Jump to content

Daƙiƙa:Wasiƙar Imam Ali Zuwa Ga Ash'as Bin Ƙaisi

Daga wikishia
Wasiƙar Imam Ali Zuwa Ga Ash'as Bin Ƙaisi
Wasiƙar Imam Ali (A.S) Zuwa Ga Ash'as Bin Ƙaisi
Zamanin fitowaShekara ta 36H
Ta fito dagaImam Ali (A.S)
Wanda ake magana da shiAsh'as Bin Ƙaisi
YareLarabci
Maudu'iMai girma yana tunasar da shi mutuwar Usman da kuma karya mubaya’ar Ɗalha da Zubairu, sannan yana neman ya yi masa mubaya’a.
Ɗan aikeZiyad Bin Marhab Hamadani
Inganacin isnadiIngantacce
Madogaran Shi'aNahjul Balaga• Littafin Waƙ'atu Siffin
Madogaran AhluS-sunnaAl-Futuh
SiffofiNuni ne ga cewa muƙaman gwamnati a tsarin mulkin Musulunci amana ce daga Allah • Kare dukiyar baitulmalin Musulmi
Mai alaƙaWasiƙar Imam Ali Zuwa Ga Usman Bin HunaifWasiƙar Imam Ali Zuwa Ga Shuraih ƘaziWasiƙar Imam Ali Zuwa Ga Sahlu Bin Hunaif


Wasiƙar Imam Ali (A.S) zuwa ga Ash'as Bin Ƙaisi tana daga cikin wasiƙun Nahjul Balaga, inda Imam Ali (A.S), yayin tunasar da kisan Usman da kuma karya mubaya'ar Ɗalha da Zubairu, ya nemi Ash'as Bin Ƙaisi, wanda yake gwamnan Azarbaijan, ya yi masa mubaya'a.[1] A ƙarshen wasiƙar, Imam Ali (A.S) ya kuma yi wa Ash'as gargaɗi game da kare baitul-mali.[2] A cewar Ayatullahi Makarim Shirazi, mai sharhin Nahjul Balaga, babban abin da wasiƙar take jaddadawa shi ne cewa mukaman gwamnati a gwamnatin Musulunci amana ce daga Allah, kuma bai kamata a mayar da su wata hanya ta neman amfanin kai ko zaluntar jama'a ba.[3] Imam Ali (A.S) ya rubuta wannan wasiƙa a shekara ta 36H, bayan Yaƙin Jamal,[4] sannan ya aika da ita zuwa ga Ash'as ta hannun Ziyad Bin Marhab Hamdani.[5]

Masana tarihin sun rawaito wannan wasiƙa da ɗan bambancin lafazi. Ibn A'asam Kufi, marubucin tarihi (wanda da ya rasu bayan shekara ta 320H), ya kawo ta a cikin littafinsa Al-Futuh. Haka nan Nasru Bin Muzahim, wanda ya rayu a ƙarni na biyu bayan hijira, ya kawo wannan wasiƙa a cikin littafinsa Waƙ'atu Siffin, tare da ɗan bambancin rubutu.[6] Sayyid Radi kuwa, a cikin Nahjul Balaga, ya kawo ƙarshen wannan wasiƙa ne kawai.[7] Wannan wasiƙa ita ce wasiƙa ta biyar a Nahjul Balaga bisa gyaran Subhi Salih, da kuma bisa bugu na Faizul Islam, Ibn Maisam da sauran masu gyara.[8]

Ash'as Bin Ƙaisi Kindi (ya rasu a shekara ta 40H) yana daga cikin mutanen da suka halarci yaƙin da aka yi wajen buɗe Azarbaijan. A shekara ta 25H, Usman Bin Affan ya naɗa shi a matsayin gwamnan Azarbaijan.[9] A cewar wasu masana tarihi, da izinin Usman, Ash'as yana karɓar dirhami 1000 a shekara daga cikin harajin Azarbaijan domin kansa.[10] A farkon mulkin Imam Ali (A.S), bai cire Ash'as daga mukaminsa ba.[11]

