Muƙamin Sayyida Ruƙayya

Daga wikishia
File:حرم رقیه دختر امام حسین ع در شهر دمشق.jpg
Haramin Sayyada Rukayya

Haramin Sayyida Ruƙayya (Larabci:حرم السيدة رقية) a birnin Damascus yake, ana danganta shi ga Ruƙayya ɗiyar Imam Husaini (A.S) wannan haramin dai shi ne hubbare na biyu a tsakanin 'yan Shi'a a birnin Damascus bayan haramin Sayyida Zainab ‘yar Ali, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi. Da kuma gare ta. An fara danganta wannan wuri ga Uwargida Ruƙayyah a karni na sha huɗu bayan hijira; Kafin haka dai an san cewa a wasu madogara na karni na goma a matsayin makabartar ɗiyar Imam Husaini (AS) amma ba tare da ambaton sunan Ruƙayyah ba. Wasu sun yi shakku kan yadda aka jingina wannan hubbaren ga Uwargida Ruƙayyah, wasu daga cikinsu suna ganin cewa ita ce makabartar Ruƙayyah ‘yar Imam Ali, tsira da amincin Allah su tabbata a gare su, wasu kuma suka ce ita ce makabartar Ruƙayya ɗiyar Imam Ali (A.S), tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi. Wasu daga cikinsu sun ce a nan ne wurin kan Imam Husaini (A.S). Akwai wani shahararren labari da ya faru a loƙacin da ake sake gina wurin,mai wannan kabari yarinya ce karama. A yau, Haramin Sayyida Ruƙayyah ya kunshi wani fili mai faɗan, gini kuma ya kasance cakude da fasahar gine-ginen muslunci da na gida kalar Iran.

Matsayi

Hubbaren Sayyida Ruƙayyah a birnin Dimashk da ake dangantawa da Ruƙayyah 'yar Imam Husaini (A.S), a matsayinsa na hubbare na biyu a cikin haramin, bayan haramin Sayyida Zainab (S) ga Shi'a a birnin Damashk.[1] Wannan wurin ibada yana ɗaya daga cikin tsoffin kasuwannin Damashk mai suna "Kasuwar Al-Amara, kusa da Bab Al-Faradis (ɗaya daga cikin kofofin tsohuwar Damashk), kuma kusa da masallacin Umayyawa. Masallaci da Kasuwar Sham.[2]

Danganta wannan wuri zuwa Gareta

Akwai sabani game da jingina haramin Uwargida Ruƙayyah ga Ruƙayyah ‘yar Imam Husaini (a.s), ko kuma Ruƙayyah ‘yar Imam Ali (a.s), .bisa ra’ayin wani malamin tarihi mai suna Ahmad Kami Yar, asalin ƙabarin sayyida Ruƙayya yakasance gurin da aka binne kan Imam Husain (a.s) a Dimashk, wannan shi ne abin da wasu suka tafi akai,kuma sun ɗauke shi a matsayin gurin da aka binne kan imamu Husain. ya zo a cikin litatafan da suke da alaƙa da gwamnatin Usmaniyawa cewa, shi wanna guri an san shi a matsayin Maƙami na Sayyida Ruƙayya, kuma ya zo a cikin wasu litatafai dayawa, kuma ƙari akan cewa kabarin sayyida Ruƙayya ne, an anbaci cewa akwai kan imamu Husain a guri, Da bambancin cewa an san Ruƙayyah a cikin daɗaɗun latattafai waɗanda suka gabata a matsayin ‘yar Imam Ali (a.s), kuma a litattafai na bayabaya ana kiranta ‘yar Imam Husaini (a.s).[3]

Ance dalilin da yake nuna cewa, wannan ƙabarin na sayyida Ruƙayya ne, an sameshi a ƙarni na goma ne, a littafin Muhammad ɗan Abi ɗalib Al-ha’iri Alkaraki wanda ya rasu a shekara ta 955 a cikin wani littafin shi mai suna Tasliyatul Majalis.[4] Inda ya ce ya ga wani rushashshen gini a gabashin masallacin Umayyawa da ke birnin Damashk, wanda a baya masallaci ne, mai dauke da sunayen Manzon Allah, (s.a.w) da Imamai goma sha biyu (a.s), a rubuce a kan wani dutse a kofarsa. Haka nan kuma an rubuta a kansa cewa wannan kabarin Sayyada sarauniya ‘yar Husaini ɗan Amirul Muminin (a.s).[5]

