Suwaid ɗan Amru

Daga wikishia
Makwancin Shahidan Karbala a cikin Haramin Imam Husaini (A.S)

Suwaid ɗan Amru (Larabci:سويد بن عمرو بن أبي مطاع الخثعمي)ɗan Abi Muɗa'a Khas'ami, shahidin ƙarshe a waƙi’ar Karbala, wanda ya yi shahada jim kaɗan bayan Imam Hussain (AS). Kamar yadda ya zo a cikin ruwayar Muhammad ɗan Jarir Ɗabari (ya rasu a shekara ta 310 bayan hijira) a cikin littafin Tarikh Ɗabari, Suwaid shi ne shahidin Karbala na ƙarshe wanda ya tafi filin,[1] ya yi yaƙi har sai da ya samu rauni, ya faɗi sumamme cikin sauran matattu. Kowa ya ɗauka an kashe shi. Bayan wani lokaci, Suwaid ya ji suna cewa: An kashe Husaini. Sai ya farka ya tashi, ya ɗauki takobinsa, ya yi yaƙi da wannan takobin da yake ɗauke da ita har ya yi shahada. Kamar yadda ɗabari,[2] da Balazri.[3] suka ce Urwa bin Baɗɗan sa’albi da Zaid bin Ruƙad Junabi suka kashe shi. Amma a cikin littafin Tasmiyya Man ƙutila Maa-lhusain (wanda aka rubuta a ƙarni na 2), an rubuta wanda ya kashe shi Hani bin sabit Hazrami.[4] Suwaid bin Amr bin Abi Muɗaa Khas'ami ɗan ƙabilar Khas'am ne. Kamar yadda Samawi (ya rasu a shekara ta 1370 bayan hijira) ya kawo a littafin sa na Absarul Aini, ya kasance mutum ne mai daraja, mai ibada, jajirtacce kuma gogagge a fagen yaƙi.[5]

Bayanin kula

  1. Ɗabari,Tarikh Al-Umam wa Al-Muluk, 1403H, juzu'i na 5, shafi na 446.
  2. Ɗabari,Tarikh Al-Umam wa Al-Muluk, 1403H, juzu'i na 5, shafi na 453.
  3. Balazri, Ansab al-Ashraf, 1397 Hijira, juzu'i na 3, shafi na 204.
  4. Fazil bin Zubair,Tasmiyya Man Qutila ma'al al-Hussein, 1405H, shafi na 28.
  5. Samavi, Absar al-Ain, 2004, shafi na 169.

Nassoshi

  • Amin, Seyyed Mohsen, Ayan-al-Shia, bincike na Hasan Amin, B.T. Belazari, Ahmad bin Yahya, Ansab al-Ashraf (Juzu'i na 3), Bincike: Mohammad Baqer Mahmoudi, Beirut, Dar al-Taraif na jarida, 1977 AD/1397 AH. Samavi, Mohammad, Ibsar al-Ain fi Ansar al-Hussein, Qom, Zamzam Hedayat, 2004. Tabari, Muhammad bin Jarir, Tarihin Al'ummai da Al-Muluk, Beirut, Cibiyar Al-alami, 1403H. Fazil bin Zubair, sunan wanda ya kashe Hussaini, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da dana, da dan’uwansa, da iyalansa, da mabiyansa, wanda Sayyid Muhammad Reza Hosseini Jalali ya yi bincike a kansa, a Qom, shekara ta 1405 bayan hijira.