Addu'a ta Bakwai cikin Assahifatu Assajadiya

Daga wikishia
Rubutun Sahifah Sajjadiyeh, wanda aka rubuta a cikin rubutun Ahmad Nirizi, wanda aka rubuta a shekara ta 1145 bayan hijira.

Addu’a ta Bakwai, (arabic: الدعاء السابع من الصحيفة السجادية) tana daga addu’ar da aka yi nakalinta daga Imam Sajjad (A.S) addu’a ce da ake yinta lokacin Wahala da saukar Bala’o’i da kuma lokacin bakin ciki, domin samun saukakawar tsanani daga Hannun Allah da kuma samun sabubban rayuwa ta hanyar Rahamar Allah, a cikin wannan addu’ar Imam Sajjad (A.S) ya ksance yana rokon Allah ya warware masa duk wani dabaibayin Rayuwa, haka Imami na hudu cikin wannan addu’a ta bakwai da take littafin Sahifa Sajjadiya ya bayyana cewa dukkanin halittu suna karkashin Iradar Allah, kumma dukkaninsu raunana a gaban Iradar Allah basu da Mataimaki da mai kawo musu dauki, dukkaninsu kaskantattu ne gaban Allah.

Anyi wasiyya da karanta wannan addu’a don kawar da damuwa cikin kebantattun ladubba a cikin karantata bayan sallar Asubahi da kuma tsakanin hudowar rana da faduwarta. Addu’a ta Bakwai cikin sharhin Sahifa Sajjadiya misalin littafin Diyar Ashikin, talifin Husaini Ansariyan cikin Harshen Farisanci da kuma Riyadul As-salikin, talifin Sayyid Ali Khan Madani cikin harshen Larabci.

Masallacin Jami'i Korramshahri

Matsayi da Kimarta

Addu’a ta bakwai ta Sahifa Sajjadiya wata addu’a ce da Hazrat Imam Sajjad (A.S) yake karanta ta a lokacin Wahala da mutum bai iya jur mata ko kuma lokacin saukar wani Bala’i mai tsanani da lokacin bakin ciki da damuwa yana karanta ta ne domin kawar da wadannan abubuwa, cikin wannan addu’a Imami na hudu ya yi bayani wazifar da take kan mutu a dunkule a lokacin afkowar bala’i, [1] Ayatullahi Ali Khamna’I Jagoran juyin juya halin muslunci a Iran shima a watan Isfand shekara 1398 wacce tayi daidai da 2019 lokacin yaduwar Annobar Korona a Iran da sauran Kasashen duniya ya karanta wannan addu’a domin kawar da wannan Annoba [2]

Abubuwan da Take Koyarwa

Abubuwan da Addu’a ta Bakwai take koyarwa sun kasance kamar haka:

  • Allah shine mai warware duk wani Dabaibayi da duk wani tsanani da wahala
  • Baki dayan Halittu suna da’a ga Iradar Allah.
  • wannan Addu’a tana samar da sabubban rayuwa da tasiri cikin sababin rayuwa ta hanyar Ludufin da Rahamar Allah.
  • gudanar Khada’u da Kadar da kudurar Allah [3]
  • Tabbatuwar Iradar Allah.
  • Allah shina Mafakar baki dayan mutane a lokacin bala’i da tsanani da wahala.
  • Raunin dukkanin halittu a gaban Allah.
  • neman Bude kofofi yayewar musibu daga Ubangiji.
  • neman dandanar dadin Amsa addu’a [4]
  • Addu’a don sauke Wajibai da himmatuwa cikin Mustahabbai
  • gudanar Baki dayan al’amura yana kasancewa kadai da Iradar Allah
  • duk wanda Allah ya kaskantar hakika bashi da mai daukaka shi. [5]

Yanda ake Karanta Addu’ar

Ya zo a bara’arin wasu rubuce-rubuce cewa akwai wata hanya da ake bi domin Khatamar Addu’a ta Bakwai ta Assahifa Assajjadiya a Ranar Lahadi zuwa kwanaki Talatin, kowacce rana za a karanta ta kafa goma bayan kammala addu’a sai a karanta zikirin Ya Rabbu ya Rabbu Ya Rabbu da numfashi daya har zuwa yankewarsa, sannan ayi Sujjada a gayawa Allah bukata, wasu sunce kafin fara wannan Addu’a ya kamata a yi salati kafa goma haka kuma kafin farawa da bayan gamawa a yi zikrin ya Allahu kafa Arba’in Sannan karanta wannan addu’a tsakanin hudowar rana da faduwarta da kuma bayan sallar Asubahi tareda nesanta Haramun da cika ciki har tsawon kwanaki talatin, haka kuma zama cikin Dahara (Alwala) da zama ana Fuskantar Alkibla da hallaro da zuciya suna daga cikin sharadinta [6]

