Jump to content

Khula ɗiyar Manzur

Daga wikishia
Domin gujewa dimauta ku duba: Khaula

Khula ɗiyar Manzur bin Zabban Fazari,(Larabci:خولة بنت منظور بن زبّان الفزارية) Ta kasance daga cikin matan Imam Hassan Mujtaba (A.S) kuma mahaifiyar Hassan Musanna, Muhammad bin Ɗalha ta fara aura kafin Imam Hassan (A.S), an kashe wannan miji na ta a lokacin yaƙin Jamal, bayan shahadar mijinta ne Imam Hassan Mujtaba (A.S) ya aure ta[1] Mahaifiyar Khaula ita ce Malika ɗiyar Kharijatu Bin Sinan.[2] Rahoton ya ce, bayan kashe mijinta na farko Muhammad Bin Ɗalha, Abdullahi ɗan Zubair, mijin ƴar uwar Khola, ya yi wa Imam Hassan (A.S) baikon aurenta, a yayin da mahaifin Khula baya nan, sai Imam ya amince. An ce lokacin da mahaifinta ya ji labari, da farko ya ji fusata, amma daga ƙarshe ya yarda.[3] amma masanin tarihin nan Baƙir Sharif Ƙarashi (Rasuwa: 1433 h.) ya yi tardidi da shakku kan ingancin wannan magana, yana ganin wannan magana an yi ne domin ƙasƙantar da darajar Imam Hassan (A.S) tare da jingina masa wani abu, kuma ya kawo shaidun wajan ƙaryata wannan magana.[4] Wasu suna ganin Imam Ya saki Khula tun kafin shahadarsa.[5] Wasu kuma suna ganin ta yi aure da Abdullahi bin Zubair bayan shahadar Imam.[6]

Amma a cewar Baƙir Sharif Ƙarashi, Khula ta ci gaba da ksancewa matar Imam har zuwa ƙarshen rayuwarsa, kuma ba ta yi aure ba bayan shahadarsa.[7] A cikin littafin Al-Amali fil-Mushiklat al-Ƙur'aniyya wal-Hukmi wal-ahadisun Nabawiyya na Abdul-Rahman Bin Ƙasim (Rasuwa: 339 H.), an bayyana cewa Khula ta kasance cikin tsananin damuwa a lokacin shahadar Imam Hassan. har mahaifinta Manzur ya rubuta mata waƙoƙi don kwantar mata da hankali.

نبئت خولة امس قد جزعت
من ان تنوب نوائب الدهر
لاتجزعی یا خول و اصطبری
ان الکرام بنوا علی الصبر

Tarjama: Jiya na na samu labari cewa Khula tana kukan baƙin ciki sakamakon musibar zamani da ta same ta, Ya ke Khula! Kada ki yi baƙin ciki kuma ki yi haƙuri domin ma'abota daraja sun ginu kan haƙuri. e.[8]


Haka kuma Khula ta haifi ƴaƴa uku da Muhammad bin Ɗalha (mijinta na farko) , mai suna Ibrahim, da Dawud da Ummu ƙasim.[9]

Bayanin kula

  1. Abolfaraj Esfahani, Al-Aghani, 1415 Hijira, juzu'i na 12, shafi na 408.
  2. Balazri, Ansab al-Ashraf, 1397 AH, juz.3, shafi na 72.
  3. Balazri, Ansab al-Ashraf, 1397 AH, juz 3, shafi na 24-25.
  4. ƙureshi, Hayat al-Imam al-Hasan, Dar al-Balagha, juzu'i na 2, shafi na 457.
  5. Duba Abul Faraj Isfahani, Al-Aghani, 1415H, Mujalladi na 12, shafi na 409.
  6. Duba ƙurashi, Hayat al-Imam al-Hasan, Dar al-Balaghah, juzu'i na 2, shafi na 457.
  7. ƙureshi, Hayat al-Imam al-Hasan, Dar al-Balagha, juzu'i na 2, shafi na 457.
  8. Az-Zajjāj, Al-Amālī, shekara ta 1354 Hijira, shafi na 7.
  9. Abolfaraj Esfahani, Al-Aghani, 1415 Hijira, juzu'i na 12, shafi na 408.

Nassoshi

  • Abul Faraj Isfahani, Ali bin Hossein, Al-Aghani, Beirut, Dar Ahya Al-Trath Al-Arabi, 1415H/1994 Miladiyya.
  • Belazari, Ahmad bin Yahya, Ansab al-Ashraf (Juzu'i na 3), Bincike: Mohammad Baƙer Mahmoudi, Beirut, Dar al-Taraif na Jarida, 1977/1397.
  • ƙurashi, Baƙer Sharif, Hayat Imam al-Hasan bin Ali (a.s), nazari da nazari, Dar al-Balagha, Beta.
  • Zajj, Abdul Rahman bin ƙasim, al-Amali fi al-Mashkilat al-ƙur'an da al-Hukm da hadisin annabci, Sharhin: Ahmad bin Amin Shenƙiti, Egypt, al-Maktab al-Mahmoudi al-Tajjariyah, bugu na biyu, 1354 AH/1935 AD.