Bisa wasu ruwayoyin tarihi, bayan Ash'as ya karanta wasiƙar Imam Ali (A.S) ga mutanensa, sai suka ƙarfafa shi ya yi mubaya'a ga Imam Ali (A.S). Amma ya ce yana tsoron cewa idan ya je wajen Ali (A.S), Imam zai karɓe masa dukiyoyin Azarbaijan, yayin da idan ya koma wajen Mu'awiya, ba zai karɓe masa komai ba.[12]

A cewar wannan ruwaya, bayan mutanensa sun zarge shi saboda wannan magana, Ash'as ya yi nadama.[13] Daga nan, kamar yadda masu binciken tarihi suka bayyana, Ash'as ya nufi Kufa, sai Imam Ali (A.S) ya karɓe dukiyar baitul-malin da take hannunsa, sannan ya cire shi daga mukaminsa.[14]

Rubutun Wasiƙa

Rubutu
Rubutu da Fassara
Fassara

أَمَّا بَعْدُ فَلَوْ لَا هَنَاتٌ كُنَّ فِيكَ كُنْتَ الْمُقَدَّمَ فِي هَذَا الْأَمْرِ قَبْلَ النَّاسِ وَ لَعَلَّ أَمْرَكَ يَحْمِلُ بَعْضُهُ بَعْضاً إِنِ اتَّقَيْتَ اللَّهَ ثُمَّ إِنَّهُ كَانَ مِنْ بَيْعَةِ النَّاسِ إِيَّايَ مَا قَدْ بَلَغَكَ

وَ كَانَ طَلْحَةُ وَ الزُّبَيْرُ مِمَّنْ بَايَعَانِي ثُمَّ نَقَضَا بَيْعَتِي عَلَى غَيْرِ حَدَثٍ وَ أَخْرَجَا أُمَّ الْمُؤْمِنِينَ وَ سَارَا إِلَى الْبَصْرَةِ فَسِرْتُ إِلَيْهِمَا فَالْتَقَيْنَا فَدَعَوْتُهُمْ إِلَى أَنْ يَرْجِعُوا فِيمَا خَرَجُوا مِنْهُ فَأَبَوْا فَأَبْلَغْتُ فِي الدُّعَاءِ وَ أَحْسَنْتُ فِي الْبَقِيَّةِ

وَ إِنَّ عَمَلَكَ لَيْسَ لَكَ بِطُعْمَةٍ وَ لَكِنَّهُ أَمَانَةٌ وَ فِي يَدَيْكَ‌ مَالٌ مِنْ مَالِ اللَّهِ وَ أَنْتَ مِنْ خُزَّانِ اللَّهِ عَلَيْهِ حَتَّى تُسَلِّمَهُ إِلَيَّ وَ لَعَلِّي أَلَّا أَكُونَ شَرَّ وُلَاتِكَ لَكَ إِنِ اسْتَقَمْتَ وَ لا قُوَّةَ إِلَّا بِاللَّهِ‌