Sharhi

Cikin sharhin da aka yi kan Sahifa Sajjadiya anyi Sharhin Addu’a ta Bakwai hakika an shrahin Luggarta da take da wahala, Diyar Ashikin [7] Shuhud Shenakt [8] Riyadul As-Salikin [9] da kuma Fi Zilalu Assahifatu Assajadiyatu [10] an yi sharhinta a littafin ta’alikat Ala Sahifa Sajjadiya talifin Faizul Kashani [11] ya yi Karin bayani cikin [12]

Matani da Tarjama

کانَ مِنْ دُعَائِهِ علیه‌السلام إِذَا عَرَضَتْ لَهُ مُهِمَّةٌ أَوْ نَزَلَتْ بِهِ، مُلِمَّةٌ وَ عِنْدَ الْکرْبِ. یا مَنْ تُحَلُّ بِهِ عُقَدُ الْمَکارِهِ، وَ یا مَنْ یفْثَأُ بِهِ حَدُّ الشَّدَائِدِ، وَ یا مَنْ یلْتَمَسُ مِنْهُ الْمَخْرَجُ إِلَی رَوْحِ الْفَرَجِ. ذَلَّتْ لِقُدْرَتِک الصِّعَابُ، وَ تَسَبَّبَتْ بِلُطْفِک الْأَسْبَابُ، وَ جَرَی بِقُدرَتِک الْقَضَاءُ، وَ مَضَتْ عَلَی إِرَادَتِک الْأَشْیاءُ. فَهِی بِمَشِیتِک دُونَ قَوْلِک مُؤْتَمِرَةٌ، وَ بِإِرَادَتِک دُونَ نَهْیک مُنْزَجِرَةٌ. أَنْتَ الْمَدْعُوُّ لِلْمُهِمَّاتِ، وَ أَنْتَ الْمَفْزَعُ فِی الْمُلِمَّاتِ، لَا ینْدَفِعُ مِنْهَا إِلَّا مَا دَفَعْتَ، وَ لَا ینْکشِفُ مِنْهَا إِلَّا مَا کشَفْتَ وَ قَدْ نَزَلَ بی‌ یا رَبِّ مَا قَدْ تَکأَّدَنِی ثِقْلُهُ، وَ أَلَمَّ بی‌مَا قَدْ بَهَظَنِی حَمْلُهُ. وَ بِقُدْرَتِک أَوْرَدْتَهُ عَلَی وَ بِسُلْطَانِک وَجَّهْتَهُ إِلَی. فَلَا مُصْدِرَ لِمَا أَوْرَدْتَ، وَ لَا صَارِفَ لِمَا وَجَّهْتَ، وَ لَا فَاتِحَ لِمَا أَغْلَقْتَ، وَ لَا مُغْلِقَ لِمَا فَتَحْتَ، وَ لَا مُیسِّرَ لِمَا عَسَّرْتَ، وَ لَا نَاصِرَ لِمَنْ خَذَلْتَ. فَصَلِّ عَلَی مُحَمَّدٍ وَ آلِهِ، وَ افْتَحْ لِی یا رَبِّ بَابَ الْفَرَجِ بِطَوْلِک، وَ اکسِرْ عَنِّی سُلْطَانَ الْهَمِّ بِحَوْلِک، وَ أَنِلْنِی حُسْنَ النَّظَرِ فِیمَا شَکوْتُ، وَ أَذِقْنِی حَلَاوَةَ الصُّنْعِ فِیمَا سَأَلْتُ، وَ هَبْ لِی‏ مِنْ لَدُنْک رَحْمَةً وَ فَرَجاً هَنِیئاً، وَ اجْعَلْ لِی مِنْ عِنْدِک مَخْرَجاً وَحِیاً. وَ لَا تَشْغَلْنِی بِالاهْتِمَامِ عَنْ تَعَاهُدِ فُرُوضِک، وَ اسْتِعْمَالِ سُنَّتِک. فَقَدْ ضِقْتُ لِمَا نَزَلَ بی‌یا رَبِّ ذَرْعاً، وَ امْتَلَأْتُ بِحَمْلِ مَا حَدَثَ عَلَی هَمّاً، وَ أَنْتَ الْقَادِرُ عَلَی کشْفِ مَا مُنِیتُ بِهِ، وَ دَفْعِ مَا وَقَعْتُ فِیهِ، فَافْعَلْ بی‌ذَلِک وَ إِنْ لَمْ أَسْتَوْجِبْهُ مِنْک، یا ذَا الْعَرْشِ الْعَظِیمِ
ya kasance yana addu'a lokacin da wata wahala ta bijiro gare shi ko wani bala'i ya sauka kansa da lokacin bakin ciki. yana cewa ya wanda da shi ne ƙulle ƙullen wahalhalu suke buɗewa, ya wanda da shi ne tsanani da kaifin wahala suke daƙushewa, ya wanda daga gare shi me ake neman mafita zuwa hutu da buɗi, tsanance tsanance sun sauƙaƙa da ikonka, sabubbba sun samu sakamakon luɗdufinka, umarni da hukuncinka sun zartu da ikonka, abubuwan sun gudana kan iradarka, abubuwa suna umartuwa da mashi'arka ba tare da kayi magana, suna kwaɓuwa da iradarka ba tare da sai ka hani ba, kai ne wanda ake kira cikin bala'i, kai ne kaɗai mafaka cikin bala'i, babu abin da yake tunkuɗuwa daga gareta sai abin da ka tunkuɗe, babu abin da yake yaye wa daga gareta sai abin da ka yaye, lallai tabbas wani bala'i ya sauka kaina wanda nauyinsa ya tsananta a kaina, kuma wasu wahalhalu da tsanani sun sauka kaina waɗanda jure musu ya tsananta a kaina, lallai da ikonka ne ka gangarar da su kaina, da kuma mulkinka ne ka fuskanto su gareni. babu mai iya cire mini abin da ka gangaro da shi kaina,lallai ba babu mai iya karkatar da abin da ka turo, kuma babu mai buɗe abin da ka kulle. kuma lallai babu wanda ya isa ya kulle abin da ka buɗe, babu wanda zai iya sauƙaƙa abin da ka tsananta, babu mai iya taimakon wanda ka kunya, ka yi salati ga Muhammad da iyalansa, ka buɗe ya Ubangiji ƙofar yayewarka da falalarka da ihsaninka, ka buɗe ƙofar yayewarka da dabararka, Kuma Ka yi mini hukunci mai kyau game da abin da na yi kuka a kansa. Kuma ka azurtani da ɗanɗana zaƙi na abin da na nema. Kuma Ka yi mini rahama daga gare Ka da kuma yayewa da jin dãɗi. Kuma Ka sanya mini mafita daga gare ka da gaggawa. Kuma kada ka shagaltar da ni mustahabbai daga barin damuwa da kiyaye farillai. haƙiƙa na shifa ƙuntatuwa sakamakon bala'in da ya sauka gareni, kuma na cika da damuwa daga ɗaukar abin da ya faru dani, kai ne kaɗai mai iko kan yaye abin da na jarrabtu da shi, ka tunkuɗe mini abin da ya faɗa cikinsa, ka yi min wannan alfarma duk da nasan ban cancanci hakan daga gareka, ya ma'abocin al'arshi mai girma.[13]