Sayyid Muhsin Amin ya yi rubutu game da wannan wurin ziyara a cikin littafin shi mai suna A’ayun Shi'a, kawai cewa ƙabarin da aka danganta ga Ruƙayyah 'yar Imam Husaini, wani wurin ziyara ne a unguwar Al-Amara a birnin Damashk, wanda Mirza Ali Asgar Kan ya sabunta shi. waziri na Iran a shekara ta 1323 Hijira, kuma an rubuta wannan da kwanan wata a saman kofa.[6]

Ya zo a cikin littafin Daneshnameh Imam Husaini (a.s), bayan da ya nazarci abin da aka jingina shi ga Ruƙayya (a.s)cewa bisa la’akari da madogaran ruwayoyi da na tarihi, ba zai yiwu a ba da tabbatacciyar magana a kan wannan haramin ba. . Amma mu'ujizar da aka gani da kuma ake gani daga wannan wuri suna ƙarfafar matsayinsa, don haka wajibi ne a girmama wannan wuri.[7]

Kissar Mamayar da Ruwa ya yi wa Kabarinta da kuma Tone shi

Wasu majiyoyin ƙarni na biyu da suka gabata sun yi nuni da cewa labarin tone ƙabari da gano gawar Ruƙayyah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare ta, na nuni da cewa ƙabari na wata yarinya ne.[8] An ce akalla mutane uku ne suka ruwaito wannan labari, Na farkonsu shi ne Muumin Shablangi a cikin littafin Nurul Al-Absar, malamin Sunna a karni na sha uku,[9] wanda shi kuma ya bayyana ma'abocin ƙabari da cewa Ruƙayyah 'yar Imam Ali, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi. , kuma ya ce gawar da aka gani a lokacin da suka fitar da ita daga cikin ƙabarin don sake ginshi, ita ce gawar budurwa, wadda batabalaga ba.[10]

Sheikh Muhammad Hashim Al-Khurasani (ya rasu a shekara ta 1352 bayan hijira) ya yi la’akari a cikin littafinsa Muntakab Al-Tawarik, cewa wannan hubbare na Ruƙayya ‘yar Hussein ne, kuma ya kawo labarin barnar da aka yi wa kabarin dalla-dalla. Ya kuma ƙara da anbaton karamuminta.sheik Muhammad Hashim Al-kurasani yace, Sayyd Ibrahim Al-Dimashƙi yana da ‘ya’ya mata uku a shekara ta 1280 bayan hijira, tsawon dare uku a jere kowacce daga babba zuwa karama, sai ta ga Ruƙayya a mafarki tana cewa mata: “Ki gaya wa babanki. cewa ƙabarina ya cika da ruwa, yazo ya gyara shi.” Malam Ibrahim bai damu ba, ya yi mafarkin ‘ya’yansa mata har dare na hudu, sai da shi da kanshi ya ga Ruƙayya, a cikin baccinshi. Bayan haka, a gaban malaman Shi’a da Sunna, suka tono ƙabarin, sannan Malam Ibrahim ya yi ta ƙoƙari da kaikawo har sai da aka gyara shi.[11] A cewar mawallafin littafin Mausu’a ta Imam Husaini, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, duk da ɗimbin dalilai na yaɗawa da naƙalto waɗannan abubuwa; Amma babu wanda ya ruwaito wannan labari sai wadanda suka dau alhakin wannan haramin, kuma Malam Mohsin Al-Amin bai yi nuni da hakan ba, duk da kasancewarsa a yankin.[12]

a cewar marubutan kundin littafin daneshnameh Imam Husaini (a.s) duk da cewa akwai samuwar kwadayi cikin rubuta wadannan rahotannin wannan labari, amma tare da haka babu wadanda suka nakalto wannan labari in banda hadiman wannan harami Sayyid Muhsin Amin shima tare da kasancewar ya zauna wannan unguwa amma kuma bai yi ko da ishara ba kan wannan labari.[13]

File:تصویر هوایی حرم حضرت رقیه.jpg
Hotan Haramin Sayyada Rukayya da aka dauko shi da jirigin sama