أَمَّا بَعْدُ فَلَوْ لَا هَنَاتٌ كُنَّ فِيكَ كُنْتَ الْمُقَدَّمَ فِي هَذَا الْأَمْرِ قَبْلَ النَّاسِ وَ لَعَلَّ أَمْرَكَ يَحْمِلُ بَعْضُهُ بَعْضاً إِنِ اتَّقَيْتَ اللَّهَ ثُمَّ إِنَّهُ كَانَ مِنْ بَيْعَةِ النَّاسِ إِيَّايَ مَا قَدْ بَلَغَكَ
Amma bayan haka, da ba don wasu kura-kuran da suka faru daga gare ka ba, da ka riga sauran mutane ka zama jagora a wannan al'amari. Amma wataƙila za ka iya yin wani abu da zai gyara abin da ya faru daga gare ka, idan ka ji tsoron Allah. Abin da ya faru game da mubaya'ar mutane gare ni ya riga ya iso gare ka.
وَ كَانَ طَلْحَةُ وَ الزُّبَيْرُ مِمَّنْ بَايَعَانِي ثُمَّ نَقَضَا بَيْعَتِي عَلَى غَيْرِ حَدَثٍ وَ أَخْرَجَا أُمَّ الْمُؤْمِنِينَ وَ سَارَا إِلَى الْبَصْرَةِ فَسِرْتُ إِلَيْهِمَا فَالْتَقَيْنَا فَدَعَوْتُهُمْ إِلَى أَنْ يَرْجِعُوا فِيمَا خَرَجُوا مِنْهُ فَأَبَوْا فَأَبْلَغْتُ فِي الدُّعَاءِ وَ أَحْسَنْتُ فِي الْبَقِيَّةِ
Ɗalha da Zubairu ma suna daga cikin waɗanda suka yi mini mubaya'a, amma ba tare da wani abin da ya faru ba, suka karya mubaya'arsu. Sun tafi Basra tare da Uwar Muminai, sai na nufi wajensu. Na gamu da su, na kira su da su koma ga abin da suka bari, amma suka ƙi. Na yi iya ƙoƙarina wajen yi musu kira, kuma a sauran mu'amalar da muka yi, na kyautata musu.
وَ إِنَّ عَمَلَكَ لَيْسَ لَكَ بِطُعْمَةٍ وَ لَكِنَّهُ أَمَانَةٌ وَ فِي يَدَيْكَ‌ مَالٌ مِنْ مَالِ اللَّهِ وَ أَنْتَ مِنْ خُزَّانِ اللَّهِ عَلَيْهِ حَتَّى تُسَلِّمَهُ إِلَيَّ وَ لَعَلِّي أَلَّا أَكُونَ شَرَّ وُلَاتِكَ لَكَ إِنِ اسْتَقَمْتَ وَ لا قُوَّةَ إِلَّا بِاللَّهِ‌
Ka sani cewa aikin da aka ba ka amanar riƙe shi ba ganima ba ne a gare ka, a'a, amana ce. Kuma a hannunka akwai dukiya daga cikin dukiyar Allah, kuma kai ma'aji ne daga cikin ma'ajin Allah har sai ka miƙa ta gare ni. Kuma wataƙila ba zan zama mafi munin gwamnoninka ba, idan ka bi hanya madaidaiciya. Babu wani ƙarfi face daga Allah.

Amma bayan haka, da ba don wasu kura-kuran da suka faru daga gare ka ba, da ka riga sauran mutane ka zama jagora a wannan al'amari. Amma wataƙila za ka iya yin wani abu da zai gyara abin da ya faru daga gare ka, idan ka ji tsoron Allah. Abin da ya faru game da mubaya'ar mutane gare ni ya riga ya iso gare ka.

Ɗalha da Zubairu ma suna daga cikin waɗanda suka yi mini mubaya'a, amma ba tare da wani abin da ya faru ba, suka karya mubaya'arsu. Sun tafi Basra tare da Uwar Muminai, sai na nufi wajensu. Na gamu da su, na kira su da su koma ga abin da suka bari, amma suka ƙi. Na yi iya ƙoƙarina wajen yi musu kira, kuma a sauran mu'amalar da muka yi, na kyautata musu.

Ka sani cewa aikin da aka ba ka amanar riƙe shi ba ganima ba ne a gare ka, a'a, amana ce. Kuma a hannunka akwai dukiya daga cikin dukiyar Allah, kuma kai ma'aji ne daga cikin ma'ajin Allah har sai ka miƙa ta gare ni. Kuma wataƙila ba zan zama mafi munin gwamnoninka ba, idan ka bi hanya madaidaiciya. Babu wani ƙarfi face daga Allah..

