da ƙagaggun hadisai[25]
  • Rasa ƙarfi, girma da darajar Musulmi, tare da jinkiri da koma-baya[26]
  • Nisantar al'umma daga ruhaniyya da yaɗuwar rashin ɗa'a da ƙimar ɗan'adam[27]
  • Samun iko da tasiri ga marasa cancanta, tare da yaɗuwar talauci da ƙunci[28]
  • Mulkin danniya na shugabanni da nesantar jama'a daga siyasa da al'amuran zamantakewa[29]
  • Fuskantar azabar Allah[30]

Na Gaba-gaba wajen Yaƙi Da Ƙauracewar Kur'ani

A cewar wasu masu bincike, daga cikin manyan masu ƙoƙarin dawo da Kur'ani cikin rayuwar Musulmi akwai: Allama Ɗabaɗaba'i, wanda ya rubuta Al-Mizan, wanda ya taimaka wajen bayyana Kur'ani da mayar da hankali ga ma'anarsa ta asali Imam Khomaini, wanda ya gabatar da fahimtar siyasa da zamantakewa a cikin Musulunci, yana jaddada matsayin Kur'ani a rayuwar al'umma[31]

Haka kuma, Sayyid Jamalud-Din Asad Abadi (ya rasu 1314 H) an bayyana shi a matsayin ɗaya daga cikin masu fara Yunƙurin komawa ga Kur'ani, wanda ya yi tasiri a ƙoƙarin gyaran al'ummar Musulmi a ƙarni na 15 Hijira.[32]

Bayanin kula

  1. Tabataba'i, Al-Mizan, juzu'i na 15, shafi na 205; Mudarrasi, Min Huda al-Qur'an, juzu'i na 8, shafi na 423.
  2. Nahj al-Balagha, gyara: Subhi Salih, huduba ta 147, shafi na 204; wasiƙa ta 47, shafi na 422.
  3. Kulaini, Al-Kafi, juzu'i na 2, shafi na 613; juzu'i na 8, shafi na 28.
  4. Ashrafi Amin, «Mahjuriyyat-e amuzeha-ye dini wa Qur'ani az didgah-e ʿAllama Shaik Muhammad ʿAbduh», shafi na 281; Fiqhizadeh da Ashrafi Amin, «Awamil wa zamineha-ye mahjuriyyat-e Qur'an dar baʿd-e siyasi wa ejtemaʿi dar andishe-ye Imam Khomaini», shafi na 58.
  5. Ayazi, «Dar jame'e-yi ke Qur'an mahjur ast afrad-e nashayeste, bi-khasiyyat wa na-salem bar sar-e kar mi-ayand., a shafin Majmae Modarresin wa Muhaqqiqin-e hawze-ye Ilmiyya-ye Qum.
  6. Ṭusi, At-Tibyan, juzu'i na 7, shafi na 486; Ṭabrisi, Majma al-Bayan, juzu'i na 7, shafi na 263; Zamakhshari, Al-Kashshaf, juzu'i na 3, shafi na 277.
  7. Faizul Kashani, As-Safi, juzu'i na 4, shafi na 11; Fakhr Razi, Mafatih al-Ghaib, juzu'i na 24, shafi na 455.
  8. Ghaffari, «Mahjuriyyat-e Qur'an», shafuffuka na 89–90; Mo'mini, «Daramadi bar Mahjuriyyat-e Qur'an-e Karim», shafuffuka na 60–61.
  9. Musṭafawi, Al-Tahqiq fi Kalimat al-Qur'an, juzu'i na 11, shafi na 240.
  10. Akhwan Muqaddam, «Nigahe be maʿna-ye Mahjuriyyat-e Qur'an dar ayeh 30 Sure-ye Furqan, bar asas-e važe-ha-ye hamnešin wa siyaq», shafuffuka na 23–28.
  11. Imam Khomaini, Sahifa-ye Imam, juzu'i na 2, shafi na 255; juzu'i na 5, shafi na 188.
  12. Imam Khomaini, Sahife Imam, juzu'i na 16, shafi na 34; Fiqhizadeh da Ashrafi Amin, «Awamil wa zamineha-ye mahjuriyyat-e Qur'an dar baʿd-e siyasi wa ejtemaʿi dar andishe-ye Imam Khomaini», shafuffuka na 58–59.
  13. Mo'mini, «Daramadi bar Mahjuriyyat-e Qur'an-e Karim», shafuffuka na 61–73.
  14. Makarim Shirazi, Tafsir-e Namuneh, juzu'i na 15, shafi na 77.
  15. Musavi, «Mahjuriyyat-e Qur'an, asbab wa neshaneha», shafuffuka na 14–16.
  16. Imam Khomaini, Sahife Imam, 1378 SH, juzu'i na 16, shafi na 34.
  17. Imam Khomaini, Adabus Salat, 1378 SH, shafi na 198.
  18. Mo'mini, «Rabete-ye Mahjuriyyat-e Qur'an wa Mahjuriyyat-e Ahl al-Bayt (a.s.)».
  19. Ashrafi Amin, «Mahjuriyyat-e amuzeha-ye dini wa Qur'ani az didgah-e Allama Shaik Muhammad Abduh», shafuffuka na 282–283; Fiqhizadeh da Ashrafi Amin, «Awamil wa zamineha-ye mahjuriyyat-e Qur'an dar baʿd-e siyasi wa ejtemaʿi dar andishe-ye Imam Khomaini», shafi na 60.
  20. Imam Khomaini, Adabus Salat, shafi na 199.
  21. Fiqhizadeh da Ashrafi Amin, «Awamil wa zamineha-ye mahjuriyyat-e Qur'an dar baʿd-e siyasi wa ejtemaʿi dar andishe-ye Imam Khomaini», shafuffuka na 65–67.
  22. Jaʿfariyan, «Nahzat-e bazgashat be Qur'an bara-ye ehya-ye ʿazamat-e az dast rafte bud», hira da mujallar Mehrnameh.
  23. Nabati, «Tathlith-e Mahjuriyyat-e Qur'an dar Jame'e-ye Irani.», an wallafa shi a shafin IKNA.
  24. Nahj al-Balagha, na Subhi Salih, huṭuba ta 147, shafi na 205; Ashrafi Amin, «Wahdat-e Musalmanan wa rabete-ye an ba mahjuriyyat-e Qur'an az didgah-e muslihan-e dini», shafi na 6.
  25. Tabataba'i, Al-Mizan fi Tafsir al-Qur'an, juzu'i na 5, shafi na 274.
  26. Imam Khomaini, Sahife Imam, juzu'i na 16, shafuffuka na 38–39.
  27. Imam Khomaini, Sahife Imam, juzu'i na 10, shafuffuka na 530–533.
  28. Ayazi, «Dar jame'e-yi ke Qur'an mahjur ast afrad-e nashayeste, bi-khasiyyat wa na-salem bar sar-e kar mi-ayand.», an wallafa shi a shafin Majmaʿ-e Modarresin wa Mohaqqeqin-e hawze-ye ʿIlmiyya-ye Qom.
  29. Ashrafi Amin, «Mahjuriyyat-e amuzeha-ye dini wa Qur'ani az didgah-e Allama Shaik Muhammad Abduh», shafi na 284.
  30. Saduq, Thawab al-Amal wa ʿIqab al-Aʿmal, shafi na 286.
  31. Ayazi, «Mahjuriyyat-e Qur'an», shafi na 634.
  32. Ayazi, «Mahjuriyyat-e Qur'an», shafi na 633.

Nassoshi