Takaitaccen Tarihin sake gina wanna ƙabari

Babu wani bayani game da gina haramin farko da tsarin sake gina shi har zuwa karni na tara bayan hijira.[14] kamar yadda ɗan Tulun al-Dimashƙi, marubucin littafin Ashshazarat Azzahabiya ya faɗa a rabinƙarni na biyu na karni na tara. Sarki Azzahiri Bardabak, wanda Sarkin Mamluki Sulɗan ya zama gwamnan Damashk a shekara ta 871. Ta hanyar sake gina haramin. ɗaya daga cikin allunan da ke cikin haramin na nuni da cewa Mirza Baba Mustafi al-Kilani ya sake gina haramin a shekara ta 1125 bayan hijira.[15] Sannan kuma a karshen zamanin daular Usmaniyya, Mirza Ali Asgar Khan Atabak babban mai ba da shawara na kasar ƙajar ya sake gina wurin harama a shekara ta 1323H.[16]

Kamar yadda wasu malaman tarihi suka ruwaito cewa, tun farko sarakunan Ayyubi (a farkon mulkinsu a shekara ta 567 bayan hijira) sun gina wani ɗan karamin ƙabari mai dauke da hubbare da ƙubba a cikin kabarin Ruƙayya, amincin Allah ya tabbata a gare ta, wanda yake cikin masallacin kan [Ra’asul] Hussain. sannan aka gyara shi kuma aka gina shi a shekara ta 1125 Hijira da 1323.[17]

A shekara ta 1343 bayan hijira, Kamal da Muhammad Ali Al Nizam, 'yan Shi'a na Damashk, sun sake gina ginin da kuɗinsu. Kafin haka, ginin hubbaren Sayyida Ruƙayya wani daki ne kuma ƙabari yana a tsakiyar shi, akwai wani karamin masallaci a gefenshi, kuma faɗin ginin bai wuce murabba'in mita 60 ba a lokacin.[18]

Faɗaɗa ƙabarin

A farkon shekarun 1970 ne wasu 'yan Shi'a da suka haɗa da Nasarullah Khalkali da Imam Musa As-Sadar suka kafa wani kwamiti da nufin faɗaɗa haramin Sayyida Ruƙayyah, inda suka sayi gidaje da shaguna da dama da ke kusa da shi. Aikin raya ginin ya fara ne a shekara ta 1404 bayan hijira, daidai da shekara ta 1984 miladiyya, kuma mafi yawanshi kuma ya kammala ne a shekara ta 1410 bayan hijira.[19]

A wani sabon ci gaba da aka samu, jimlar dakin ibadar ya kai murabba'in murabba'i 4,500, wanda murabba'in mita 600 ya haɗa da tsakar gida da wani babban fili, sauran kuma gine-gine ne na ƙasa, wani masallaci mai faɗin murabba'in mita 800. an kuma gina shi a kudancin ginin. Wurin wurin ibadar da hanyoyinshi a cikin sabon ginin ya kai murabba'in mita 2,600.[20]

Fannin gini

Nau'in gine-ginen da aka yi amfani da shi wajen faɗaɗa hubbaren Sayyida Ruƙayya a baya-bayan nan, shi ne tsarin gine-ginen Musulunci na Iran,[21] kuma an ce kayayyakinshi da kayan adonsa sun sha bamban da sauran abubuwan tarihi na gine-gine da na addini a Damash.[22] Ginin ɗakin ibada yana da kofofin shiga da dama, mafi muhimmanci daga cikinsu shi ne kofar kudu maso yamma, a saman wannan kofar akwai wani baka da aka lullube da kayan ado, a sama kuma an rubuta cewa, “Wannan shi ne hubbaren Madam Ruƙayyah ‘yar gidan sarautar shahidi Husaini a Karbala”[23] A saman kan kofar akwai wata minarat mai nisan mita 34 daga kasa. Ƙofar da ke da alaƙa da babban farfajiyar gidan ibadar tana da siffar rectangular kuma tana kewaye da hanyoyi.[24] Babban bangaren ginin dai ya haɗa da babban ɗakin ibada na yamma, da kuma manya-manyan masallatai guda biyu a tsakiya daga gabas, ta yadda kowane bangare yana da kofar shiga harabar farfajiyar da ke arewa, kuma a kusa da wurin ibadar akwai guraren dake rufi da madubai. An lullube rufin ɗakin ibadar da kayan ado, kuma an lullube sassanshi da muƙarnai, tsakanin duwatsun ana iya ganin rubutun ayoyin kur'ani da hadisai na falalar Ahlul Baiti, tsira da amincin Allah su tabbata a gare su.[25]

