Jump to content

Ƙissar Rahba

Daga wikishia

Ƙissar Rahba (Larabci: يوم الرحبة) ko Munashadar Rahba ƙissa ce da take ishara zuwa ga shaida da wasu adadin Sahabbai suka bayar kan cewa lallai sun ji hadisin Ghadir da kunnuwansu daga Manzon Allah (S.A.W), wannan lamari ya faru ne bayan da Imam Ali (A.S) ya buƙace su da bayar da shaida daga adadin Sahabbai da adadinsu ya kasance tsakanin Mutum 12 zuwa 30, an naƙalto wannan ƙissa cikin litattafan Shi'a da Ahlus-sunna.

Ƙissar Da Kuma Dalilin Sanya Suna

A cewar Allama Amini, a shekara ta 25 bayan hijira dangane da abin da aka naƙalto daga kasancewar Annabi (S.A.W) ya gabatar da Imam Ali (A.S) kan Sauran Sahabbai, an samu wasu mutane sun tuhume shi kan wannan Magana tare da yin jayayya da shi dangane da Halifancinsa, da wannan dalili ne Imam Ali (A.S) ya hallara a Filin Kufa domin kare haƙƙinsa da kuma yin martani da raddi kan waɗanda suke jayayya da shi cikin lamarin Halifancinsa, ya haɗa su da Allah kan su tuna da hadisin ghadir[1] da wannan dalili ne ake kiran ranar Rahba da sunan Munashadatu Rahba (rantsuwar Rahhba) saboda Hazrat Ali (A.S) a farkon fara maganarsa ya yi amfani da kalmar Anshidullaha (ina rantsuwa da Allah) ya nemi waɗanda suka hallara a wannan wuri su bada shaida da hadisin Ghadir,[2] [Tsokaci 1] Munashada tana nufin rantsuwa da Allah.[3]

Bayan ya gama Magana, sai wasu daga cikin Sahabbai suka miƙe tsaye suka bada Shaida da cewa eh lallai sun ji hadisin Ghadir daga bakin Annabi (S.A.W), na'am a wasu Masadir an naƙalto cewa wasu daga cikinsu misalin Zaidu Bin Arƙam ba su yarda sun bada shaida ba, sai Imam Ali ya la'ance su,[4] na'am Sayyid Muhsin Amin ya rubuta cewa riwayoyin da suke naƙalto cewa Zaidu ya noƙe bai bada shaida ba kuskure aka yi cikin naƙalinsu, Barra'u Bin Azib ne yaƙi bada shaida ba Zaidu Bn Arƙam ba, saboda shi Zaidu Bn Arƙam daga gare shi ne aka rawaito da yawan riwayoyin Ghadir, kuma ya kasance yana fifita Hazrat Ali (A.S) kan sauran Sahabbai haka ya kasance daga kebantattun Mataimakan Hazrat Ali (A.S).[5]

Waɗanda Suka Bada Shaida

an samu Mabambantan naƙali kan adadin Sahabban da suka bada shaida kan cewa lallai sun ji Hadisin Ghadir daga Annabi (S.A.W), mafi karancin adadinsu shi ne mutane goma sha biyu, mafi yawansu shi ne adadin mutane talatin, Allama Amini ya ambaci adadin waɗanda suka bada shidai da aka naƙalto su a cikin litattafan Ahlus-Sunna sun kasance mutane ashirin da huɗu,[6] an naƙalto daga Ahmad Bin Hanbal cewa adadin waɗanda suka bada shaida ya kai mutane talatin.[7]

Abu Amra Ansari, Abul Hasim Bin At-Tihan, Abu Ayyub Ansari, Khuzaimatu Bin Sabit Ansari (Zu Shahadataini), Sahal Bin Hanif, Abu Sa'id Khudri, Sahal Bin Sa'ad Ansari, Abdullahi Bin Sabit Ansari (Khadimul Rasul) Ubaidu Bin Azib Ansari, Addi Bn Hatim, Najiyatu Bn Amru Khuza'i, Nu'uman Bin Ijlan suna daga cikin mafi shaharar cikin waɗanda suka bada shaida.[8]

Wuri Da Lokaci

Abin da ake nufi da Rahba wani fili ne da yake tsakiyar Masallacin Kufa, wanda a galibin lokuta a wannan fili ne Imam Ali (A.S) yake zama ya yi Alƙalanci ko wa'azi,[9] kamar yanda aka bayyana a zamanin Zayad Bin Abihi sakamakon tsananin tsoro marawaitan Hadisi maimakon ambaton sunan Imam Ali (A.S) suna amfani da sunan (Sahibul Rahba), 10 duk da cewa Rahba zai iya kasancewa tana da wasu Misdaƙan daban.[10]