'


Bayanin kula

  1. Mamdohi, Shuhud Wa Shenakti, 2005, juzu'i na 1, shafi 425.
  2. a class="external text" href="https://farsi.khamenei.ir/others-report?id=45072">«دعایی که رهبر انقلاب خواندن آن را در دوران شیوع بیماری توصیه کردند.
  3. Matani Du'a
  4. Matani Du'a
  5. Ansari, Diyar Asheghen, 1371, juzu'i na 4, shafi 103-224
  6. Akbari Savji, Ab Hayat, 1392, oda 186.
  7. Ansari, Diyar Asheghen, 1371, juzu'i na 4, shafi na 103-224.
  8. Mamdouhi Kermanshahi, Shuhud wa Shenakti , 1385, juzu'i na 1, shafi na 425-435.
  9. Hosseini Madani, Riaz Al-Salkin, 1409 AH, juzu'i na 2, shafi na 325-301.
  10. Mughniyeh, Fi Zilali Al-Sahifa al-Sajadiyeh, 1428 AH, shafi na 141-135.
  11. Faiz Kashani, Ta'alikat Ala Al-Sahifa Al-Sajadiyeh, 1407 AH, shafi na 32-33.
  12. class="external text" href="https://www.erfan.ir/farsi/sahifeh7">ترجمه از شیخ حسین انصاریان.
  13. ترجمه از شیخ حسین انصاریان.

Nassoshi

Ayatullahi Al-uzma Khamenei, wanda aka saka a ranar 13 ga Maris, 2018, an duba shi a ranar 12 ga Disamba, 2019.

  • Faiz Kashani, Mohammad Bin Mortaza, Sharhin Ali Sahifa Al-Sajadiyyah, Tehran, Al-Paqeeh da Cibiyar Bincike ta Al-Thaqafiyah, 1407H.
  • Mughniyeh, Mohammad Javad, fi zilali Al-Sahifa al-Sajadiyya, Qum, Dar al-Kitab al-Islami, 1428H.
  • Mamdouhi Kermanshahi, Hasan, Hankali da Ilimi: Fassara da Sharhin Sahifa Sajjadiyeh, tare da gabatarwar Ayatullah Javadi Amoli, Qom, Bostan Kitab, 2005.