Haramin Sayyada Ruƙayya yana tsakiyar garin Dimashk, kuma a kan shi akwai wani akwati na katako wanda aka lulluɓe da koren kyale mai ɗauke da ayoyin Alƙur’ani. A sama da ƙabarin akwai wani hubbare na azurfa da aka gina a shekara ta 1376 bayan hijira/1956, wanda cibiyar Banu Zahra da ke birnin Tehran ta bayar da ita ga hubbaren Madam Ruƙayyah, wannan dakin ibada yana tsakanin sabon dakin ibada mai fentin azurfa da kuma mafi girma. wanda aka gina shi a garin Isfahan kuma aka sanya shi a shekara ta 1414H/1994 miladiyya, kuma sama da babban dakin ibadar yana da tsayin mita 14 daga kasa, sannan an lullube samanshi da kayan ado na geometric, kuma saman cikinsa an yi shi da muƙarnai. da madubai.[26]

Wanda yake shugabatar gurin

Bayan labarin mafarkin ‘ya’yan Sayyid Ibrahim al-Dimashƙi, Sulɗan Abdulmajeed (ɗaya daga cikin sarakunan Daular Usmaniyya) ya mika wa Sayyid Ibrahim rikon dukkan hubbaren Zainabiyya, da hubbaren Ruƙayyah, Sakina, da Ummu Kulthum. Bayan Sayyid Ibrahim al-Dimashƙi dansa da jikansa suka zama masu kula da wadannan wurare,[27] kuma a yanzu Ahmed al-Ashƙar ya zama mai kula da haramin Sayyida Ruƙayya.[28]

Harin Ta’addanci akan Makamin Sayyida Ruƙayya

A shekarar farko ta yunkurin 'yan ta'addar takfiriyya a kasar Siriya, Sheik Abbas al-Laham, limami na maƙami Sayyida Ruƙayya, 'yan ta'adda sun kai hari a gaban kofar shiga haramin, kuma ya yi shahada bayan da aka yi musu ruwan harsashi da dama.[29] ‘Yan ta’addan da ke a yankin Jobar da ke gabashin Dimashƙ sun yi ta harba harsashi, inda aka yi ta kai farmaki a kan hubbaren Sayyida Ruƙayyah sau da yawa, amma harsashin ba su kai ga cima hadafi ba.[30]