🌞
🔄


Bayanin kula

  1. Ibn A'asam, Al-Futuh, juzu'i na 2, shafina 503.
  2. Ibn A'asam, Al-Futuh, juzu'i na 2, shafina 503; Ibn Muzahim, Waƙ'atu Siffin, shafina 20.
  3. Makarim Shirazi, Payam-e Imam Amirul-Mu'uminin, juzu'i na 9, shafina 67.
  4. Aghazade, Hukumat-e Ash'as Bin Ƙais Dar Azarbaijan, shafina 34.
  5. Ibn A'asam, Al-Futuh, juzu'i na 2, shafina 503.
  6. Ibn A'asam, Al-Futuh, juzu'i na 2, shafina 503; Ibn Muzahim al-Minƙari, Waƙ'atu Siffin, shafina 20.
  7. Nahjul Balaga, Tas'hihu Subhi Salih, wasiƙa ta 5, shafina 366.
  8. Nahjul Balaga, Tas'hihu Subhi Salih, wasiƙa ta 5, shafina 366; Nahjul Balaga, Tas'hihu wa Tarjame Faizu al-Islam, wasiƙa ta 5, juzu'i na 5, shafina 389; Ibn Abil Hadid, Sharhu Nahjul Balaga, juzu'i na 4, shafina 33; Ibn Maisam, Sharhu NahjulBalaga, juzu'i na 4, shafi' na 350; Abduhu, Sharhu Nahjul Balaga, Alkahira, juzu'i na 3, shafina 7; Mughniya, Fi Zilal Nahjul-Balaga, juzu'i na 3, shafina 388.
  9. Balazuri, Futuhul-Buldan, juzu'i na 2, shafina 420.
  10. Aghazade, Hukumat-e Ash'as Bin Ƙais Dar Azarbaijan, shafina 30.
  11. Yaƙubi, Tarikhul Yaƙubi, juzu'i na 2, shafina 200.
  12. Ibn A'asam, Al-Futuh, juzu'i na 2, shafina 503; Ibn Muzahim, Waƙ'atu Siffin, shafina 21.
  13. Ibn A'asam, Al-Futuh, juzu'i na 2, shafina 503; Ibn Muzahim, Waƙ'atu Siffin, shafina 21.
  14. Aghazade, Hukumat-e Ash'as Bin Ƙais Dar Azarbaijan, shafina 38.

Nassoshi

  • Abduhu, Muhammad, Sharhu Nahjul Balaga, Alkahira, Matba'atu al-Istiƙama. babu kwanan wata.
  • Aghazade, Jafar Hukumat-e Ash'as Bin Ƙais Dar Azarbaijan, Pajuhishnamaye Tarih-ha-ye Mahalli-ye Iran, mujalladi na 7, lamba na 1. 1397Sh.
  • Balazuri, Yahya, Futuhul-Buldan, Alkahira, Matba'atu Lajnatil-Bayan al-Arabi.1957M.
  • Faizu al-Islam al-Isfahani, Ali-Naƙi, Tarjame Wa Sharhu Nahjul Balaga, ba a ambaci wurin bugawa ba, ba a ambaci gidan bugu ba.
  • Ibn A'asam al-Kufi, Muhammad bn Ali, Al-Futuh, Beirut, Dar al-Adwa.1411H.
  • Ibn Abi al-Hadid, Abd al-Hamid, Sharhu Nahjul Balaga, Qum, Maktabatu Ayatullahi al-Uzma al-Mar'ashi al-Najafi. babu kwanan wata.
  • Ibn Maisam, Maisam Bin Ali, Sharhu Nahjul Balaga, Tehran, Daftaru Nashril-Kitab.1404H.
  • Ibn Muzahim al-Minƙari, Nasr, Waƙ'atu Siffin, Qum, Maktabatu Ayatullahi al-Mar'ashi al-Najafi.1404H.
  • Makarim Shirazi, Nasir, Payam-e Imam Amirul-Mu'uminin, Tehran, Darul-Kutub al-Islamiyya. 1386Sh.
  • Mughniya, Muhammad Jawad, Fi Zilal Nahjul Balaga, Beirut, Darul-Ilmi lil-Malayin.1979M.
  • Sayyid Radi, Muhammad Bin Husain, Nahjul Balaga, Tash'hihu Subhi Salih, Qum, Hijrat. 1414H.
  • Yaƙubi, Ahmad bn Abi Yaƙub, Tarikhul Yaƙubi, Beirut, Dar Sadir. babu kwanan wata.