Fatawar haramcin cin mutuncin jagorori masu alfarma na Ahlus Sunna

Daga wikishia

Fatawar Haramcin Zagi Cin Mutuncin Jagorori Masu Alfarma Na Ahlus Sunna (arabic: فتوى تحريم الإساءة لمقدسات أهل السنة ) ita ce fatawar Ayatullahi Khamna'i Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran game da Haramcin Zagi da cin mutuncin Ramzin Ahlus-Sunna da matan Annabin Muslunci (S.A.W) An fitar da wannan fatawa ne a matsayin martani ga cin mutuncin da Yasir Al-Habib, Malamin Shi’a dan kasar Kuwait da yake yi ga A’isha Matar Annabi (S.A.W) da kuma neman fatawar gamayyar malaman Shi’a na Saudiyya kan wannan batu. Fatawar haramcin zagi da cin mutuncin Ahlus-Sunnah ta yadu da yawa a kafafen yada labarai na Larabawa. ta kuma yi tasisi na gaske Har ila yau, wannan fatawa ta bada gudummawa cikin hadin kan Musulmai.

Fage

An fitar da fatawar a kan kare alfarmar Ahlus-Sunna ne biyo bayan zagin Yasir al-Habib, wani malamin Shi’a daga Kuwait, ga Aisha matar Annabi (S.A.W). Habib ya sha magana a kan A’isha da Umar bin Khaddab, wadanda su ke da matsayi na musamman a wajen Ahlus-Sunna.[1] Kuma a shekara ta 1389 shamsi, Yasir Habib ya gudanar da wani bikin murnar ranar mutuwar A’isha Matar Annabi (S.A.W) a birnin Landan tare da yi mata kalaman batanci [2] An watsa wannan biki na Yasser. a Tashar tauraron dan Adam ta Al-Habib mai suna Fadak [3] A ranar tunawa da rasuwar halifa na biyu ne aka yi bikin. An kuma watsa wannan shirin ta hanyar sadarwar tauraron dan adam.[4]

yada kalaman Al-Habib ya haifar da fushi da nuna rashin amincewar Ahlus-Sunna da kuma haifar da martani a duniyar Musulunci, musamman na kasashen Ahlu-Sunna, kuma ya haifar da matsaloli da dama ga mabiya Shi'ar Kuwait da Saudiyya, yaduwar Mazhabr Shi'anci a kasashan Larabawa da,Kasashen Musulunci ya samu cikas duka sakamakon wannan kalaman batanci, kuma maganar Al-Habib wani taimako ne daga Allah da zai sanaya mutane su yi bincike su san hakikanin Shi'anci.[5] bayan wannan kalaman batanci na Yasir Habib Malaman Shi'a na Saudoiya sun aiko da neman Fatawa zuwa ga Jagoran juyin juya halin muslunci na Jamhuriyar Musulunci ta Iran tare da bukatar ya bayyana ra'ayin sa na shari'a game da " zagin A'isha da kuma yin kalaman batanci kanta ta"[6] Bayan wadannan abubuwan ne malaman Shi'a na Saudiyya suka tuntubi jagoran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei nassin fatawa.

Matanin Fatawar Ayatullah Khamenei

Ayatullah Khamenei yayin da yake mayar da martani ga binciken malaman Shi'a na yankin Ahsa na kasar Saudiyya game da zagin A'isha Matar Annabi (S.A.W) cin mutuncin mutane.

Yanda wannan Fatawa Ta Sanya Martani da Canjin Tunani

Fatawar Ayatullah Khamna'i:
'“Zagin Jagororin ‘yan’uwa Ahlus-Sunnah da suka hada da zargin matar Manzon Allah A’isha haramun ne. Wannan al’amari ya hada da matan annabawa baki daya musamman Annabinmu Annabi Muhammad (S.A.W).

(Taskar kwanan wata, Jaridar Resalat, 11 Mehr 1389, shafi na 3.)[7]

Fatawar cin mutuncin Ahlus-Sunna ta kasance tare da canjin tunani da martani a kafafen yada labarai da kasashen Larabawa. Misali, jaridun "Al-Anba" da "Al-Rai Al-Aam" da aka buga a Kuwait, gidan yanar gizon "Mahit", "Al-Safir" da "Al-Antaqad" na Labanon, "Al-Watan" da "Akaz". " Jaridu a Saudiyya, jaridar "Al-Hayat" da aka buga a London, jaridar "Al-Shoroq" Mirsa da gidan rediyo da talabijin na kasar da wasu tashoshin tauraron dan adam na Larabawa sun ruwaito shi.[8]

Tashar talabijin ta Aljazeera a cikin shirin "Maura'ul-Khobar" tare da halartar masana ta yi nazari kan wannan fatawa da irin rawar da take takawa wajen hadin kai da kusanci a tsakanin mabiya addinin Musulunci daban-daban.[9]