Bayanin kula

  1. Qaidan, Amakin Ziyarti Siyahati Suriya, 2007, shafi na 57.
  2. Khameyar, Asare Payambar (S.A.W) wa Ziyaratgahaye Ahlul Baiti (A.S) dar Suriye, 1393, shafi na 237.
  3. Khameyar, Asare Payambar (S.A.W) wa Ziyaratgahaye Ahlul Baiti (A.S) dar Suriye, 1393, shafi na 237.
  4. Mohammadi Raishahri, Daneshnameh Imam Husaini (AS), 1388, juzu'i na 1, shafi na 389.
  5. Haeri, Teslia Majlis, 1418 AH, juzu'i na 2, shafi na 93.
  6. Amin, Aayan al-Shia, 1421 AH, juzu'i na 7, shafi na 34. ↑
  7. Mohammadi Rishahri, Daneshnameh Imam Husaini (AS), 1388, juzu'i na 1, shafi na 393.
  8. Khameyar, Asare Payambar (S.A.W) wa ziyaratgahaye Ahlul Baiti (A.S) dar Suriye shafi na 241
  9. Khameyar, Asare Payambar (S.A.W) wa ziyaratgahaye Ahlul Baiti (A.S) dar Suriye shafi 241
  10. Shablanji, Noor al-Absar, Razi Publishing House, shafi na 195.
  11. Khameyar, Ayyukan Manzon Allah (SAW) da wuraren ibadar Ahlul Baiti (a.s) a Sham, 1393, shafi na 250
  12. Khorasani, Muntakabul Al-Tawarikh, 2008, shafi na 388.
  13. Mohammadi Rishahri, Daneshnameh Imam Husaini (AS), 1388, juzu'i na 1, shafi na 392.
  14. Khameyar, Ayyukan Manzon Allah (SAW) da wuraren ibadar Ahlul Baiti (a.s) dar Suriye, 1393, shafi na 246.
  15. Khameyar, Ayyukan Manzon Allah (SAW) da wuraren ibadar Ahlul Baiti (a.s) a Sham, 1393, shafi na 246.
  16. Qaidan, Amakin Ziyarati wa Siyahati Siriya, 2007, shafi na 57 da 58; Moghadis, Jagoran Wuraren Hajji a Suriye, 2009, shafi na 119 da 120.
  17. Khameyar, Ayyukan Manzon Allah (SAW) da wuraren ibadar Ahlul Baiti (a.s) a Sham, 1393, shafi na 247.
  18. Khameyar, Ayyukan Manzon Allah (SAW) da wuraren ibadar Ahlul Baiti (a.s) a Sham, 1393, shafi na 250.
  19. Qaidan, Amakin Ziyarati Siyahati Suriye, 2007, shafi na 58; Makdisi, Rahnamaye Amakin Ziyarati dar Kishware Suriye, 2009, shafi na 120.
  20. Makdisi, Rahnamaye Amakin Ziyarati dar Kishware Suriye, 2009, shafi na 121
  21. Khameyar, Asare Payambar (S.A.W) da wuraren ibadar Ahlul Baiti (a.s) a Sham, 1393, shafi na 250.
  22. Khameyar, Asare Payambar (S.A.W) wa amakain ziyaratri Ahlul-baiti (a.s) dare Suriye, 1393, shafi na 251
  23. Khameyar, Asare Payambar (S.A.W) wa Amakin Ziyarati Ahlul Baiti (a.s) dar suriye, 1393, shafi na 251
  24. Khameyar, Asare Payambar (S.A.W) wa amakain ziyaratri Ahlul-baiti (a.s) dare Suriye, 1393, shafi na 251-252
  25. Khameyar, Asare Payambar (S.A.W) wa amakain ziyaratri Ahlul-baiti (a.s) dare Suriye, 1393, shafi na 251
  26. Khameyar, Asare Payambar (S.A.W) wa amakain ziyaratri Ahlul-baiti (a.s) dare Suriye, 1393, shafi na 251-252
  27. خراسانی، منتخب التواریخ، ۱۳۸۸ش، ص۳۸۸؛ «آیا تروریست‌ها به حرم حضرت رقیه حمله کرده‌اند»، سایت مشرق‌نیوز
  28. دیدار تولیت حرم حضرت رقیه با تولیت آستان قدس رضوی
  29. «آیا تروریست‌ها به حرم حضرت رقیه حمله کرده‌اند»، سایت مشرق‌نیوز
  30. «آیا تروریست‌ها به حرم حضرت رقیه حمله کرده‌اند»، سایت مشرق‌نیوز

Nassoshi

  • «آیا تروریست‌ها به حرم حضرت رقیه حمله کرده‌اند»، سایت مشرق‌نیوز، تاریخ درج مطلب: ۸ آذر ۱۳۹۳ش، تاریخ بازدید: ۲۰ مرداد ۱۴۰۱ش.
  • Amin, Seyyed Mohsen, Ayan al-Shi'a, Beirut, Dar al-Taqran, 1421H.
  • Haeri, Muhammad bin Abi Talib, Tasliya Majlis da Zaina Majlis, Qum, Al-Maarif Islamic Foundation, 1418H.
  • Khameyar, Ahmed, Asare Payambar (S.A.W) wa amakin ziyarati Ahlul-baiti (A.S) dar Suriye, Cibiyar Nazarin Hajji da Ziarat, Tehran, Mash'ar, 2013.
  • Khorasani, Mohammad Hashem, Muntakab Tawarikh, Tehran, kantin sayar da littattafai na Islama, bugu na 7, 2008.
  • «زندگی نامه شیخ نبیل الحلباوی»، سایت مجمع جهانی اهل‌بیت(ع)، تاریخ بازدید: ۲۰ مرداد ۱۴۰۱ش.
  • Shablanji, Momin bin Hasan, Noor al-Absaar fi Manaqib al-Bayt al-Nabi al-Mukhtar (a.s), Qom, Razi, Bita.
  • Qaidan, Asghar, Amakain ziyarati siyahati Suriye, Tehran, Mash'ar, 2007.
  • Mohammadi Rishahri, Mohammad et al., Daneshanameh Imam Hossein bar Paye Alqur'ani, Hadisi wa Tarikh, Qum, Darul Hadith, bugu na biyu, 2018.
  • Moghadis, Ehsan, Rahnamaye ziyarati dar Kishaware Suriye), Tehran, Mash'ar, 2009
  • نماز جمعه حتی یکبار تعطیل نشد، خبرگزاری رسمی حوزه، تاریخ انتشار: ۱۸ آذر ۱۳۹۳ش، تاریخ بازدید: ۲۰ مرداد ۱۴۰۱ش.