Ƙissar Rahba ta faru ne a shekara ta 35 bayan hijira,[11] a farkon Halifanci Imam Ali (A.S), a cikin riwayar da Ya'ala Bin Mu'alla ya naƙalto, ya zo cewa: Lokacin da Amirul Muminin (A.S) ya shiga Kufa, ya yi wannan munazarar.[12]

Marawaita

Allama Amini ya ambaci adadin maruwaitan Manasheda na Rahba – wadanda suka rawaito domin ɗabaƙoƙin da za su zo daga bayan – kamar 18, daga cikinsu huɗu Sahabbai ne, goma sha hudu kuma Taabi'in ne.[13]:

  • Sahabbai:
  1. Habba Bin Juwaini Urani
  2. Zaidu Bin Arƙam
  3. Amir bin Wasila
  4. Ya'ala Bin Murra Bin Wahab Saƙafi

Tabi'ai:

  1. Abu Sulaiman Mu'azzin
  2. Asbag Bin Nabata
  3. Zazan Abu Amru
  4. Zar Bin Habish
  5. Ziyad Bin Abi Ziyad
  6. Zaidu Bin Yasi'u Hamadani
  7. Sa'id Bin Abi Hadan
  8. Sa'id Bin Wahab Hamadani
  9. Abu Amara AbduliKhairi Bin Yazid Hamadani
  10. Abdur-Rahman Bin Abi Laila
  11. Amru Zi Marra
  12. Umaira Bin Sa'ad Hamadani
  13. Hani Bin Hani Hamadani
  14. Harisa Bin Nasri[14]

Bayanin kula

  1. Amini, Al-Ghadir, 1416 Hijira, Mujalladi na 1, shafi na 339.
  2. Ibn Abi Al-Hadid, Sharh Nahj Al-Balaghah, 1404 AH, juzu'i na 4, shafi na 74.
  3. Dehkhoda,Luggatname, zaili "Manashed"
  4. Halabi, Sireh Halabiyeh, 1353 Hijira, juzu'i na 3, shafi na 308.
  5. Al-Amin, Ayan al-Shia, juzu'i na 7, shafi na 88.
  6. Amini, Al-Ghadir, 1416 AH, Juzu'i na 1, shafi na 376-377.
  7. Amini, Al-Ghadir, 1416 Hijira, juzu'i na 1, shafi na 377.
  8. Amini, Al-Ghadir, 1416 AH, Juzu'i na 1, shafi na 376-377.
  9. Matrazi, Maghreb, juzu'i na 1, shafi na 324.
  10. Hosseini Tehrani, ImamShinasi, 1427 AH, juzu'i na 9, shafi na 41.
  11. Amini, Al-Ghadir, 1416 Hijira, juzu'i na 1, shafi na 377.
  12. Hosseini Tehrani, Imamshinasi, 1427 AH, juzu'i na 9, shafi na 41.
  13. Amini, Al-Ghadir, 1416 Hijira, Mujalladi na 1, shafi na 339.
  14. Amini, Al-Ghadir, 1416 AH, Juzu'i na 1, shafi na 339-376.

Tsokaci

  1. ina rokonku don Allah wane ne ya rage daga mutanen da suka hadu da Annabi (S.A.W) ya kuma ji bayanin da yayi a ranar ghadir khum game da ni, ya taimaka ya tashi tsaye, ya bada shaida kan abin da ya ji daga Annabi

Nassoshi

  • Abd al-Hamid bin Hebatullah, Sharh Nahj Al-Balaghah, ƙum, wanda maktabat Ayatullahi Uzma Al-Mar'ashi Al-Najafi ta buga, 1404H.
  • Amini, Abdul Hossein, Al-Ghadir, ƙum, Al-Ghadir center, 1416 AH.
  • Hosseini Tehrani, Seyed Mohammad Hossein, Imamshinasi, Mashhad, Allamah Tabatabai bugu, 1427H.
  • Halabi Shafi'i, Ali bin Burhan al-Din, Sire Halabiyyah, Masar, 1353H.
  • Madani, Ali Khan bin Ahmad, bugu na farko, Mashhad, Al-Al-Bait Lahia Al-Trath Foundation, 2004.
  • Mutarzi, Nasser bin Abd al-Said, Maghreb, Edited by Mahmoud Fakhouri da Abd al-Hamid Mukhtar, Aleppo, School of Osama bin Zayd, 1979.