Hakazalika masana daban-daban a kasashen Larabawa sun mayar da martani kan fatawar cin mutuncin Ahlus-Sunnah. Daga cikin su Sheikh Ahmad Al-Tayeb Shehin Malamin Jami’ar Azhar ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa, an fitar da wannan fatawa a daidai lokacin da ya dace domin hana rarrabuwar kawuna da kuma rufe kofofin fitina, kuma ta bayyana sha’awa da kishin hadin kan al’ummar musulmai. Musulmai.Su ma malaman addinin kasar Labanon suna goyan bayan hakan, sun dauki fatawa wajen kawar da makirce-makircen makiya. ga masu niyyar kawo cikas ga hadin kan al'ummar musulmi, bayanin su na karshe ya goyi bayan fatawar Ayatullah Khamene'i.

Rohi wakilan Ahlus Sunna a majalisar musulinci ta Iran a cikin wata sanarwa da suka fitar, sun dauki wannan fatawa a matsayin abin alfahari da karfafa gwiwa ga Ahlus Sunnar kasar [15] Malaman Sunna na lardin Golestan, ta hanyar fitar da bayanai daban-daban, sun bayyana hakan. na fatawar Ayatullah Sayyid Ali Khamenei daidai da tunaninsa da aiki da shi, sun yi hakan ne wanda ke kawar da izinin fitina daga makiya[16].

Bayanin kula

Nassoshi

  • «یاسر الحبیب؛ آخوند لندن‌نشین/ دیروز در شبکه فدک، امروز در صوت العترة»‌، خبرگزاری تسنیم، تاریخ درج مطلب: ۲۳ د«استقبال جهان اسلام از استفتای جدید آیت‌الله خامنه‌ای»، روزنامه رسالت، ۱۱ مهر ۱۳۸۹ش.
  • «استقبال شیخ الازهر از فتوای رهبر انقلاب»، سایت خبرآنلاین، تاریخ درج مطلب: ۱۲ مهر ۱۳۸۹ش، تاریخ بازدید: ۱ بهمن ۱۳۹۹ش.
  • «الکویت: الغاء جنسیة رجل الدین الشیعی یاسر الحبیب»، بی‌بی‌سی عربی، تاریخ درج مطلب: ۲۹ شهریور ۱۳۸۹ش، تاریخ بازدید: ۲۵ دی ۱۳۹۹ش.
  • «تقدیر نماینده خاش از فتوای رهبری درباره حرمت نمادهای اهل سنت»، سایت خبرآنلاین، تاریخ درج مطلب: ۱۳ مهر ۱۳۸۹ش، تاریخ بازدید: ۱ بهمن ۱۳۹۹ش.
  • «حمایت از فتوای رهبری درباره حرام بودن توهین به اهل سنت در کنفرانس تقریب لندن»، خبرآنلاین، تاریخ درج مطلب: ۱۲ مهر ۱۳۸۹ش، تاریخ بازدید: ۴ بهمن ۱۳۹۹ش.
  • «روایت‌های جعلی شبکه‌های سلام، فدک و اهل‌بیت از شیعه»، مشرق نیوز، ۲۱ شهریور ۱۳۹۲ش، تاریخ بازدید: ۲۵ دی ۱۳۹۹ش.
  • «علمای اهل سنت استان گلستان: شیعه و سنی هر نوع توطئه دشمنان اسلام را خنثی می‌کنند مقام معظم رهبری منادی وحدت جهان اسلام است»، ایسنا، تاریخ درج مطلب: ۲۰ مهر ۱۳۸۹ش، تاریخ بازدید: ۱ بهمن ۱۳۹۹ش.
  • «فتوایی که فتنه تفرقه بین مسلمین را خنثی کرد»، خبرگزاری فارس، تاریخ درج مطلب: ۲۰ مهر ۱۳۸۹ش، تاریخ بازدید: ۲۴ دی ۱۳۹۹ش.
  • «گروه‌های مذهبی لبنان از فتوای مهم رهبر انقلاب حمایت کردند»، خبرگزاری مهر، تاریخ درج مطلب: ۱۰ مهر ۱۳۸۹ش، تاریخ بازدید: ۱ بهمن ۱۳۹۹ش.
  • «وحدت اسلامی در دیدگاه رهبر انقلاب و تاثیرات جهانی آن»، سایت مشرق، تاریخ درج مطلب: ۲۰ مرداد ۱۳۹۵ش، تاریخ بازدید: ۲ بهمن ۱۳۹۹ش.

ی ۱۳۹۲ش، تاریخ بازدید: ۱ بهمن ۱۳۹۹ش.