Shin Akwai Mai Taimako Da Zai Taimaka Mini

Hal Min Nasirun Yansurni (Larabci هل من ناصر ينصرني) Shahararriyar jumla daga bakin Imam Husaini (A.S) a ƙarshen mintunan da suka rage masa a rayuwa a ranar Ashura, a cewar Jawad Muhaddisi cikin al'adun Ashura wannan jumla da wannan ma'anar ba ta zo ba cikin litattafan tarihi,[1] sai dai cewa wasu litattafai da suke da alaƙa da waƙi'ar Karbala sun kawo wata jumlar kwatankwacinta.[2]
Bisa naƙalin marubutan waƙi'o'in Ashura lokacin da Sahabban Imam Husaini (A.S) suka yi shahada sai ya zamana shi kaɗai ya rage a raye, sai ya furta wannan jumloli kan harshensa
Shin akwai wani mai bada kariya da zai baiwa haramin Manzon Allah? Kariya shin akwai wani mai kaɗaita Allah da yake jin tsoron Allah game da mu? shin akwai wani mai jin kuka da yake fata daga Allah cikin jin kukanmu ? shin akwai mai taimako da yake fatan daga abin da yake wurin Allah cikin taimakonmu?[3] Shin akwai wani mai jin kukarmu da zai nuna fatan rahamar Allah a garemu? Shin akwai wani mai taimako da ke ganin ladan da Allah ya tanada ta hanyar taimakonmu? Shin akwai mai goyon baya da ya dogara ga jinƙan Allah wajen tashi[4] don taimaka mana?[5]
Imam Husaini (A.S) lokacin da yake gidan Bani Muƙatil yayin da ya gayyaci Ubaidullahi Bin Hurri Ju'ufi ya zo ya taimaka masa sai Ubaidullahi ya nemi ya yi masa uzuri, sai Imam ya ce masa ya tashi ya fita daga wurin, saboda matuƙar ya ji sautin neman taimakon Imam sannan yaƙi amsawa to Allah ya halaka shi,[6] wasu ba'ari suna ganin taken “Labbaika Ya Husaini” matsayin amsa kiran tamaikonsa a ranar Ashura.[7]
A cikin fim ɗin ranar Ashura wanda Shahram Asadi ya shirya wanda aka yi shi game da waƙi'ar Karbala, Jarumi na farko a cikin Fim ɗin ya kasance wani matashi sabon muslunta, ya bada labarin cewa ya ji wata murya cikin kunnensa tana ta maimaituwa “Wanene zai taimaka mini?” sai ya bibiyi sawun wannan murya har zuwa Karbala.[8]
Wannan baitukan waƙa ne guda biuyu da ake dangantawa da Nasirid-dini Shah Ƙajar:
Tarjama: Idan a wancan rana na ji gayyatar aboki, Da na cimma burina a wancan ran.[9]
Bayanin kula
- ↑ Muhaddisi, Farhang Ashura, 1376, shafi na 471
- ↑ Sayyid Ibn Tawus, Allahouf, 1348, shafi na 116; Ibn Nama Hali, Muthir al-Ahzan, 1406H, shafi na 70.
- ↑ https://makarem.ir/maaref/fa/article/index/254217/
- ↑ https://makarem.ir/maaref/fa/article/index/254217/
- ↑ Sayyid Ibn Tawus, Allahouf Ala Qatla Al-Tofou, shekara ta 1348 na kalandar Iran, shafi na 116
- ↑ Tabari, Tarikh Al-Umam wa Al-Muluk, 1387 Hijira, juzu'i na 5, shafi na 407
- ↑ «شعار «لبیک یا حسین» به معنای اجابت دعوت سیدالشهدا(ع) است»، Kamfanin labarai na Mehr.
- ↑ «نگاهی به فیلم روز واقعه»،"Paygah-e Etela-Resani-ye Hoze".
- ↑ https://www.karbobala.com/poems/info/866Karbo wa Bala" wani shafin yanar gizo ne na musamman da ya ƙware kan batutuwa masu alaƙa da Imam Husaini (A.S).
Nassoshi
- Ibn Nama Hilli, Jafar Bn Muhammad, Muthirul Ahzan, ƙum, mazhabar imam al-Mahdi, 1406H.
- Sayyed Ibn Tawoos, Allahouf Ali ƙatali Al-Tofouf, Tehran, Jahan Publishing House, 1348.
- «نگاهی به فیلم روز واقعه»، ، پایگاه اطلاعرسانی حوزه، در مجله پاسدار اسلام، شماره ۱۶۴، مرداد ۱۳۷۴ش.
- Tabari, Muhammad bin Jarir, Tarkh Al'umama wa Al-Muluk, tahkik Muhammad Abulfazl Ibrahim a Beirut, Darul Trath, 1967 miladiyya/1387H.
- Mohaddisi, Javad, Farhang Ashura, ƙom, shahararren bugu, 1376.
- «شعار «لبیک یا حسین» به معنای اجابت دعوت سیدالشهدا(ع) است»"Kamfanin dillancin labarai na Mehr, kwanan wata da aka saka labarin: 10 ga watan Mordad 1401 (kalanda Iran), kwanan wata da aka duba: 11 ga watan Azar 1402 (kalanda Iran)."