Dutsen Sina'i

Daga wikishia

Dutsen Sina'i (Larabci: طور سيناء) dutse ko jerin tsaunuka, wanda yake a kasar Masar, anbatonsa ya zo a cikin Alkur'ani da Attaura, kuma a can ne abubuwa daban-daban suka faru ga Annabi Musa (A.S), daga cikin abubuwan da suka faru akwai; Allah ya yi magana da shi kuma ya tafi zuwa ganawa da Ubangijinsa sau biyu, a karo na farko shi kadai, ya ɗauki kwanaki arba'in, kuma a karo na biyu ya tafi a cikin jama'a mutum saba'in daga mutanenshi (Bani Isra'ila) kuma a lokacin ne Allah ya karbi rayuwar Musa(A.S) ya faru.

An rawaito daga manzon Allah (S.A.W) cewa: dalilin tsarkin wannan dutsen shi ne wuri ne da Allah ya yi magana da Annabi Musa (A.S), kuma inda aka tsarkake ko girmama rayuka, inda aka zabi mala'iku, kuma anbatonsa ya zo a waƙa.

Wurin Da Wannan Dutsan Yake

Dutsen Sina'i yana kudu da hamadar Sina'i, a tsakanin jerin tsaunuka, a arewa maso gabashin Masar a kan iyakarta da Falasdinu, Jordan, da ƙasar Saudiyya.[1] An ce ƙila yana ƙasar Sham,[2] Wasu sun ce abin da ake kira Dutsen Sinai jerin tsaunuka ne, amma abin da ake kira ɗuri sinin wani yanki ne na yankin Sina'a.[3] Shi kuma Dairu Sanat katrin yana kusa da wannan dutsan.[4]

Ambatansa A Alƙur'ani Da Dalilin Da Yasa Ake Kiranshi Da Sunansa=

Alƙur'ani ya anbaci dutsan ɗuri Sina'a sau ɗaya, kuma alƙur'ani ya yi magana kan wata bishiya wadda take fitowa a kan shi wanda take fitar da mai,[5] kuma ya rantse da ɗuri sinin,[6] wanda wasu daga malaman tafsiri suka ce shi ne ɗuri sina'a,[7] kazalika wasu masu tafsiri suka ce ɗuri ɗin da aka ambata a wasu ayoyi[8] shi ne dai ɗuri sina'a.[9] Shaik Saduƙ ya naƙalto daga ɗan Abbas cewa kowanne dutse a samarshi akwai abin da zai amfanar na tsirrai da bishiyu to ana kiranshi ɗuri sina'a ko kuma ɗuri sinin,to sabo da haka ne ake kiran dutse da Annabi Musa (A.S) yake kai da ɗuri sina'a, sabo da a kanshi akwai bishiyar Zaitun.[10]

Tsarkin Wannan Dutsen

A cikin dutsen Sinai Allah ya yi magana da Annabinsa Musa (A.S), kuma a kan aya ta 12 a cikin Suratul Taha, ya umarce shi da ya tuɓe takalmansa, kuma ya shiryar da shi zuwa ga tsarkin wannan wuri da cewa: lallai .”[11][12] Kuma Allah ya yi rantsuwa da wannan mataki a cikin Suratul Tur.[13] An karbo daga Manzon Allah (S.A.W), game da kwazazzabo mai tsarki: Me ya sa aka ce da shi mai tsarki, sai ya ce: Saboda an tsarkake rayuka a cikinshi, kuma an zaɓi Mala'iku akanshi, kuma Allah ya yi magana da musa a kanshi.[14]

Abin da Ya Faru A Kan Ɗuri Sina

Dangane da abin da ya zo a cikin ayoyi da ruwayoyi, abubuwa sun faru a dutsen Sinai ga Musa (A.S), da Bani Isra'ila:

  • Annabi Musa (AS) ya tafi kasar Masar ya fara karbar wahayi:

lokacin da Musa ya cika alkawarinshi da Shu'aibu a Madyana, sai ya fita da matarshi, da ɗansa, da dukiyarsa, suka nufi Masar, bayan hanya ta bace masa.[15] kwatsam sai ya ga hango wuta ta bayyana a kan wani dutse, sai ya nufe ta,[16] to a lokacin ne annabtarshi ta fara, kuma aka yi mishi wahayi,[17] kuma wannan wurin shi ne wanda Kur'ani ya ambace shi da lafazin ɗuri a wasu lokuta,[18][19] kuma wasu masu tafsiri sun ce: ɗur shi ne dutsen Sinai, kuma ɗur wani kwari ne a kasanshi.[20]

Miƙatin Musa Na Kwanaki Arba'in

Bayan da Bani Isra'ila suka bar Masar, Musa ya hau wani dutse, ya zauna a kanshi na tsawon kwanaki arba'in, ya karbi allunan Attaura[21]wasu malaman tafsiri sun ce wannan dutsen shi ne ɗuri sina'a kuma hakan ya zo a Attaura.[22] Ku yi shiri da safe, ku hau Dutsen Sinai da safe, ku tsaya tare da ni a kan ƙololuwan dutsen.[23] Miƙatin Musa tare da mutum saba'in daga Bani Isra'ila, Musa ya tafi da mutane saba'in daga Bani Isra'ila, har da Yusha'u matsayin kalifan shi san da zai tafi zuwa ga Miƙatin Ubangijinshi, sai Allah Ya ɗaukaka dutse a saman su, sai suka mika wuya, kuma azabar Ubangiji ba ta sauka a kansu ba.[24] Ya zo a cikin ruwaya daga Imam Sadik (A.S), cewa wannan lamari ya faru ne a dutsen Sinai.[25]

