Jump to content

Isra'il (Laƙabi)

Daga wikishia
Ka da ku kuskure da gwamnatin Isra'ila

Isra'il (Larabci: إسرائيل) laƙabi ne na annabi Yaƙub, kamar yadda littafin Tafsir Majma'ul Bayan ya yi bayani, a harshen Abraniyanci Isra'il yana nufin zaɓaɓɓen Allah ko bawan Allah.[1] Shaik Ɗusi yana ganin wannan kalma ta Isra'il ta harhaɗu ne daga kalmomi guda biyu “Isra” wace take nufin bawa da kuma "Il" da take da ma'anar Allah, da haka ta ba ba ma'anar bawan Allah.[2] Malaman tafsiri na Shi'a suna ganin cewa abin nufi daga kalmar Isra'il da ta zo a aya ta 93 suratul alu imran da aya ta 58 suratul an'am shi ne Yaƙub.[3] Da wannan dalili ne ne ake kira ƴaƴa da zuriyar Yaƙub da sunan Bani Isr'ail.[4]

A cikin Attaura ya zo cewa bayan Allah ya yi kokawa tare da Yaƙub ya ji irin ƙarfin da yake da shi da galaba da ya yi kan Allah da ɗan'adam, sai Allah ya kira shi da Isra'il.[5]

Bayanin kula

  1. Tabarsi, Majma' al-Bayan, 1415ƙ, juzu'i. 1, shafi. 182.
  2. Sheikh Tusi, Al-Tebyan, Dar Ihya Al-Turahat Al-Arab, juzu'i. 1, shafi. 180.
  3. Tabarsi, Majma al-Bayan, 1415ƙ, juzu'i. 2, shafi. 344; Subhani, Manshru al-Jawid, 1391SH, juzu'i. 11, shafi. 325.
  4. Rouhi, Simaye Bani Isra’il Dar Ƙur’an Wa Ahdaini, 1384SH, shafi. 58.
  5. Ahde Atiƙ, 1393SH, juzu'i. 1, shafi na 234-236.

Nassoshi

  • Rouhi, Abul-Fadl, Simaye Bani Isra'il Dar Qur'ai Wa Ahdaini, a cikin Mujallar Marafat, lamba. 95, Nuwamba 1384SH.
  • Subhani, Jafar, Manshor Jawid, Ƙum, Gidauniyar Imam Sadiƙ (AS), 1390SH.
  • Sheikh Tusi, Muhammad ibn Hassan, Al-Tebyan fi Tafsirin Ƙuran, Beirut, Wallafar Dar Ihya al-Turat al-Arab, babu kwanan wata.
  • Tabarsi, Fadl ibn Hassan, Majmu’ul al-Bayan fi Tafsir al-Quran, Beirut, Wallafar Gidauniyar Al-Alami, 1415ƙ..
  • Ahadu al-Atiq (Juzu'i na 1: Littattafan Sharia ko Attaura), wanda Pirouz Sayar ya fassara, Tehran, Mawallafar Hermes, 1393SH.