Wafatin Musa

Bisa wasu ruwayuyi annabi Musa ya yi wafati a Ɗuri Sina.[26]

Bayanin kula

  1. Al-Mustafawi, al-Tahaqiq fi Kalamat al-Qur'an al-Karim, juzu'i na 5, shafi na 293.
  2. Ibn Manzoor, Lasan al-Arab, juzu'i na 4, shafi na 508.
  3. Al-Mustafawi, Al-TaHaqiq fi Kalmat al-Qur'an, juzu'i na 5, shafi na 293-295
  4. Majmu'atu muallifi, Mujaz Dayiratul Al-marif Islamiyya, juzu'i na 22, shafi na 969.
  5. Al-Mu’uminun: 20.
  6. Al-Tin: 2.
  7. Makarem Al-Shirazi, Al-Amsal, juzu'i na 20, shafi na 307.
  8. Al-Baqarah: 63 da 93; Nisa'i: 154; da Maryam: 52; Taha: 80;qasas: 29 da 46; Form: 1.
  9. Makarem Al-Shirazi, Al-Amsal, juzu'i na 1, shafi na 260; Vaj 17, shafi na 153; Al-Tayeb, Atayeb Bayan fi Tafsirin Qur'an, juzu'i na 12, shafi na 292.
  10. Al-Saduq, Ilal al-Shara’i’, juzu’i na 1, shafi na 68
  11. Taha: 12.
  12. Al-Qurashi, Kamus Kur’ani, juzu’i na 5, shafi na 256.
  13. Mataki: 1.
  14. Al-Saduq, Ilal al-Shara’i’, juzu’i na 1, shafi na 472.
  15. Makarem Al-Shirazi, Al-Amsal, juzu'i na 9, shafi na 532.
  16. Taha: 10 & 11.
  17. Taha: 12 da 13.
  18. Kasas: 29.
  19. Taha: 12.
  20. Moghniyya, al-Tafsir al-Kashif, juzu'i na 7, shafi na 509.
  21. Al-Araf: 145-142.
  22. Al-Ghazi, Bayan al-Ma'ani, juzu'i na 1, shafi na 416.
  23. الكتاب المقدس (العهد القديم)، سفر الخروج، الأصحاح 34، الآية: 2.الكتاب المقدس.
  24. Suratul Baqarah: 93.
  25. Al-Qami, Tafsirin Al-Qummi, juzu'i na 1, shafi na 246.
  26. Al-Bahrani, Al-Burhan fi Tafsir Qur'an, juzu'i na 4, shafi na 289.

Nassoshi

  • Al-Saduq, Muhammad, 'Illal al-Shar'i, Qom - Iran, mawallafi: Laburaren Al-Dawari, bugu na 1, 1385H.
  • "Al-Qur'ani Mai Girma".
  • Bible'.
  • Al Ghazi, Abdul Qadir, Bayan al-Ma'ani, Damascus - Syria, mawallafi: Al-Tarqi Press, bugun farko, 1382 AH.
  • Al-Bahrani, Hashim, Al-burhan fi Tafsiril Alqur'an', edita ta: The Mission Foundation, Qom - Iran, mawallafin: Mu'assasar Jakadanci, Sashen Nazarin Musulunci, bugu na farko, 1415 AH.
  • Al-Mustafawi, Hassan, Tahkik fi Kalemat Kur'an Al-karim Tehran - Iran, Mawallafi: Cibiyar Tarjama da Buga Al-Kitab, bugu na 1, 1402H.
  • Al-Qurashi, Ali Akbar, Kamus Kur'ani, Tehran - Iran, mawallafi: Dar Al-Kutub Al-Islamiyyah, bugu na 6, 1371H.
  • Al-Tayeb, Abdul Hussein, Atyab Al-Bayan fi Tafsir Al-Qur'an, Tehran - Iran, mawallafi: Islam Publications, bugu na biyu, 1378 AH.
  • Ibn Arabi, Muhammad bin Ali, ' Diwan Ibn Arabi (Mafi Girman Diwan), edited by: Ahmed Hassan Basaj, Beirut - Lebanon, publisher: Dar Al-Kutub Al-Ilmiyyah, D.T.
  • Ibn Manzur, Muhammad, Lisan al-Arab, editan: Ahmed Fares, Sahib al-Jawa'ib, Beirut, Lebanon, mawallafi: Dar al-Sadir, bugu na 3, 1414H.
  • Jam'i az nawisendigan, 'Mujaz dayiratil almarif islami, D.M., Mawallafi: Cibiyar Kirkirar Hankali ta Sharjah, bugun farko, 1418H/1998 miladiyya.
  • Makarem Al-Shirazi, Nasser, 'Al-Amsal fi tafsir' kitanillahi al-munazzal', Muhammad Ali Azarshab, Qum - Iran, mawallafin: Imam Ali bin Abi Talib Mazhabar Template:S.A.W, 1st shekara ta 1421 H.
  • Mughniyeh, Muhammad Jawad, Tafsir Alkashi Qom - Iran, Dar Al-Kitab Al-Islami, bugu na 1, 1424H.

Al-Qummi, Ali bin Ibrahim, Tafsir Al-Qumi, bugun: Tayyab Al-Jazairi, Qum - Iran, bugun Darul-Kitab, bugu na 3, 1404H.